< Farawa 11 >
1 To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
Forsothe the lond was of o langage, and of the same speche.
2 Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
And whanne thei yeden forth fro the eest, thei fonden a feeld in the lond of Sennaar, and dwelliden ther ynne.
3 Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
And oon seide to his neiybore, Come ye, and make we tiel stonys, and bake we tho with fier; and thei hadden tiel for stonus, and pitche for morter;
4 Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
and seiden, Come ye, and make we to vs a citee and tour, whos hiynesse stretche `til to heuene; and make we solempne oure name bifor that we be departid in to alle londis.
5 Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
Forsothe the Lord cam down to se the citee and tour, which the sones of Adam bildiden.
6 Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
And he seide, Lo! the puple is oon, and o langage is to alle, and thei han bigunne to make this, nethir thei schulen ceesse of her thouytis, til thei fillen tho in werk; therfor come ye, go we doun,
7 Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
and scheende we there the tunge of hem, that ech man here not the voys of his neiybore.
8 Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
And so the Lord departide hem fro that place in to alle londis; and thei cessiden to bielde a cytee.
9 Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
And therfor the name therof was clepid Babel, for the langage of al erthe was confoundide there; and fro thennus the Lord scaterede hem on the face of alle cuntrees.
10 Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
These ben the generaciouns of Sem. Sem was of an hundrid yeer whanne he gendride Arfaxath, twey yeer aftir the greet flood.
11 Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Sem lyuede aftir that he gendride Arfaxath fyue hundrid yeer, and gendride sones and douytris.
12 Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
Forsothe Arfaxath lyuede fyue and thretti yeer, and gendride Sale;
13 Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Arfaxath lyuede aftir that he gendride Sale thre hundride and thre yeer, and gendride sones and douytris.
14 Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
Also Sale lyuede thretti yeer, and gendride Heber;
15 Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Sale lyuede after that he gendride Heber foure hundrid and thre yeer, and gendride sones and douytris.
16 Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
Sotheli Heber lyuede foure and thretti yeer, and gendride Falech;
17 Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Heber lyuede aftir that he gendride Falech foure hundrid and thretti yeer, and gendride sones and douytris.
18 Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
Also Falech lyuede thretti yeer, and gendride Reu;
19 Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Falech lyuede aftir that he gendride Reu two hundrid and nyne yeer, and gendride sones and douytris.
20 Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
And Reu lyuede two and thretti yeer, and gendride Saruch;
21 Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Reu lyuede aftir that he gendride Saruch two hundrid and seuene yeer, and gendride sones and douytris.
22 Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
Sotheli Saruch lyuede thretti yeer, and gendride Nachor;
23 Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Saruch lyuede aftir that he gendride Nacor two hundrid yeer, and gendride sones and douytris.
24 Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
Forsothe Nachor lyuede nyne and twenti yeer, and gendride Thare;
25 Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and Nachor lyuede after that he gendride Thare an hundrid and nynetene yeer, and gendride sones and douytris.
26 Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
And Thare lyuede seuenti yeer, and gendride Abram, and Nachor, and Aran.
27 Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
Sotheli these ben the generaciouns of Thare. Thare gendride Abram, Nachor, and Aran. Forsothe Aran gendride Loth;
28 Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
and Aran diede bifore Thare, his fadir, in the lond of his natiuite, in Vr of Caldeis.
29 Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
Forsothe Abram and Nachor weddiden wyues; the name of the wijf of Abram was Saray, and the name of the wiif of Nachor was Melcha, the douyter of Aran, fadir of Melcha and fadir of Jescha.
30 Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
Sotheli Saray was bareyn, and hadde no children.
31 Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
And so Thare took Abram, his sone, and Loth, the sone of Aran his sone, and Saray, his douyter in lawe, the wijf of Abram, his sone, and ledde hem out of Vr of Caldeis, that thei schulen go in to the lond of Chanaan; and thei camen `til to Aran, and dwelliden there.
32 Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.
And the daies of Thare weren maad two hundrid yeer and fyue, and he was deed in Aran.