< Farawa 11 >

1 To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
And all the world was of one tonge and one language.
2 Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
And as they came from the east they founde a playne in the lande of Synear and there they dwelled.
3 Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
And they sayd one to a nother: come on let us make brycke ad burne it wyth fyre. So brycke was there stone and slyme was there morter
4 Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
And they sayd: Come on let vs buylde vs a cyte and a toure that the toppe may reach vnto heauen. And let vs make us a name for perauenture we shall be scatered abrode over all the erth.
5 Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
And the LORde came downe to see the cyte and the toure which the childern of Ada had buylded.
6 Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
And the LORde sayd: See the people is one and haue one tonge amonge them all. And thys haue they begon to do and wyll not leaue of from all that they haue purposed to do.
7 Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
Come on let vs descende and myngell theire tonge even there that one vnderstonde not what a nother sayeth.
8 Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
Thus ye LORde skatered them from thence vppon all the erth. And they left of to buylde the cyte.
9 Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
Wherfore the name of it is called Babell because that the LORDE there confounded the tonge of all the world. And because that the LORde from thence skatered them abrode vppon all the erth.
10 Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
These are the generations of Sem: Se was an hundred yere olde and begat Arcphachsad ij. yere after the floude.
11 Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Se lyved after he had begot Arphachsad. v. hundred yere an begat sonnes and doughters.
12 Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
And Arphacsad lyued. xxxv. yere and begat Sala
13 Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and lyved after he had begot Sala iiij. hudred yere and. iij and begat sonnes and doughters.
14 Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
And Sala was. xxx. yere old and begat Eber
15 Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
ad lyued after he had begot Eber. iiij. hudred and thre yere ad begat sonnes and doughters
16 Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
When Eber was. xxxiiij. yere olde he begat Peleg
17 Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and lyued after he had begot Peleg foure hundred and. xxx. yere and begat sonnes and doughters.
18 Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
And Peleg when he was. xxx. yere olde begat Regu
19 Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and lyued after he had begot Regu. ij. hundred and. ix. yere and begat sonnes and doughters.
20 Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
And Regu when he had lyued. xxxij. yere begat Serug
21 Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and lyued after he had begot Serug. ij. hundred and. vij. yere and begat sonnes and doughters.
22 Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
And when Serug was. xxx. yere olde he begat Nahor
23 Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and lyued after he had begot Nahor. ij. hundred yere and begat sonnes and doughters.
24 Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
And Nahor when he was. xxix. yere olde begat Terah
25 Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
and lyved after he had begot Terah an hundred and. xix. yere and begat sonnes and doughters.
26 Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
And when Terah was. lxx. yere olde he begat Abram Nahor and Haran.
27 Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
And these are the generations of Terah. Terah begat Abram Nahor and Haran. And Haran begat Lot.
28 Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
And Haran dyed before Terah his father in the londe where he was borne at Vr in Chaldea.
29 Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
And Abram and Nahor toke them wyves. Abras wyfe was called Sarai. And Nahors wyfe Mylca the doughter of Haran which was father of Milca ad of Iisca.
30 Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
But Sarai was baren and had no childe.
31 Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
Than toke Terah Abram his sonne and Lot his sonne Harans sonne and Sarai his doughter in lawe his sone Abrams wyfe. And they went wyth hym from Vr in Chaldea to go in to the lade of Chanaan. And they came to Haran and dwelled there.
32 Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.
And when Terah was ij. hundred yere old and. v. he dyed in Haran.

< Farawa 11 >