< Farawa 11 >

1 To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
At first, all the people in [MTY] the world spoke the same language [DOU].
2 Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
As people moved further east, they arrived at a plain in Babylonia region and began to live there.
3 Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
Then they said to each other, “(Hey/Come on), let’s form bricks and bake them to make them hard, for building!” So they used bricks instead of stones, and used tar instead of (mortar/a mixture of cement, sand and lime) to hold them together.
4 Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
They said, “Hey, let’s build a city for ourselves! We also ought to build a very high tower that reaches up to the sky! In that way we will become famous! If we do not do this, we will be scattered all over the earth!”
5 Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
So they began to build the city and the tower. Then Yahweh looked down and saw the city and the tower that those [puny] men were building.
6 Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
Yahweh said, “These people are one group that all speak the same language. If they have begun to do this now, then (there is nothing that they will decide to do that will be impossible for them/they will be able to do whatever they decide to do) [LIT]!
7 Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
So, okay/now, we will go down there and cause there to be many different languages, so that they will not be able to understand each other.”
8 Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
So Yahweh did that. As a result, the people stopped building the city, and Yahweh caused them to disperse all over the earth.
9 Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
The city was called Babel which means ‘confusion’, because there Yahweh caused the people to become confused because the people [MTY] spoke [different languages that the others could not understand], not just one language. From there Yahweh caused them to disperse all over the earth.
10 Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
(This is a bigger list/I will now tell you more) of the descendants of Shem: Two years after the flood, when Shem was 100 years old, he became the father of Arpachshad.
11 Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
After Arpachshad was born, Shem lived 500 more years and had more sons and daughters.
12 Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
When Arphachshad was 35 years old, he became the father of Shelah.
13 Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
After Shelah was born, Arpachshad lived 403 more years and became the father of more sons and daughters.
14 Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
When Shelah was 30 years old, he became the father of Eber.
15 Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
After Eber was born, Shelah lived 403 more years and became the father of other sons and daughters.
16 Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
When Eber was 34 years old, he became the father of Peleg.
17 Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
After Peleg was born, Eber lived 430 more years and became the father of other sons and daughters.
18 Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
When Peleg was 30 years old, he became the father of Reu.
19 Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
After Reu was born, Peleg lived 209 more years and became the father of other sons and daughters.
20 Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
When Reu was 32 years old, he became the father of Serug.
21 Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
After Serug was born, Reu lived 207 more years and became the father of other sons and daughters.
22 Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
When Serug was 30 years old, he became the father of Nahor.
23 Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
After Nahor was born, Serug lived 200 more years and became the father of other sons and daughters.
24 Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
When Nahor was 29 years old, he became the father of Terah.
25 Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
After Terah was born, Nahor lived 119 more years and became the father of other sons and daughters.
26 Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
When Terah was 70 years old, his son Abram was born. Later, two other sons, Nahor and Haran were born.
27 Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
(This is/I will now give) a list of the descendants of Terah: Terah’s sons were Abram, Nahor, and Haran. Haran’s son was named Lot.
28 Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
Haran died before his father died. He died in Ur [city] in Chaldea land, where he was born.
29 Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
Abram and Nahor both married. Abram’s wife was named Sarai, and Nahor’s wife was named Milcah. Milcah and her younger sister Iscah were the daughters of Haran.
30 Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
Sarai was unable to bear any children.
31 Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
Terah decided to leave Ur and go to live in Canaan land. So he took his son Abram and his grandson Lot, the son of Haran, and Abram’s wife Sarai with him. But instead of going to Canaan, they stopped at Haran [town] and lived there.
32 Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.
When Terah was 205 years old, he died there in Haran.

< Farawa 11 >