< Farawa 11 >

1 To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
And the whole earth was of one language, and of one kind of words.
2 Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
And it came to pass, as they journeyed toward the east, that they found a plain in the land of Shinar, and they dwelt there.
3 Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
And they said to one another, Go to, let us make bricks, and burn them thoroughly. And thus the brick served them for stone, and slime served them for mortar.
4 Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
And they said, Go to, let us build ourselves a city, and a tower, the top of which may reach unto heaven; and let us make ourselves a name, lest we be scattered abroad upon the face of the whole earth.
5 Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
And the Lord came down to see the city and the tower, which the children of man were building.
6 Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
And the Lord said, Behold, it is one people, and they have all one language, and this is the first thing they undertake to do; and now shall they not be restrained in all which they have imagined to do?
7 Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
Go to, let us go down, and confound there their language, that they may not understand one another's speech.
8 Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
So the Lord scattered them abroad from there over the face of all the earth; and they left off to build the city.
9 Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
Therefore is the name of it called Babel, because the Lord did there confound the language of all the earth; and from there did the Lord scatter them abroad over the face of all the earth.
10 Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
These are the generations of Shem: Shem, when a hundred years old, begat Arpachshad, two years after the flood.
11 Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Shem lived after he had begotten Arpachshad five hundred years; and begat sons and daughters.
12 Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
And Arpachshad lived five and thirty years, and begat Shelach.
13 Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Arpachshad lived after he had begotten Shelach four hundred and three years; and begat sons and daughters.
14 Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
And Shelach lived thirty years, and begat Eber.
15 Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Shelach lived after he had begotten Eber four hundred and three years; and begat sons and daughters.
16 Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
And Eber lived four and thirty years, and begat Peleg.
17 Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Eber lived after he had begotten Peleg four hundred and thirty years; and begat sons and daughters.
18 Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
And Peleg lived thirty years, and begat Reu.
19 Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Peleg lived after he had begotten Reu two hundred and nine years; and begat sons and daughters.
20 Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
And Reu lived two and thirty years, and begat Serug.
21 Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Reu lived after he had begotten Serug two hundred and seven years; and begat sons and daughters.
22 Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
And Serug lived thirty years, and begat Nachor.
23 Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Serug lived after he had begotten Nachor two hundred years; and begat sons and daughters.
24 Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
And Nachor lived nine and twenty years, and begat Terach.
25 Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Nachor lived after he had begotten Terach a hundred and nineteen years; and begat sons and daughters.
26 Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
And Terach lived seventy years, and begat Abram, Nachor, and Haran.
27 Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
Now these are the generations of Terach: Terach begat Abram, Nachor, and Haran; and Haran begat Lot.
28 Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
And Haran died before his father Terach in the land of his nativity, in Ur of the Chaldees.
29 Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
And Abram and Nachor took themselves wives; the name of Abram's wife was Sarai; and the name of Nachor's wife was Milcah, the daughter of Haran, the father of Milcah, and the father of Yiscah.
30 Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
But Sarai was barren; she had no child.
31 Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
And Terach took Abram his son, and Lot, the son of Haran, his son's son, and Sarai his daughter-in-law, the wife of his son Abram; and they went forth with them from Ur of the Chaldees, to go into the land of Canaan; and they came unto Charan, and dwelt there.
32 Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.
And the days of Terach were two hundred and five years; and Terach died in Charan.

< Farawa 11 >