< Farawa 11 >
1 To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
And the earth was of one tongue, and of the same speech.
2 Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
And when they removed from the east, they found a plain in the land of Sennaar, and dwelt in it.
3 Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
And each one said to his neighbour: Come, let us make brick, and bake them with fire. And they had brick instead of stones, and slime instead of mortar.
4 Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
And they said: Come, let us make a city and a tower, the top whereof may reach to heaven: and let us make our name famous before we be scattered abroad into all lands.
5 Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
And the Lord came down to see the city and the tower, which the children of Adam were building.
6 Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
And he said: Behold, it is one people, and all have one tongue: and they have begun to do this, neither will they leave off from their designs, till they accomplish them in deed.
7 Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
Come ye, therefore, let us go down, and there confound their tongue, that they may not understand one another’s speech.
8 Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
And so the Lord scattered them from that place into all lands, and they ceased to build the city.
9 Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
And therefore the name thereof was called Babel, because there the language of the whole earth was confounded: and from thence the Lord scattered them abroad upon the face of all countries.
10 Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
These are the generations of Sem: Sem was a hundred years old when he begot Arphaxad, two years after the flood.
11 Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Sem lived after he begot Arphaxad, five hundred years, and begot sons and daughters.
12 Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
And Arphaxad lived thirty-five years, and begot Sale.
13 Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Arphaxad lived after he begot Sale, three hundred and three years; and begot sons and daughters.
14 Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
Sale also lived thirty years, and begot Heber.
15 Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Sale lived after he begot Heber, four hundred and three years; and begot sons and daughters.
16 Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
And Heber lived thirty-four years, and begot Phaleg.
17 Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Heber lived after he begot Phaleg, four hundred and thirty years: and begot sons and daughters.
18 Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
Phaleg also lived thirty years, and begot Reu.
19 Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Phaleg lived after he begot Reu, two hundred and nine years, and begot sons and daughters.
20 Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
And Reu lived thirty-two years, and begot Sarug.
21 Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Reu lived after he begot Sarug, two hundred and seven years, and begot sons and daughters.
22 Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
And Sarug lived thirty years, and begot Nachor.
23 Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Sarug lived after he begot Nachor, two hundred years: and begot sons and daughters.
24 Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
And Nachor lived nine and twenty years, and begot Thare.
25 Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
And Nachor lived after he begot Thare, a hundred and nineteen years: and begot sons and daughters.
26 Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
And Thare lived seventy years, and begot Abram, and Nachor, and Aran.
27 Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
And these are the generations of Thare: Thare begot Abram, Nachor, and Aran. And Aran begot Lot.
28 Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
And Aran died before Thare his father, in the land of his nativity in Ur of the Chaldees.
29 Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
And Abram and Nachor married wives: the name of Abram’s wife was Sarai: and the name of Nachor’s wife, Melcha, the daughter of Aran, father of Melcha, and father of Jescha.
30 Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
And Sarai was barren, and had no children.
31 Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
And Thare took Abram, his son, and Lot the son of Aran, his son’s son, and Sarai his daughter in law, the wife of Abram his son, and brought them out of Ur of the Chaldees, to go into the land of Chanaan: and they came as far as Haran, and dwelt there.
32 Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.
And the days of Thare were two hundred and five years, and he died in Haran.