< Galatiyawa 1 >

1 Bulus manzo, aikakke ba daga wurin mutum ba, ba kuma ta wurin mutane ba, amma ta wurin Yesu Kiristi da kuma Allah Uba, wanda ya tā da Yesu daga matattu.
Paul, apôtre, non de la part des hommes, ni par un homme, mais par Jésus-Christ, et Dieu le Père, qui l'a ressuscité des morts;
2 Dukan’yan’uwan kuma da suke tare da ni a nan, Suna gai da ikkilisiyoyi a Galatiya.
Et tous les frères qui sont avec moi, aux Églises de Galatie.
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
La grâce et la paix vous soient données de la part de Dieu le Père, et de notre Seigneur Jésus-Christ,
4 Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, (aiōn g165)
Qui s'est donné lui-même pour nos péchés, afin de nous retirer de ce siècle corrompu, selon la volonté de Dieu notre Père, (aiōn g165)
5 a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
Auquel soit gloire aux siècles des siècles! Amen. (aiōn g165)
6 Ina mamaki yadda kuka yi saurin yashe wanda ya kira ku ta wurin alherin Kiristi, kuna juyewa ga wata bishara dabam
Je m'étonne que vous abandonniez si promptement celui qui vous avait appelés à la grâce de Christ, pour passer à un autre évangile;
7 wadda a gaskiya ba bishara ba ce ko kaɗan. Tabbatacce waɗansu mutane suna birkitar da ku, suna kuma ƙoƙari su karkatar da bisharar Kiristi.
Non qu'il y en ait un autre, mais il y a des gens qui vous troublent, et qui veulent pervertir l'Évangile de Christ.
8 Amma ko mu, ko mala’ika daga sama ya yi wa’azin wata bishara dabam da wadda muka yi muku, bari yă zama la’ananne har abada!
Mais quand nous-mêmes, ou un ange du ciel vous annoncerait un évangile différent de celui que nous vous avons annoncé, qu'il soit anathème!
9 Kamar yadda muka riga muka faɗa, haka yanzu ma ina ƙara cewa in wani yana muku wa’azin wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, bari yă zama la’ananne har abada!
Comme nous l'avons déjà dit, je le dis encore maintenant: Si quelqu'un vous annonce un évangile différent de celui que vous avez reçu, qu'il soit anathème!
10 Za a ce, ina ƙoƙarin neman amincewar mutane ne, ko amincewa ta Allah? Ko kuwa ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne? Da a ce har yanzu ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne, ai, da ban zama bawan Kiristi ba.
Car, est-ce les hommes que je prêche, ou Dieu? ou est-ce que je cherche à plaire aux hommes? Si je plaisais aux hommes, je ne serais pas un serviteur de Christ.
11 Ina so ku sani’yan’uwa, cewa bisharar da nake wa’azi, ba mutum ne ya ƙago ta ba.
Je vous le déclare donc, frères: l'Évangile que j'ai annoncé n'est pas de l'homme;
12 Ban karɓe ta daga wurin wani mutum ba, ba a kuma koya mini ita ba, a maimako, na karɓe ta, ta wurin wahayi daga Yesu Kiristi ne.
Car je ne l'ai ni reçu ni appris d'un homme, mais par une révélation de Jésus-Christ.
13 Kun dai ji labarin rayuwata ta dā a cikin Yahudanci, yadda na tsananta wa ikkilisiyar Allah ƙwarai, na kuma yi ƙoƙarin hallaka ta.
Vous avez, en effet, entendu dire quelle était autrefois ma conduite dans le judaïsme; comment je persécutais à outrance l'Église de Dieu, et la ravageais;
14 Na ci gaba a cikin Yahudanci fiye da yawancin Yahudawan da suke tsarana, na kuma yi ƙwazo ƙwarai ga bin al’adun kakannina.
Et comment j'étais plus avancé dans le judaïsme que beaucoup de ceux de mon âge dans ma nation, étant le plus ardent zélateur des traditions de mes pères.
15 Amma sa’ad da Allah, wanda ya keɓe ni daga mahaifa ya kira ni ta wurin alherinsa, ya kuma gamshe shi
Mais quand il plut à Dieu, qui m'avait choisi dès le sein de ma mère, et qui m'a appelé par sa grâce,
16 yă bayyana Ɗansa a cikina, domin in yi wa’azinsa cikin Al’ummai. Ban nemi shawarar wani mutum ba.
De me révéler intérieurement son Fils, afin que je l'annonçasse parmi les Gentils; aussitôt, je ne consultai ni la chair ni le sang,
17 Ban kuma tafi Urushalima domin in ga waɗanda suka riga ni zaman manzanni ba, sai dai na hanzarta na tafi ƙasar Arabiya, daga baya sai na koma Damaskus.
Et je ne montai point à Jérusalem vers ceux qui étaient apôtres avant moi; mais je m'en allai en Arabie, et je revins encore à Damas.
18 Bayan shekara uku, sai na haura zuwa Urushalima domin in sadu da Bitrus, na kuwa zauna tare da shi kwana goma sha biyar.
Ensuite, trois ans après, je montai à Jérusalem, pour y visiter Pierre; et je demeurai chez lui quinze jours;
19 Ban ga wani a ciki sauran manzanni ba, sai dai Yaƙub ɗan’uwan Ubangiji.
Mais je ne vis aucun des autres apôtres, sinon Jacques, le frère du Seigneur.
20 Ina tabbatar muku a gaban Allah cewa abin da nake rubuta muku ba ƙarya ba ne.
Or, dans les choses que je vous écris, voici, devant Dieu, je ne mens point.
21 Daga baya sai na tafi Suriya da Silisiya.
J'allai ensuite dans les pays de Syrie et de Cilicie;
22 Ikkilisiyoyin da suke cikin Kiristi da suke a Yahudiya ba su san ni ba tukuna.
Mais j'étais inconnu de visage aux Églises de Judée qui sont en Christ.
23 Sun dai sami labari ne kawai cewa, “Mutumin da dā yake tsananta mana yanzu yana wa’azin bangaskiyar da dā ya yi ƙoƙari yă hallaka.”
Elles avaient seulement entendu dire: Celui qui autrefois nous persécutait, annonce maintenant la foi, que jadis il ravageait.
24 Sai suka yabi Allah saboda ni.
Et elles glorifiaient Dieu à cause de moi.

< Galatiyawa 1 >