< Galatiyawa 5 >
1 Saboda’yanci ne Kiristi ya’yantar da mu. Sai ku tsaya daram, kada ku yarda ku sāke komawa ƙarƙashin nauyin bauta.
Til Friheden har Kristus frigjort os. Saa staar nu fast, og lader eder ikke atter holde under Trældoms Aag!
2 Ku lura da kalmomina! Ni Bulus ina gaya muku cewa in kuka yarda aka yi muku kaciya, wannan ya nuna Kiristi ba shi da amfani a gare ku ba ko kaɗan.
Se, jeg, Paulus, siger eder, at dersom I lade eder omskære, vil Kristus intet gavne eder.
3 Haka kuma ina ƙara sanar wa kowane mutumin da ya yarda aka yi masa kaciya cewa dole yă kiyaye dukan Doka.
Men jeg vidner atter for hvert Menneske, som lader sig omskære, at han er skyldig at opfylde hele Loven.
4 Ku da kuke ƙoƙarin kuɓuta ta wurin Doka an raba ku da Kiristi ke nan; kuka kuma fāɗi daga alheri.
I ere tabte for Kristus, I, som retfærdiggøres ved Loven; I ere faldne ud af Naaden.
5 Amma ta wurin bangaskiya muna marmarin jira adalcin da muke bege ta wurin Ruhu.
Vi vente jo ved Aanden af Tro Retfærdigheds Haab.
6 Gama a cikin Kiristi Yesu, kaciya ko rashin kaciya ba su da wani amfani. Abin da kawai yake da amfani shi ne, bangaskiyar da take bayyana kanta ta wurin ƙauna.
Thi i Kristus Jesus gælder hverken Omskærelse eller Forhud noget, men Tro, som er virksom ved Kærlighed.
7 Kun yi tsere mai kyau a dā. Wa ya shige gabanku ya hana ku bin gaskiya?
I vare godt paa Vej; hvem har hindret eder i at adlyde Sandhed?
8 Wannan rarrashin da ake muku ba daga wanda ya kira ku ba ne.
Den Overtalelse kom ikke fra ham, som kaldte eder.
9 “Ɗan yisti kaɗan ne yake gama dukan curin burodi.”
En liden Surdej g syrer hele Dejgen.
10 Ina da tabbaci cikin Ubangiji cewa ba za ku bi wani ra’ayi dabam ba. Wannan da yake rikita ku za a hukunta shi, ko shi wane ne.
Jeg har den Tillid til eder i Herren, at I ikke ville mene noget andet; men den, som forvirrer eder, skal bære sin Dom, hvem han end er.
11 ’Yan’uwa, da a ce har yanzu ina wa’azin kaciya ne, to, me ya sa ake tsananta mini har yanzu? In haka ne, ashe, an kawar da abin da yake sa tuntuɓe game da gicciye ke nan.
Men jeg, Brødre! dersom jeg endnu prædiker Omskærelse, hvorfor forfølges jeg da endnu? Saa er jo Korsets Forargelse gjort til intet.
12 Da ma a ce masu tā da hankalinku ɗin nan su yanke gabansu gaba ɗaya mana!
Gid de endog maatte lemlæste sig selv, de, som forstyrre eder!
13 Ku’yan’uwana, an kira ku ga zama’yantattu. Amma kada ku yi amfani da’yancinku don aikata ayyukan mutuntaka a maimakon haka, ku yi hidimar juna da ƙauna.
I bleve jo kaldede til Frihed, Brødre! kun at I ikke bruge Friheden til en Anledning for Kødet, men værer ved Kærligheden hverandres Tjenere!
14 Dukan doka an taƙaita a cikin umarni ɗaya ne cewa, “Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.”
Thi hele Loven er opfyldt i eet Ord, i det: „Du skal elske din Næste som dig selv.”
15 In kun ci gaba da cizo, kuna kuma cin naman juna, ku yi hankali in ba haka ba za ku hallaka juna.
Men naar I bide og æde hverandre, da ser til, at I ikke fortæres af hverandre!
16 Saboda haka ina ce muku, ku yi rayuwa ta wurin Ruhu, ba za ku kuwa gamsar da sha’awace-sha’awacen mutuntaka ba.
Men jeg siger: Vandrer efter Aanden, saa fuldbyrde I ingenlunde Kødets Begæring.
17 Gama mutuntaka yana son abin da Ruhu yake ƙi, Ruhu kuma yana son abin da mutuntaka yake ƙi. Waɗannan biyu kuwa gāba suke da juna, har ku kāsa yin abin da kuke so.
Thi Kødet begærer imod Aanden, og Aanden imod Kødet; disse staa nemlig hinanden imod, for at I ikke skulle gøre, hvad I have Lyst til.
18 Amma in Ruhu ne yake bishe ku, ba ku a ƙarƙashin Doka ke nan.
Men naar I drives af Aanden, ere I ikke under Loven.
19 Ayyukan mutuntaka kuwa a fili suke. Wato, fasikanci, ƙazanta da kuma lalata;
Men Kødets Gerninger ere aabenbare, saasom: Utugt, Urenhed, Uterlighed,
20 bautar gumaka da sihiri; ƙiyayya, faɗa, kishi, fushi mai zafi, sonkai, tsattsaguwa, hamayya,
Afgudsdyrkelse, Trolddom, Fjendskaber, Kiv, Nid, Hidsighed, Rænker, Tvedragt, Partier,
21 da ƙyashi; buguwa, shashanci, da ire-irensu. Na gargaɗe ku, yadda na yi a dā, cewa masu irin wannan rayuwa ba za su gāji mulkin Allah ba.
Avind, Drukkenskab, Svir og deslige; hvorom jeg forud siger eder, ligesom jeg ogsaa før har sagt, at de, som øve saadanne Ting, skulle ikke arve Guds Rige.
22 Amma amfanin da Ruhu yake bayar shi ne ƙauna, farin ciki, salama, haƙuri, kirki, nagarta, aminci,
Men Aandens Frugt er Kærlighed, Glæde, Fred, Langmodighed, Mildhed, Godhed, Trofasthed,
23 sauƙinkai, da kuma kamunkai. Ai, ba ruwan Doka da waɗannan abubuwa.
Sagtmodighed, Afholdenhed. Imod saadanne er Loven ikke,
24 Waɗanda suke na Kiristi Yesu, sun gicciye mutuntaka tare da abubuwan da mutum yake marmari da kuma sha’awace-sha’awacensa.
men de, som høre Kristus Jesus til, have korsfæstet Kødet med dets Lidenskaber og Begæringer.
25 Da yake muna rayuwa ta Ruhu ne, bari mu ci gaba da al’amuranmu ta wurin Ruhu.
Naar vi leve ved Aanden, da lader os ogsaa vandre efter Aanden!
26 Kada mu zama masu girman kai, muna tsokana muna kuma jin kishin juna.
Lader os ikke have Lyst til tom Ære, saa at vi udæske hverandre og bære Avind imod hverandre.