< Galatiyawa 4 >

1 Abin da nake nufi shi ne, muddin magāji yana ɗan yaro ne tukuna, babu bambanci tsakaninsa da bawa, ko da yake shi ne da mallakar kome.
Digo, porém, que, enquanto o herdeiro é criança, em nada é diferente do servo, ainda que seja senhor de tudo.
2 Yana ƙarƙashin iyayen goyonsa da masu riƙon amana har yă zuwa cikar lokacin da mahaifinsa ya sa.
Mas está sob tutores e administradores, até o tempo determinado pelo pai.
3 Haka yake, sa’ad da muke’yan yara, mun kasance cikin bauta a ƙarƙashin ƙa’idodin duniya.
Assim também nós, quando éramos crianças, estávamos escravizados debaixo dos princípios elementares do mundo.
4 Amma da lokacin da aka tsara ya yi sosai, sai Allah ya aiki Ɗansa, haifaffe daga mace, haifaffe a ƙarƙashin Doka,
Mas quando o tempo se completou, Deus enviou o seu Filho, nascido de mulher, nascido sob a Lei,
5 domin yă fanshi waɗanda suke a ƙarƙashin doka, saboda mu sami cikakken matsayin zaman’ya’ya.
para redimir os que estavam sob a Lei, a fim de que nós recebêssemos a adoção como filhos.
6 Da yake ku’ya’ya ne, sai Allah ya aiko da Ruhun Ɗansa a cikin zukatanmu, Ruhun da yake kira, “Abba, Uba.”
E, como sois filhos, Deus enviou aos nossos corações o Espírito do seu Filho, que clama: “Aba, Pai!”
7 Saboda haka kai ba bawa ba ne kuma, kai ɗa ne; da yake kuwa kai ɗa ne, Allah ya mai da kai magāji.
Portanto, tu já não és mais servo, mas sim filho; e se és filho, também és herdeiro por meio de Deus.
8 Dā da ba ku san Allah ba, ku bayi ne ga waɗanda a ainihi ba alloli ba ne.
Quando, porém, não conhecíeis a Deus, vós servíeis aos que por natureza não são deuses.
9 Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma a ce Allah ya san ku, yaya kuke sāke komawa ga ƙa’idodin duniya marasa ƙarfi, abin tausayi kuma? Kuna so ku sāke komawa ga bautarsu ne?
Mas agora, que conheceis Deus, mais que isso, por Deus sois conhecidos, por que voltais outra vez aos fracos e miseráveis princípios elementares, aos quais quereis servir de novo?
10 Kuna kiyaye ranaku da watanni da lokuta da shekaru na musamman!
Vós guardais dias, meses, tempos, e anos.
11 Kai, kun ba ni tsoro, don ya zama kamar duk wahalar da na yi a kanku banza ne!
Temo a vosso respeito de que talvez eu tenha trabalhado para convosco em vão.
12 Ina roƙonku’yan’uwa, ku zama kamar ni, gama na zama kamar ku. Ba ku yi mini wani laifi ba.
Rogo-vos, irmãos, que sejais como eu, pois também eu sou como vós. Nenhum mal me fizestes.
13 Kun san rashin lafiyar da na yi, shi ne ya yi mini hanyar da na kawo muku bishara da farko.
E vós sabeis que foi com uma enfermidade da carne que vos anunciei o Evangelho pela primeira vez;
14 Ko da yake ciwona gwaji ne gare ku, ba ku yi mini reni ko ƙyama ba. A maimakon haka, kuka karɓe ni sai ka ce mala’ikan Allah, kuma sai ka ce Kiristi Yesu kansa.
E não cedestes à tentação de ter desprezo ou repugnância por meu aspecto físico; ao contrário, vós me recebestes como a um mensageiro de Deus, como ao [próprio] Cristo Jesus.
15 Me ya faru da dukan farin cikinku? Na tabbata, a lokacin, da mai yiwuwa ne da kun ciccire idanunku kun ba ni.
Onde está, pois, a vossa alegria? Pois eu vos dou testemunho de que, se fosse possível, teríeis arrancado os vossos próprios olhos para dá-los a mim.
16 Yanzu na zama abokin gābanku don na faɗa muku gaskiya ke nan?
Tornei-me, por acaso, vosso inimigo por ter vos dito a verdade?
17 Waɗancan mutane suna neman su rinjaye ku da ƙwazo, amma ba da kyakkyawar aniya ba. Abin da suke so shi ne su raba ku da mu, saboda ƙwazonku yă koma gare su.
Eles têm interesse por vós, mas não com boa intenção; mas querem vos isolar [de mim], para que vós mostreis interesse por eles.
18 Yana da kyau ku kasance da irin wannan niyya idan da nufi mai kyau ne, ku kuma kasance a haka koyaushe ba sai ina tare da ku ba.
É bom, porém, mostrar interesse para o bem sempre, e não somente quando estou presente convosco.
19 Ya ku’ya’yana ƙaunatattu, ina sāke shan wahalar naƙudarku, har sai Kiristi ya kahu a cikinku.
Meus filhinhos, por quem volto a sofrer dores de parto, até que Cristo seja formado em vós:
20 Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canja muryata mana! Gama na damu ƙwarai saboda ku!
queria eu estar agora presente convosco, e mudar meu tom de voz, pois estou perplexo a vosso respeito.
21 Ku gaya mini, ku da kuke so ku zauna a ƙarƙashin Doka, ba ku san abin da Doka ta ce ba ne?
Respondei-me vós, que quereis estar sob a Lei: não ouvis a Lei?
22 Gama a rubuce yake cewa Ibrahim yana da’ya’ya biyu maza, ɗaya ta wurin mace’yar aikin gidansa, ɗaya kuma ta wurin ainihin matarsa.
Pois está escrito que Abraão tinha dois filhos: um da escrava, e outro da livre.
23 Ɗansa na wajen mace’yar aikin gidansa ya zo bisa ga ƙa’idar jiki ne; amma ɗansa na wajen ainihin matarsa ya zo a sakamakon alkawarin ne.
O da escrava nasceu segundo a carne, mas o da livre, pela promessa.
24 Za a iya ɗaukan waɗannan al’amura a matsayin misali, domin matan nan suna misalta alkawura biyu ne. Alkawari ɗaya daga Dutsen Sinai ne yana kuma haihuwar’ya’yan da za su zama bayi. Hagar ke nan.
Isto serve de ilustração, pois estes são dois pactos: um é o do monte Sinai, que gera filhos para a escravidão, que é Agar.
25 Hagar tana a matsayin Dutsen Sinai a Arabiya tana kuma kwatancin birnin Urushalima na yanzu, gama ita baiwa ce tare da’ya’yanta.
Ora, esta Agar é o monte Sinai, na Arábia, e corresponde à Jerusalém de agora, pois é escravizada com os filhos dela.
26 Amma Urushalimar da take sama’yantacciya ce, ita ce kuma mahaifiyarmu.
Mas a Jerusalém de cima é livre; esta é a nossa mãe.
27 Gama a rubuce yake cewa, “Ki yi farin ciki, ya ke bakararriya, wadda ba ta haihuwa ki ɓarke da murna, ki kuma tā da murya, ke da ba kya naƙuda; domin da yawa ne’ya’yan macen da aka yashe, fiye da na mai miji.”
Pois está escrito: Alegra-te, ó estéril, que não geras filhos; extravasa gritando de júbilo, tu, que não estás de parto; porque muitos mais são os filhos da solitária, que os da que tem marido.
28 To, ku’yan’uwa, ku’ya’yan alkawari ne kamar Ishaku.
Vós, porém, irmãos, como Isaque, sois filhos da promessa.
29 A wancan lokaci, wannan ɗa wanda aka haifa ta wurin ƙa’idar jiki ya tsananta wa wanda aka haifa ta ikon Ruhu. Haka ma yake har yanzu.
Porém, assim como naquele tempo o que nasceu segundo a carne perseguia o que [nasceu] segundo o Espírito, assim também é agora.
30 Amma me Nassi ya ce? Nassi ya ce, “Kori macen nan’yar aikin gida da ɗanta don ɗan mace’yar aikin gida ba zai taɓa raba gādo tare da ɗa na ainihin matarka ba.”
Mas o que diz a Escritura? Expulsa a escrava e o filho dela, porque de maneira nenhuma o filho da escrava herdará com o filho da livre.
31 Saboda haka,’yan’uwa, mu ba’ya’yan mace’yar aikin gida ba ne, amma na ainihin matan gidan ne.
Portanto, irmãos, não somos filhos da escrava, mas sim da livre.

< Galatiyawa 4 >