< Galatiyawa 4 >

1 Abin da nake nufi shi ne, muddin magāji yana ɗan yaro ne tukuna, babu bambanci tsakaninsa da bawa, ko da yake shi ne da mallakar kome.
Now as long as the heir is a child, he differeth nothing from a servant, though he is to be lord of all:
2 Yana ƙarƙashin iyayen goyonsa da masu riƙon amana har yă zuwa cikar lokacin da mahaifinsa ya sa.
but is under guardians and managers till the time appointed by the father.
3 Haka yake, sa’ad da muke’yan yara, mun kasance cikin bauta a ƙarƙashin ƙa’idodin duniya.
So we when we were children, were in servitude under the elements of the world:
4 Amma da lokacin da aka tsara ya yi sosai, sai Allah ya aiki Ɗansa, haifaffe daga mace, haifaffe a ƙarƙashin Doka,
but when the fulness of the time came, God sent forth his Son born of a woman made under the law,
5 domin yă fanshi waɗanda suke a ƙarƙashin doka, saboda mu sami cikakken matsayin zaman’ya’ya.
that He might redeem those that were under the law, that we might receive the adoption of sons.
6 Da yake ku’ya’ya ne, sai Allah ya aiko da Ruhun Ɗansa a cikin zukatanmu, Ruhun da yake kira, “Abba, Uba.”
And because ye are sons, God hath sent forth the Spirit of his Son into your hearts, crying, Abba, Father.
7 Saboda haka kai ba bawa ba ne kuma, kai ɗa ne; da yake kuwa kai ɗa ne, Allah ya mai da kai magāji.
So that thou art no longer a servant, but a son; and if a son, an heir also of God through Christ.
8 Dā da ba ku san Allah ba, ku bayi ne ga waɗanda a ainihi ba alloli ba ne.
But then indeed, when ye knew not God, ye served those which in reality are no gods.
9 Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma a ce Allah ya san ku, yaya kuke sāke komawa ga ƙa’idodin duniya marasa ƙarfi, abin tausayi kuma? Kuna so ku sāke komawa ga bautarsu ne?
But now that ye know God, or rather are known by God, how is it that ye turn again to the poor weak elements, to which ye desire again to be in bondage as before?
10 Kuna kiyaye ranaku da watanni da lokuta da shekaru na musamman!
Ye observe days, and months, and times, and years:
11 Kai, kun ba ni tsoro, don ya zama kamar duk wahalar da na yi a kanku banza ne!
so that I am afraid for you, least I have indeed bestowed upon you labour in vain.
12 Ina roƙonku’yan’uwa, ku zama kamar ni, gama na zama kamar ku. Ba ku yi mini wani laifi ba.
Brethren, I beseech you, be as I am; for I also was as ye are: and ye have not injured me at all.
13 Kun san rashin lafiyar da na yi, shi ne ya yi mini hanyar da na kawo muku bishara da farko.
But ye know that in the infirmity of the flesh I preached the gospel to you at first:
14 Ko da yake ciwona gwaji ne gare ku, ba ku yi mini reni ko ƙyama ba. A maimakon haka, kuka karɓe ni sai ka ce mala’ikan Allah, kuma sai ka ce Kiristi Yesu kansa.
and my temptation which was in my flesh ye despised not, nor rejected me for it; but received me as an angel of God, even as Christ Jesus.
15 Me ya faru da dukan farin cikinku? Na tabbata, a lokacin, da mai yiwuwa ne da kun ciccire idanunku kun ba ni.
What then was your blessedness? for I bear you witness that, if it had been possible, ye would have plucked out your own eyes, and have given them to me.
16 Yanzu na zama abokin gābanku don na faɗa muku gaskiya ke nan?
And am I become your enemy for telling you the truth?
17 Waɗancan mutane suna neman su rinjaye ku da ƙwazo, amma ba da kyakkyawar aniya ba. Abin da suke so shi ne su raba ku da mu, saboda ƙwazonku yă koma gare su.
They are zealous for you, but not as they ought: for they would exclude us, that ye may be zealous for them:
18 Yana da kyau ku kasance da irin wannan niyya idan da nufi mai kyau ne, ku kuma kasance a haka koyaushe ba sai ina tare da ku ba.
But it is good to be zealously affected always in that which is good, and not only when I am present with you.
19 Ya ku’ya’yana ƙaunatattu, ina sāke shan wahalar naƙudarku, har sai Kiristi ya kahu a cikinku.
My little children, of whom I do as it were travail in birth again,
20 Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canja muryata mana! Gama na damu ƙwarai saboda ku!
till Christ be formed in you, I should be glad to be present with you even now, and to change my voice; for I am in doubt about you.
21 Ku gaya mini, ku da kuke so ku zauna a ƙarƙashin Doka, ba ku san abin da Doka ta ce ba ne?
Tell me, you that are so desirous to be under the law, do ye not hear the law?
22 Gama a rubuce yake cewa Ibrahim yana da’ya’ya biyu maza, ɗaya ta wurin mace’yar aikin gidansa, ɗaya kuma ta wurin ainihin matarsa.
where it is written, that Abraham had two sons, one by a servant, and one by a free-woman?
23 Ɗansa na wajen mace’yar aikin gidansa ya zo bisa ga ƙa’idar jiki ne; amma ɗansa na wajen ainihin matarsa ya zo a sakamakon alkawarin ne.
But he who was of the servant, was born according to the course of nature; whereas the son of the free-woman was by virtue of the promise.
24 Za a iya ɗaukan waɗannan al’amura a matsayin misali, domin matan nan suna misalta alkawura biyu ne. Alkawari ɗaya daga Dutsen Sinai ne yana kuma haihuwar’ya’yan da za su zama bayi. Hagar ke nan.
Which things are figurative; for these persons are emblems of the two covenants, the one from mount Sinai, bringing forth children unto bondage, which is Hagar: for this name Hagar,
25 Hagar tana a matsayin Dutsen Sinai a Arabiya tana kuma kwatancin birnin Urushalima na yanzu, gama ita baiwa ce tare da’ya’yanta.
a rock, is expressive of mount Sinai in Arabia, and answereth to the present Jerusalem, which is in bondage with her children.
26 Amma Urushalimar da take sama’yantacciya ce, ita ce kuma mahaifiyarmu.
But the Jerusalem above is represented by the free-woman, which is the mother of us all.
27 Gama a rubuce yake cewa, “Ki yi farin ciki, ya ke bakararriya, wadda ba ta haihuwa ki ɓarke da murna, ki kuma tā da murya, ke da ba kya naƙuda; domin da yawa ne’ya’yan macen da aka yashe, fiye da na mai miji.”
For it is written, Rejoice thou barren, that for a while didst not bear, break forth and cry aloud for joy, thou that didst not travail with child; for many more are the children of the desolate than of her that hath an husband."
28 To, ku’yan’uwa, ku’ya’yan alkawari ne kamar Ishaku.
Now we, brethren, like Isaac, are children of the promise.
29 A wancan lokaci, wannan ɗa wanda aka haifa ta wurin ƙa’idar jiki ya tsananta wa wanda aka haifa ta ikon Ruhu. Haka ma yake har yanzu.
But as then he that was born after the flesh, persecuted him who was born after the Spirit, even so it is now.
30 Amma me Nassi ya ce? Nassi ya ce, “Kori macen nan’yar aikin gida da ɗanta don ɗan mace’yar aikin gida ba zai taɓa raba gādo tare da ɗa na ainihin matarka ba.”
But what saith the scripture? "Cast out the servant and her son: for the son of the servant shall not inherit with the son of the free-woman."
31 Saboda haka,’yan’uwa, mu ba’ya’yan mace’yar aikin gida ba ne, amma na ainihin matan gidan ne.
Now we, my brethren, are not children of the servant, but of the free-woman.

< Galatiyawa 4 >