< Galatiyawa 4 >

1 Abin da nake nufi shi ne, muddin magāji yana ɗan yaro ne tukuna, babu bambanci tsakaninsa da bawa, ko da yake shi ne da mallakar kome.
But I say, that the heir, as long as he is a minor, differs in no respect from a servant, though he is owner of all;
2 Yana ƙarƙashin iyayen goyonsa da masu riƙon amana har yă zuwa cikar lokacin da mahaifinsa ya sa.
but is under guardians and managers till the time appointed by the father.
3 Haka yake, sa’ad da muke’yan yara, mun kasance cikin bauta a ƙarƙashin ƙa’idodin duniya.
So, also, we, when we were minors, were in bondage under the rudiments of the world.
4 Amma da lokacin da aka tsara ya yi sosai, sai Allah ya aiki Ɗansa, haifaffe daga mace, haifaffe a ƙarƙashin Doka,
But when the fullness of the time came, God sent forth his Son, born of a woman, born under the law,
5 domin yă fanshi waɗanda suke a ƙarƙashin doka, saboda mu sami cikakken matsayin zaman’ya’ya.
that he might buy off those who were under the law, that we might receive the adoption.
6 Da yake ku’ya’ya ne, sai Allah ya aiko da Ruhun Ɗansa a cikin zukatanmu, Ruhun da yake kira, “Abba, Uba.”
And because you are sons, God has sent forth the Spirit of his Son into your hearts, crying, Abba, Father.
7 Saboda haka kai ba bawa ba ne kuma, kai ɗa ne; da yake kuwa kai ɗa ne, Allah ya mai da kai magāji.
So, then, you are no longer a servant, but a son; and if a son, an heir also of God, through Christ.
8 Dā da ba ku san Allah ba, ku bayi ne ga waɗanda a ainihi ba alloli ba ne.
But, then, because you knew not God, you were enslaved to those who, by nature, are not gods:
9 Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma a ce Allah ya san ku, yaya kuke sāke komawa ga ƙa’idodin duniya marasa ƙarfi, abin tausayi kuma? Kuna so ku sāke komawa ga bautarsu ne?
now, however, after having known God, rather indeed having been known by God, how is it that you are turning back to the weak and beggarly rudiments, to which you desire again to be in bondage, as at first?
10 Kuna kiyaye ranaku da watanni da lokuta da shekaru na musamman!
You observe days and months and times and years.
11 Kai, kun ba ni tsoro, don ya zama kamar duk wahalar da na yi a kanku banza ne!
fear for you, lest I have bestowed labor upon you in vain.
12 Ina roƙonku’yan’uwa, ku zama kamar ni, gama na zama kamar ku. Ba ku yi mini wani laifi ba.
Brethren, I beseech you, be as I am; because I was as you are. You have injured me in nothing.
13 Kun san rashin lafiyar da na yi, shi ne ya yi mini hanyar da na kawo muku bishara da farko.
You know that through weakness of the flesh I preached the gospel to you at the first:
14 Ko da yake ciwona gwaji ne gare ku, ba ku yi mini reni ko ƙyama ba. A maimakon haka, kuka karɓe ni sai ka ce mala’ikan Allah, kuma sai ka ce Kiristi Yesu kansa.
and my trial, which was in my flesh, you did not despise or loathe; but you received me as an angel of God, as Christ Jesus.
15 Me ya faru da dukan farin cikinku? Na tabbata, a lokacin, da mai yiwuwa ne da kun ciccire idanunku kun ba ni.
How great, then, was your blessedness! For I testify for you, that, if possible, you would have torn out your eyes, and have given them to me.
16 Yanzu na zama abokin gābanku don na faɗa muku gaskiya ke nan?
Have I then become your enemy, because I tell you the truth?
17 Waɗancan mutane suna neman su rinjaye ku da ƙwazo, amma ba da kyakkyawar aniya ba. Abin da suke so shi ne su raba ku da mu, saboda ƙwazonku yă koma gare su.
They are ardently attached to you, but not honorably; indeed, they desire to exclude us, that you may be ardently attached to them.
18 Yana da kyau ku kasance da irin wannan niyya idan da nufi mai kyau ne, ku kuma kasance a haka koyaushe ba sai ina tare da ku ba.
It is honorable to be ardently attached always, in what is honorable, and not only when I am present with you.
19 Ya ku’ya’yana ƙaunatattu, ina sāke shan wahalar naƙudarku, har sai Kiristi ya kahu a cikinku.
My little children, for whom I again suffer the pains of gestation, till Christ be formed in you,
20 Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canja muryata mana! Gama na damu ƙwarai saboda ku!
I desire to be present with you now, and to change my tone, for I am in doubt concerning you.
21 Ku gaya mini, ku da kuke so ku zauna a ƙarƙashin Doka, ba ku san abin da Doka ta ce ba ne?
Tell me, you that desire to be under the law, do you not understand the law?
22 Gama a rubuce yake cewa Ibrahim yana da’ya’ya biyu maza, ɗaya ta wurin mace’yar aikin gidansa, ɗaya kuma ta wurin ainihin matarsa.
For it is written, that Abraham had two sons; one by a bondmaid, and one by a free woman.
23 Ɗansa na wajen mace’yar aikin gidansa ya zo bisa ga ƙa’idar jiki ne; amma ɗansa na wajen ainihin matarsa ya zo a sakamakon alkawarin ne.
But the one by the bondmaid was born according to the flesh; the other, by the free woman, was by promise.
24 Za a iya ɗaukan waɗannan al’amura a matsayin misali, domin matan nan suna misalta alkawura biyu ne. Alkawari ɗaya daga Dutsen Sinai ne yana kuma haihuwar’ya’yan da za su zama bayi. Hagar ke nan.
These things are allegorized: for these women are the two covenants; the one from the Mount Sinai that brings forth for bondage, which is Hagar.
25 Hagar tana a matsayin Dutsen Sinai a Arabiya tana kuma kwatancin birnin Urushalima na yanzu, gama ita baiwa ce tare da’ya’yanta.
For Hagar represents Mount Sinai in Arabia, and corresponds to the present Jerusalem, for she is in bondage with her children.
26 Amma Urushalimar da take sama’yantacciya ce, ita ce kuma mahaifiyarmu.
But Jerusalem which is above is free; and she is the mother of us all.
27 Gama a rubuce yake cewa, “Ki yi farin ciki, ya ke bakararriya, wadda ba ta haihuwa ki ɓarke da murna, ki kuma tā da murya, ke da ba kya naƙuda; domin da yawa ne’ya’yan macen da aka yashe, fiye da na mai miji.”
For it is written: Rejoice you barren, that do not bear: break forth and cry aloud, you that travail not: for many more are the children of the deserted, than of her that had the husband of the deserted.
28 To, ku’yan’uwa, ku’ya’yan alkawari ne kamar Ishaku.
We, indeed, brethren, like Isaac, are children of promise.
29 A wancan lokaci, wannan ɗa wanda aka haifa ta wurin ƙa’idar jiki ya tsananta wa wanda aka haifa ta ikon Ruhu. Haka ma yake har yanzu.
But as then, he that was born according to the flesh persecuted him that was born according to the Spirit, so even now.
30 Amma me Nassi ya ce? Nassi ya ce, “Kori macen nan’yar aikin gida da ɗanta don ɗan mace’yar aikin gida ba zai taɓa raba gādo tare da ɗa na ainihin matarka ba.”
But what says the scripture? Cast out the bondwoman and her son; for the son of the bondwoman shall not be heir with the son of the free-woman.
31 Saboda haka,’yan’uwa, mu ba’ya’yan mace’yar aikin gida ba ne, amma na ainihin matan gidan ne.
Therefore, brethren, we are not children of the bondwoman, but of the free-woman.

< Galatiyawa 4 >