< Galatiyawa 4 >
1 Abin da nake nufi shi ne, muddin magāji yana ɗan yaro ne tukuna, babu bambanci tsakaninsa da bawa, ko da yake shi ne da mallakar kome.
Men jeg siger: Saa længe Arvingen er umyndig, er der ingen Forskel imellem ham og en Træl, skønt han er Herre over alt Godset;
2 Yana ƙarƙashin iyayen goyonsa da masu riƙon amana har yă zuwa cikar lokacin da mahaifinsa ya sa.
men han staar under Formyndere og Husholdere indtil den af Faderen bestemte Tid.
3 Haka yake, sa’ad da muke’yan yara, mun kasance cikin bauta a ƙarƙashin ƙa’idodin duniya.
Saaledes stode ogsaa vi, dengang vi vare umyndige, som Trælle under Verdens Børnelærdom.
4 Amma da lokacin da aka tsara ya yi sosai, sai Allah ya aiki Ɗansa, haifaffe daga mace, haifaffe a ƙarƙashin Doka,
Men da Tidens Fylde kom, udsendte Gud sin Søn, født af en Kvinde, født under Loven,
5 domin yă fanshi waɗanda suke a ƙarƙashin doka, saboda mu sami cikakken matsayin zaman’ya’ya.
for at han skulde løskøbe dem, som vare under Loven, for at vi skulde faa Sønneudkaarelsen.
6 Da yake ku’ya’ya ne, sai Allah ya aiko da Ruhun Ɗansa a cikin zukatanmu, Ruhun da yake kira, “Abba, Uba.”
Men fordi I ere Sønner, har Gud udsendt i vore Hjerter sin Søns Aand, som raaber: Abba, Fader!
7 Saboda haka kai ba bawa ba ne kuma, kai ɗa ne; da yake kuwa kai ɗa ne, Allah ya mai da kai magāji.
Altsaa er du ikke længer Træl, men Søn; men er du Søn, da er du ogsaa Arving ved Gud.
8 Dā da ba ku san Allah ba, ku bayi ne ga waɗanda a ainihi ba alloli ba ne.
Dengang derimod, da I ikke kendte Gud, trællede I for de Guder, som af Natur ikke ere det.
9 Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma a ce Allah ya san ku, yaya kuke sāke komawa ga ƙa’idodin duniya marasa ƙarfi, abin tausayi kuma? Kuna so ku sāke komawa ga bautarsu ne?
Men nu, da I have lært Gud at kende, ja, meget mere ere blevne kendte af Gud, hvor kunne I da atter vende tilbage til den svage og fattige Børnelærdom, som I atter forfra ville trælle under?
10 Kuna kiyaye ranaku da watanni da lokuta da shekaru na musamman!
I tage Vare paa Dage og Maaneder og Tider og Aar.
11 Kai, kun ba ni tsoro, don ya zama kamar duk wahalar da na yi a kanku banza ne!
Jeg frygter for, at jeg maaske har arbejdet forgæves paa eder.
12 Ina roƙonku’yan’uwa, ku zama kamar ni, gama na zama kamar ku. Ba ku yi mini wani laifi ba.
Vorder ligesom jeg, thi ogsaa jeg er bleven som I, Brødre! jeg beder eder. I have ikke gjort mig nogen Uret.
13 Kun san rashin lafiyar da na yi, shi ne ya yi mini hanyar da na kawo muku bishara da farko.
Men I vide, at det var paa Grund af en Kødets Svaghed, at jeg første Gang forkyndte Evangeliet for eder;
14 Ko da yake ciwona gwaji ne gare ku, ba ku yi mini reni ko ƙyama ba. A maimakon haka, kuka karɓe ni sai ka ce mala’ikan Allah, kuma sai ka ce Kiristi Yesu kansa.
og det, som i mit Kød var eder til Fristelse, ringeagtede I ikke og afskyede I ikke, men I modtoge mig som en Guds Engel, som Kristus Jesus.
15 Me ya faru da dukan farin cikinku? Na tabbata, a lokacin, da mai yiwuwa ne da kun ciccire idanunku kun ba ni.
Hvor er da nu eders Saligprisning? Thi jeg giver eder det Vidnesbyrd, at, om det havde været muligt, havde I udrevet eders Øjne og givet mig dem.
16 Yanzu na zama abokin gābanku don na faɗa muku gaskiya ke nan?
Saa er jeg vel bleven eders Fjende ved at tale Sandhed til eder?
17 Waɗancan mutane suna neman su rinjaye ku da ƙwazo, amma ba da kyakkyawar aniya ba. Abin da suke so shi ne su raba ku da mu, saboda ƙwazonku yă koma gare su.
De ere nidkære for eder, dog ikke for det gode; men de ville udelukke eder, for at I skulle være nidkære for dem.
18 Yana da kyau ku kasance da irin wannan niyya idan da nufi mai kyau ne, ku kuma kasance a haka koyaushe ba sai ina tare da ku ba.
Men det er godt at vise sig nidkær i det gode til enhver Tid, og ikke alene, naar jeg er nærværende hos eder.
19 Ya ku’ya’yana ƙaunatattu, ina sāke shan wahalar naƙudarku, har sai Kiristi ya kahu a cikinku.
Mine Børn, som jeg atter føder med Smerte, indtil Kristus har vundet Skikkelse i eder!
20 Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canja muryata mana! Gama na damu ƙwarai saboda ku!
— ja jeg vilde ønske, at jeg nu var til Stede hos eder og kunde omskifte min Røst; thi jeg er raadvild over for eder.
21 Ku gaya mini, ku da kuke so ku zauna a ƙarƙashin Doka, ba ku san abin da Doka ta ce ba ne?
Siger mig, I, som ville være under Loven, høre I ikke Loven?
22 Gama a rubuce yake cewa Ibrahim yana da’ya’ya biyu maza, ɗaya ta wurin mace’yar aikin gidansa, ɗaya kuma ta wurin ainihin matarsa.
Der er jo skrevet, at Abraham havde to Sønner, en med Tjenestekvinden og en med den frie Kvinde.
23 Ɗansa na wajen mace’yar aikin gidansa ya zo bisa ga ƙa’idar jiki ne; amma ɗansa na wajen ainihin matarsa ya zo a sakamakon alkawarin ne.
Men Tjenestekvindens Søn er avlet efter Kødet, den frie Kvindes ved Forjættelsen.
24 Za a iya ɗaukan waɗannan al’amura a matsayin misali, domin matan nan suna misalta alkawura biyu ne. Alkawari ɗaya daga Dutsen Sinai ne yana kuma haihuwar’ya’yan da za su zama bayi. Hagar ke nan.
Dette har en billedlig Betydning. Thi disse Kvinder ere tvende Pagter, den ene fra Sinai Bjerg, som føder til Trældom: Denne er Hagar.
25 Hagar tana a matsayin Dutsen Sinai a Arabiya tana kuma kwatancin birnin Urushalima na yanzu, gama ita baiwa ce tare da’ya’yanta.
Thi „Hagar‟ er Sinai Bjerg i Arabien, men svarer til det nuværende Jerusalem; thi det er i Trældom med sine Børn.
26 Amma Urushalimar da take sama’yantacciya ce, ita ce kuma mahaifiyarmu.
Men Jerusalem heroventil er frit, og hun er vor Moder.
27 Gama a rubuce yake cewa, “Ki yi farin ciki, ya ke bakararriya, wadda ba ta haihuwa ki ɓarke da murna, ki kuma tā da murya, ke da ba kya naƙuda; domin da yawa ne’ya’yan macen da aka yashe, fiye da na mai miji.”
Thi der er skrevet: „Fryd dig, du ufrugtbare, du, som ikke føder! bryd ud og raab, du, som ikke har Fødselsveer! thi mange ere den enliges Børn fremfor hendes, som har Manden.‟
28 To, ku’yan’uwa, ku’ya’yan alkawari ne kamar Ishaku.
Men vi, Brødre! ere Forjættelsens Børn i Lighed med Isak.
29 A wancan lokaci, wannan ɗa wanda aka haifa ta wurin ƙa’idar jiki ya tsananta wa wanda aka haifa ta ikon Ruhu. Haka ma yake har yanzu.
Men ligesom dengang han, som var avlet efter Kødet, forfulgte ham, som var avlet efter Aanden, saaledes ogsaa nu.
30 Amma me Nassi ya ce? Nassi ya ce, “Kori macen nan’yar aikin gida da ɗanta don ɗan mace’yar aikin gida ba zai taɓa raba gādo tare da ɗa na ainihin matarka ba.”
Men hvad siger Skriften: „Uddriv Tjenestekvinden og hendes Søn; thi Tjenestekvindens Søn skal ingenlunde arve med den frie Kvindes Søn.‟
31 Saboda haka,’yan’uwa, mu ba’ya’yan mace’yar aikin gida ba ne, amma na ainihin matan gidan ne.
Derfor, Brødre! ere vi ikke Tjenestekvindens Børn, men den frie Kvindes.