< Galatiyawa 3 >
1 Ya ku Galatiyawa marasa azanci! Wa ya ruɗe ku? A idanunku aka bayyana Yesu Kiristi gicciyeyye a sarari.
I uforstandige galatere! hvem har forgjort eder, I som har fått Jesus Kristus malt for øinene som korsfestet?
2 Zan so in san abu guda tak daga gare ku. Kun karɓi Ruhu ta wurin kiyaye Doka ne, ko kuwa ta wurin gaskata abin da kuka ji?
Bare dette vil jeg få vite av eder: Var det ved lov-gjerninger I fikk Ånden, eller ved troens forkynnelse?
3 Ashe, rashin azancinku har ya kai ga haka? Bayan kun fara da Ruhu, a yanzu kuma da halin mutuntaka za ku ƙarasa?
Er I så uforstandige? I begynte i Ånd; vil I nu fullende i kjød?
4 Ashe, wahaloli dabam-dabam da kuka sha sun zama a banza ke nan? Haka zai yiwu kuwa?
Så meget har I oplevd forgjeves! - om det da virkelig er forgjeves.
5 Allah ya ba ku Ruhunsa yana kuma aikata ayyukan banmamaki a cikinku saboda kuna kiyaye Doka ne, ko kuwa domin kuna gaskatawa abin da kuka ji ne?
Han altså som gir eder Ånden og virker kraftige gjerninger iblandt eder, gjør han det ved lov-gjerninger eller ved troens forkynnelse?
6 Ku dubi Ibrahim mana, “Ya gaskata Allah, aka kuwa lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
Likesom Abraham trodde Gud, og det blev regnet ham til rettferdighet.
7 Ku sani fa, waɗannan waɗanda suka gaskata,’ya’yan Ibrahim ne.
Derfor skal I vite at de som har tro, de er Abrahams barn.
8 Nassi ya hanga cewa Allah zai kuɓutar da Al’ummai ta wurin bangaskiya, ya kuwa sanar wa Ibrahim wannan bisharar tun kafin lokaci yă yi cewa, “Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinka.”
Og da Skriften forutså at det er ved tro Gud rettferdiggjør hedningene, forkynte den Abraham forut det evangelium: I dig skal alle folk velsignes.
9 Saboda haka waɗanda suke da bangaskiya sun sami albarka tare da Ibrahim, mutumin bangaskiya.
Så blir da de som har tro, velsignet med den troende Abraham.
10 Dukan waɗanda suka dogara ga kiyaye Doka la’anannu ne, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda bai ci gaba da yi dukan abubuwan da aka rubuta a Littafin Doka ba.”
For så mange som holder sig til lov-gjerninger, er under forbannelse; for det er skrevet: Forbannet er hver den som ikke blir ved i alt som er skrevet i lovens bok, så han gjør det!
11 A fili yake ba wanda zai kuɓuta a gaban Allah ta wurin Doka, domin “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
Og at ingen blir rettferdiggjort for Gud ved loven, er åpenbart; for: Den rettferdige, ved tro skal han leve;
12 Doka ba tă dangana ga bangaskiya ba; a maimakon haka, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
men loven har ikke noget med troen å gjøre, men: Den som gjør det, skal leve derved.
13 Kiristi ya fanshe mu daga la’anar Doka ta wurin zama la’ana saboda mu, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda aka rataye a kan itace.”
Kristus kjøpte oss fri fra lovens forbannelse, idet han blev en forbannelse for oss - for det er skrevet: Forbannet er hver den som henger på et tre -
14 Ya fanshe mu domin albarkar da aka yi wa Ibrahim yă zo ga Al’ummai, ta wurin Kiristi Yesu, domin ta wurin bangaskiya mu karɓi alkawarin Ruhu.
forat Abrahams velsignelse kunde komme over hedningene i Kristus Jesus, så vi ved troen kunde få Ånden, som var oss lovt.
15 ’Yan’uwa, bari in yi muku misali da rayuwarmu ta yau da kullum. Kamar dai yadda ba mai kawarwa ko yă ƙara wani abu cikin alkawarin da mutane suka kafa, haka yake a wannan batu.
Brødre! jeg taler på menneskelig vis. Selv en menneskelig pakt vil ingen gjøre til intet eller legge noget til efterat den er stadfestet.
16 Alkawaran nan fa ga Ibrahim ne aka faɗa da kuma wani zuriyarsa. Nassi bai ce, “da zuriyoyi ba” wanda ya nuna kamar mutane da yawa, amma “ga zuriyarka,” wanda yake nufin mutum ɗaya, wanda shi ne Kiristi.
Nu blev løftene gitt Abraham og hans ætt; han sier ikke: Og dine ætlinger, som om mange, men som om én: Og din ætt, og dette er Kristus.
17 Abin da nake nufi shi ne, Dokar da aka shigar ita bayan shekaru 430, ba tă kawar da alkawarin da Allah ya yi tun dā ba.
Dette er da min mening: En pakt som forut er stadfestet av Gud, gjør ikke loven, som er gitt fire hundre og tretti år efter, ugyldig, så den skulde gjøre løftet til intet.
18 Gama da a ce gādon yă dangana a kan doka ne, ai, da ba zai dangana a kan alkawari ba; amma Allah cikin alherinsa ya ba wa Ibrahim gādon ta wurin alkawari.
For får en arven ved lov, da får en den ikke lenger ved løfte; men Gud har gitt Abraham den ved løfte.
19 To, don me aka kawo Doka? An yi ƙari da Doka ne don fitowa da laifi fili har kafin na zuriyan nan ya zo, wanda aka yi wa alkawarin, an ba da doka ta wurin mala’iku ne, aka kuma danƙa ta a hannun matsakanci.
Hvad skulde da loven til? Den blev lagt til for overtredelsenes skyld, inntil den ætt kom som løftet gjaldt - gitt ved engler, ved en mellemmanns hånd;
20 Kuma akan bukaci wani a tsakani ne idan da mutum biyu ake zance, Allah kuwa ɗaya ne.
men en mellemmann er ikke bare for én; men Gud er én.
21 To, Dokar ce tana gāba da alkawaran Allah ke nan? Sam, ko kaɗan! Gama da a ce an ba da Dokar da tana iya ba da rai, tabbatacce, da sai a sami adalci ta wurin Doka.
Er da loven imot Guds løfter? Langt derifra! for var det gitt nogen lov som kunde gjøre levende, da kom rettferdigheten virkelig av loven;
22 Amma Nassi ya kulle kome a ƙarƙashin ikon zunubi, domin abin da aka yi alkawarin nan, da ake bayar ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi, a ba da shi ga waɗanda suka gaskata.
men Skriften har lagt alt inn under synd, forat det som var lovt, skulde ved tro på Jesus Kristus bli gitt dem som tror.
23 Kafin bangaskiyan nan tă zo, mun kasance a daure a kurkuku a ƙarƙashin Doka, a kulle sai da bangaskiyar da za tă zo ta bayyana.
Men før troen kom, blev vi holdt innestengt i varetekt under loven til den tro som skulde åpenbares.
24 Ta haka aka sa Dokar ta zama jagorarmu zuwa ga Kiristi don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya.
Så er da loven blitt vår tuktemester til Kristus, forat vi skulde bli rettferdiggjort av tro;
25 Yanzu da bangaskiya ta zo, ba sauran zamanmu a ƙarƙashin Doka.
men efterat troen er kommet, er vi ikke lenger under tuktemesteren;
26 Dukanku’ya’yan Allah ne ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
alle er I jo Guds barn ved troen på Kristus Jesus;
27 Gama dukanku da aka yi muku baftisma cikin Kiristi, kuna sanye da Kiristi ke nan.
for I, så mange som er døpt til Kristus, har iklædd eder Kristus.
28 Babu bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, bawa da’yantacce, namiji da ta mace, gama dukanku ɗaya ne cikin Kiristi Yesu.
Her er ikke jøde eller greker, her er ikke træl eller fri, her er ikke mann og kvinne; for I er alle én i Kristus Jesus.
29 In kuwa ku na Kiristi ne, to, ku zuriyar Ibrahim ne, magāda kuma bisa ga alkawarin nan.
Men hører I Kristus til, da er I jo Abrahams ætt, arvinger efter løfte.