< Galatiyawa 3 >
1 Ya ku Galatiyawa marasa azanci! Wa ya ruɗe ku? A idanunku aka bayyana Yesu Kiristi gicciyeyye a sarari.
ω ανοητοι γαλαται τισ υμασ εβασκανεν τη αληθεια μη πειθεσθαι οισ κατ οφθαλμουσ ιησουσ χριστοσ προεγραφη εν υμιν εσταυρωμενοσ
2 Zan so in san abu guda tak daga gare ku. Kun karɓi Ruhu ta wurin kiyaye Doka ne, ko kuwa ta wurin gaskata abin da kuka ji?
τουτο μονον θελω μαθειν αφ υμων εξ εργων νομου το πνευμα ελαβετε η εξ ακοησ πιστεωσ
3 Ashe, rashin azancinku har ya kai ga haka? Bayan kun fara da Ruhu, a yanzu kuma da halin mutuntaka za ku ƙarasa?
ουτωσ ανοητοι εστε εναρξαμενοι πνευματι νυν σαρκι επιτελεισθε
4 Ashe, wahaloli dabam-dabam da kuka sha sun zama a banza ke nan? Haka zai yiwu kuwa?
τοσαυτα επαθετε εικη ειγε και εικη
5 Allah ya ba ku Ruhunsa yana kuma aikata ayyukan banmamaki a cikinku saboda kuna kiyaye Doka ne, ko kuwa domin kuna gaskatawa abin da kuka ji ne?
ο ουν επιχορηγων υμιν το πνευμα και ενεργων δυναμεισ εν υμιν εξ εργων νομου η εξ ακοησ πιστεωσ
6 Ku dubi Ibrahim mana, “Ya gaskata Allah, aka kuwa lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
καθωσ αβρααμ επιστευσεν τω θεω και ελογισθη αυτω εισ δικαιοσυνην
7 Ku sani fa, waɗannan waɗanda suka gaskata,’ya’yan Ibrahim ne.
γινωσκετε αρα οτι οι εκ πιστεωσ ουτοι εισιν υιοι αβρααμ
8 Nassi ya hanga cewa Allah zai kuɓutar da Al’ummai ta wurin bangaskiya, ya kuwa sanar wa Ibrahim wannan bisharar tun kafin lokaci yă yi cewa, “Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinka.”
προιδουσα δε η γραφη οτι εκ πιστεωσ δικαιοι τα εθνη ο θεοσ προευηγγελισατο τω αβρααμ οτι ενευλογηθησονται εν σοι παντα τα εθνη
9 Saboda haka waɗanda suke da bangaskiya sun sami albarka tare da Ibrahim, mutumin bangaskiya.
ωστε οι εκ πιστεωσ ευλογουνται συν τω πιστω αβρααμ
10 Dukan waɗanda suka dogara ga kiyaye Doka la’anannu ne, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda bai ci gaba da yi dukan abubuwan da aka rubuta a Littafin Doka ba.”
οσοι γαρ εξ εργων νομου εισιν υπο καταραν εισιν γεγραπται γαρ επικαταρατοσ πασ οσ ουκ εμμενει εν πασιν τοισ γεγραμμενοισ εν τω βιβλιω του νομου του ποιησαι αυτα
11 A fili yake ba wanda zai kuɓuta a gaban Allah ta wurin Doka, domin “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
οτι δε εν νομω ουδεισ δικαιουται παρα τω θεω δηλον οτι ο δικαιοσ εκ πιστεωσ ζησεται
12 Doka ba tă dangana ga bangaskiya ba; a maimakon haka, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
ο δε νομοσ ουκ εστιν εκ πιστεωσ αλλ ο ποιησασ αυτα ανθρωποσ ζησεται εν αυτοισ
13 Kiristi ya fanshe mu daga la’anar Doka ta wurin zama la’ana saboda mu, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda aka rataye a kan itace.”
χριστοσ ημασ εξηγορασεν εκ τησ καταρασ του νομου γενομενοσ υπερ ημων καταρα γεγραπται γαρ επικαταρατοσ πασ ο κρεμαμενοσ επι ξυλου
14 Ya fanshe mu domin albarkar da aka yi wa Ibrahim yă zo ga Al’ummai, ta wurin Kiristi Yesu, domin ta wurin bangaskiya mu karɓi alkawarin Ruhu.
ινα εισ τα εθνη η ευλογια του αβρααμ γενηται εν χριστω ιησου ινα την επαγγελιαν του πνευματοσ λαβωμεν δια τησ πιστεωσ
15 ’Yan’uwa, bari in yi muku misali da rayuwarmu ta yau da kullum. Kamar dai yadda ba mai kawarwa ko yă ƙara wani abu cikin alkawarin da mutane suka kafa, haka yake a wannan batu.
αδελφοι κατα ανθρωπον λεγω ομωσ ανθρωπου κεκυρωμενην διαθηκην ουδεισ αθετει η επιδιατασσεται
16 Alkawaran nan fa ga Ibrahim ne aka faɗa da kuma wani zuriyarsa. Nassi bai ce, “da zuriyoyi ba” wanda ya nuna kamar mutane da yawa, amma “ga zuriyarka,” wanda yake nufin mutum ɗaya, wanda shi ne Kiristi.
τω δε αβρααμ ερρηθησαν αι επαγγελιαι και τω σπερματι αυτου ου λεγει και τοισ σπερμασιν ωσ επι πολλων αλλ ωσ εφ ενοσ και τω σπερματι σου οσ εστιν χριστοσ
17 Abin da nake nufi shi ne, Dokar da aka shigar ita bayan shekaru 430, ba tă kawar da alkawarin da Allah ya yi tun dā ba.
τουτο δε λεγω διαθηκην προκεκυρωμενην υπο του θεου εισ χριστον ο μετα ετη τετρακοσια και τριακοντα γεγονωσ νομοσ ουκ ακυροι εισ το καταργησαι την επαγγελιαν
18 Gama da a ce gādon yă dangana a kan doka ne, ai, da ba zai dangana a kan alkawari ba; amma Allah cikin alherinsa ya ba wa Ibrahim gādon ta wurin alkawari.
ει γαρ εκ νομου η κληρονομια ουκετι εξ επαγγελιασ τω δε αβρααμ δι επαγγελιασ κεχαρισται ο θεοσ
19 To, don me aka kawo Doka? An yi ƙari da Doka ne don fitowa da laifi fili har kafin na zuriyan nan ya zo, wanda aka yi wa alkawarin, an ba da doka ta wurin mala’iku ne, aka kuma danƙa ta a hannun matsakanci.
τι ουν ο νομοσ των παραβασεων χαριν προσετεθη αχρι ου ελθη το σπερμα ω επηγγελται διαταγεισ δι αγγελων εν χειρι μεσιτου
20 Kuma akan bukaci wani a tsakani ne idan da mutum biyu ake zance, Allah kuwa ɗaya ne.
ο δε μεσιτησ ενοσ ουκ εστιν ο δε θεοσ εισ εστιν
21 To, Dokar ce tana gāba da alkawaran Allah ke nan? Sam, ko kaɗan! Gama da a ce an ba da Dokar da tana iya ba da rai, tabbatacce, da sai a sami adalci ta wurin Doka.
ο ουν νομοσ κατα των επαγγελιων του θεου μη γενοιτο ει γαρ εδοθη νομοσ ο δυναμενοσ ζωοποιησαι οντωσ αν εκ νομου ην η δικαιοσυνη
22 Amma Nassi ya kulle kome a ƙarƙashin ikon zunubi, domin abin da aka yi alkawarin nan, da ake bayar ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi, a ba da shi ga waɗanda suka gaskata.
αλλα συνεκλεισεν η γραφη τα παντα υπο αμαρτιαν ινα η επαγγελια εκ πιστεωσ ιησου χριστου δοθη τοισ πιστευουσιν
23 Kafin bangaskiyan nan tă zo, mun kasance a daure a kurkuku a ƙarƙashin Doka, a kulle sai da bangaskiyar da za tă zo ta bayyana.
προ του δε ελθειν την πιστιν υπο νομον εφρουρουμεθα συγκεκλεισμενοι εισ την μελλουσαν πιστιν αποκαλυφθηναι
24 Ta haka aka sa Dokar ta zama jagorarmu zuwa ga Kiristi don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya.
ωστε ο νομοσ παιδαγωγοσ ημων γεγονεν εισ χριστον ινα εκ πιστεωσ δικαιωθωμεν
25 Yanzu da bangaskiya ta zo, ba sauran zamanmu a ƙarƙashin Doka.
ελθουσησ δε τησ πιστεωσ ουκετι υπο παιδαγωγον εσμεν
26 Dukanku’ya’yan Allah ne ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
παντεσ γαρ υιοι θεου εστε δια τησ πιστεωσ εν χριστω ιησου
27 Gama dukanku da aka yi muku baftisma cikin Kiristi, kuna sanye da Kiristi ke nan.
οσοι γαρ εισ χριστον εβαπτισθητε χριστον ενεδυσασθε
28 Babu bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, bawa da’yantacce, namiji da ta mace, gama dukanku ɗaya ne cikin Kiristi Yesu.
ουκ ενι ιουδαιοσ ουδε ελλην ουκ ενι δουλοσ ουδε ελευθεροσ ουκ ενι αρσεν και θηλυ παντεσ γαρ υμεισ εισ εστε εν χριστω ιησου
29 In kuwa ku na Kiristi ne, to, ku zuriyar Ibrahim ne, magāda kuma bisa ga alkawarin nan.
ει δε υμεισ χριστου αρα του αβρααμ σπερμα εστε και κατ επαγγελιαν κληρονομοι