< Galatiyawa 3 >

1 Ya ku Galatiyawa marasa azanci! Wa ya ruɗe ku? A idanunku aka bayyana Yesu Kiristi gicciyeyye a sarari.
Ô Galates insensés! qui est-ce qui vous a ensorcelés pour faire que vous n'obéissiez point à la vérité, vous à qui Jésus-Christ a été auparavant portrait devant les yeux, et crucifié entre vous?
2 Zan so in san abu guda tak daga gare ku. Kun karɓi Ruhu ta wurin kiyaye Doka ne, ko kuwa ta wurin gaskata abin da kuka ji?
Je voudrais seulement entendre ceci de vous: avez-vous reçu l'Esprit par les œuvres de la Loi, ou par la prédication de la foi?
3 Ashe, rashin azancinku har ya kai ga haka? Bayan kun fara da Ruhu, a yanzu kuma da halin mutuntaka za ku ƙarasa?
Etes-vous si insensés, qu'en ayant commencé par l'Esprit, maintenant vous finissiez par la chair?
4 Ashe, wahaloli dabam-dabam da kuka sha sun zama a banza ke nan? Haka zai yiwu kuwa?
Avez-vous tant souffert en vain? si toutefois c'est en vain.
5 Allah ya ba ku Ruhunsa yana kuma aikata ayyukan banmamaki a cikinku saboda kuna kiyaye Doka ne, ko kuwa domin kuna gaskatawa abin da kuka ji ne?
Celui donc qui vous donne l'Esprit, et qui produit en vous les dons miraculeux, [le fait-il] par les œuvres de la Loi, ou par la prédication de la foi?
6 Ku dubi Ibrahim mana, “Ya gaskata Allah, aka kuwa lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
Comme Abraham a cru à Dieu, et il lui a été imputé à justice;
7 Ku sani fa, waɗannan waɗanda suka gaskata,’ya’yan Ibrahim ne.
Sachez aussi que ceux qui sont de la foi, sont enfants d'Abraham.
8 Nassi ya hanga cewa Allah zai kuɓutar da Al’ummai ta wurin bangaskiya, ya kuwa sanar wa Ibrahim wannan bisharar tun kafin lokaci yă yi cewa, “Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinka.”
Aussi l'Ecriture prévoyant que Dieu justifierait les Gentils par la foi, a auparavant évangélisé à Abraham, en lui [disant]: toutes les nations seront bénies en toi.
9 Saboda haka waɗanda suke da bangaskiya sun sami albarka tare da Ibrahim, mutumin bangaskiya.
C'est pourquoi ceux qui sont de la foi, sont bénis avec le fidèle Abraham.
10 Dukan waɗanda suka dogara ga kiyaye Doka la’anannu ne, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda bai ci gaba da yi dukan abubuwan da aka rubuta a Littafin Doka ba.”
Mais tous ceux qui sont des œuvres de la Loi, sont sous la malédiction; car il est écrit: maudit est quiconque ne persévère pas dans toutes les choses qui sont écrites au Livre de la Loi pour les faire.
11 A fili yake ba wanda zai kuɓuta a gaban Allah ta wurin Doka, domin “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
Or que par la Loi personne ne soit justifié devant Dieu, cela paraît [par ce qui est dit]: que le juste vivra de la foi.
12 Doka ba tă dangana ga bangaskiya ba; a maimakon haka, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
Or la Loi n'est pas de la foi; mais l'homme qui aura fait ces choses, vivra par elles.
13 Kiristi ya fanshe mu daga la’anar Doka ta wurin zama la’ana saboda mu, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda aka rataye a kan itace.”
Christ nous a rachetés de la malédiction de la Loi, quand il a été fait malédiction pour nous; (car il est écrit: maudit est quiconque pend au bois.)
14 Ya fanshe mu domin albarkar da aka yi wa Ibrahim yă zo ga Al’ummai, ta wurin Kiristi Yesu, domin ta wurin bangaskiya mu karɓi alkawarin Ruhu.
Afin que la bénédiction d'Abraham parvînt aux Gentils par Jésus-Christ, et que nous reçussions par la foi l'Esprit qui avait été promis.
15 ’Yan’uwa, bari in yi muku misali da rayuwarmu ta yau da kullum. Kamar dai yadda ba mai kawarwa ko yă ƙara wani abu cikin alkawarin da mutane suka kafa, haka yake a wannan batu.
Mes frères, je vais vous parler à la manière des hommes. Si une alliance faite par un homme, est confirmée, nul ne la casse, ni n'y ajoute.
16 Alkawaran nan fa ga Ibrahim ne aka faɗa da kuma wani zuriyarsa. Nassi bai ce, “da zuriyoyi ba” wanda ya nuna kamar mutane da yawa, amma “ga zuriyarka,” wanda yake nufin mutum ɗaya, wanda shi ne Kiristi.
Or les promesses ont été faites à Abraham, et à sa semence; il n'est pas dit, et aux semences, comme s'il avait parlé de plusieurs, mais comme parlant d'une seule, et à sa semence: qui est Christ.
17 Abin da nake nufi shi ne, Dokar da aka shigar ita bayan shekaru 430, ba tă kawar da alkawarin da Allah ya yi tun dā ba.
Voici donc ce que je dis: c'est que quant à l'alliance qui a été auparavant confirmée par Dieu en Christ, la Loi qui est venue quatre cent-trente ans après, ne peut point l'annuler, pour abolir la promesse.
18 Gama da a ce gādon yă dangana a kan doka ne, ai, da ba zai dangana a kan alkawari ba; amma Allah cikin alherinsa ya ba wa Ibrahim gādon ta wurin alkawari.
Car si l'héritage est par la Loi, il n'est point par la promesse; or Dieu l'a donné à Abraham par la promesse.
19 To, don me aka kawo Doka? An yi ƙari da Doka ne don fitowa da laifi fili har kafin na zuriyan nan ya zo, wanda aka yi wa alkawarin, an ba da doka ta wurin mala’iku ne, aka kuma danƙa ta a hannun matsakanci.
A quoi donc [sert] la Loi? elle a été ajoutée à cause des transgressions, jusqu'à ce que vînt la semence à [l'égard de] laquelle la promesse avait été faite; et elle a été ordonnée par les Anges, par le ministère d'un Médiateur.
20 Kuma akan bukaci wani a tsakani ne idan da mutum biyu ake zance, Allah kuwa ɗaya ne.
Or le Médiateur n'est pas d'un seul: mais Dieu est un seul.
21 To, Dokar ce tana gāba da alkawaran Allah ke nan? Sam, ko kaɗan! Gama da a ce an ba da Dokar da tana iya ba da rai, tabbatacce, da sai a sami adalci ta wurin Doka.
La Loi donc [a-t-elle été ajoutée] contre les promesses de Dieu? nullement. Car si la Loi eût été donnée pour pouvoir vivifier, véritablement la justice serait de la Loi.
22 Amma Nassi ya kulle kome a ƙarƙashin ikon zunubi, domin abin da aka yi alkawarin nan, da ake bayar ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi, a ba da shi ga waɗanda suka gaskata.
Mais l'Ecriture a montré que tous les hommes étaient pécheurs, afin que la promesse par la foi en Jésus-Christ fût donnée à ceux qui croient.
23 Kafin bangaskiyan nan tă zo, mun kasance a daure a kurkuku a ƙarƙashin Doka, a kulle sai da bangaskiyar da za tă zo ta bayyana.
Or avant que la foi vînt, nous étions gardés sous la Loi, étant renfermés [sous l'attente] de la foi qui devait être révélée.
24 Ta haka aka sa Dokar ta zama jagorarmu zuwa ga Kiristi don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya.
La Loi a donc été notre Pédagogue [pour nous amener] à Christ, afin que nous soyons justifiés par la foi.
25 Yanzu da bangaskiya ta zo, ba sauran zamanmu a ƙarƙashin Doka.
Mais la foi étant venue, nous ne sommes plus sous le Pédagogue.
26 Dukanku’ya’yan Allah ne ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
Parce que vous êtes tous enfants de Dieu par la foi en Jésus-Christ.
27 Gama dukanku da aka yi muku baftisma cikin Kiristi, kuna sanye da Kiristi ke nan.
Car vous tous qui avez été baptisés en Christ, vous avez revêtu Christ;
28 Babu bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, bawa da’yantacce, namiji da ta mace, gama dukanku ɗaya ne cikin Kiristi Yesu.
[Où] il n'y a ni Juif ni Grec; [où] il n'y a ni esclave ni libre; [où] il n'y a ni mâle ni femelle; car vous êtes tous un en Jésus-Christ.
29 In kuwa ku na Kiristi ne, to, ku zuriyar Ibrahim ne, magāda kuma bisa ga alkawarin nan.
Or si vous êtes de Christ, vous êtes donc la semence d'Abraham, et héritiers selon la promesse.

< Galatiyawa 3 >