< Galatiyawa 3 >
1 Ya ku Galatiyawa marasa azanci! Wa ya ruɗe ku? A idanunku aka bayyana Yesu Kiristi gicciyeyye a sarari.
O foolish Galatians! Who has bewitched you to keep you from obeying the truth? In your presence, before your very eyes, Jesus Christ was publicly portrayed as crucified.
2 Zan so in san abu guda tak daga gare ku. Kun karɓi Ruhu ta wurin kiyaye Doka ne, ko kuwa ta wurin gaskata abin da kuka ji?
Let me ask you this one question: Did you receive the Spirit by works of the law or by hearing with faith?
3 Ashe, rashin azancinku har ya kai ga haka? Bayan kun fara da Ruhu, a yanzu kuma da halin mutuntaka za ku ƙarasa?
Are you so foolish? Having begun by the Spirit, are you now trying to be perfected by the flesh?
4 Ashe, wahaloli dabam-dabam da kuka sha sun zama a banza ke nan? Haka zai yiwu kuwa?
Did you suffer so much in vain?—if indeed it was in vain.
5 Allah ya ba ku Ruhunsa yana kuma aikata ayyukan banmamaki a cikinku saboda kuna kiyaye Doka ne, ko kuwa domin kuna gaskatawa abin da kuka ji ne?
Does God supply you with the Spirit and work miracles among you because you perform the works of the law or because you hear with faith?
6 Ku dubi Ibrahim mana, “Ya gaskata Allah, aka kuwa lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
Remember, “Abraham believed God, and it was counted to him as righteousness.”
7 Ku sani fa, waɗannan waɗanda suka gaskata,’ya’yan Ibrahim ne.
Therefore you must understand that those who have faith are the sons of Abraham.
8 Nassi ya hanga cewa Allah zai kuɓutar da Al’ummai ta wurin bangaskiya, ya kuwa sanar wa Ibrahim wannan bisharar tun kafin lokaci yă yi cewa, “Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinka.”
Now the Scripture, foreseeing that God would justify the Gentiles by faith, preached the gospel beforehand to Abraham, saying, “All the nations will be blessed in yoʋ.”
9 Saboda haka waɗanda suke da bangaskiya sun sami albarka tare da Ibrahim, mutumin bangaskiya.
So then, those who have faith are blessed along with Abraham, the man of faith.
10 Dukan waɗanda suka dogara ga kiyaye Doka la’anannu ne, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda bai ci gaba da yi dukan abubuwan da aka rubuta a Littafin Doka ba.”
For all who rely on the works of the law are under a curse, because it is written, “Cursed is everyone who does not continue to do everything written in the Book of the Law.”
11 A fili yake ba wanda zai kuɓuta a gaban Allah ta wurin Doka, domin “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
Now it is evident that no one is justified before God by the law, because “the righteous will live by faith.”
12 Doka ba tă dangana ga bangaskiya ba; a maimakon haka, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
But the law is not based on faith; on the contrary, “The person who does these things will live by them.”
13 Kiristi ya fanshe mu daga la’anar Doka ta wurin zama la’ana saboda mu, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda aka rataye a kan itace.”
Christ redeemed us from the curse of the law by becoming a curse for us, for it is written, “Cursed is everyone who hangs on a tree.”
14 Ya fanshe mu domin albarkar da aka yi wa Ibrahim yă zo ga Al’ummai, ta wurin Kiristi Yesu, domin ta wurin bangaskiya mu karɓi alkawarin Ruhu.
He redeemed us so that the blessing of Abraham would come to the Gentiles in Christ Jesus, so that we could receive the promise of the Spirit through faith.
15 ’Yan’uwa, bari in yi muku misali da rayuwarmu ta yau da kullum. Kamar dai yadda ba mai kawarwa ko yă ƙara wani abu cikin alkawarin da mutane suka kafa, haka yake a wannan batu.
Brothers, let me give an example from everyday life: When a man-made covenant is ratified, no one annuls it or adds to it.
16 Alkawaran nan fa ga Ibrahim ne aka faɗa da kuma wani zuriyarsa. Nassi bai ce, “da zuriyoyi ba” wanda ya nuna kamar mutane da yawa, amma “ga zuriyarka,” wanda yake nufin mutum ɗaya, wanda shi ne Kiristi.
Now the promises were spoken to Abraham and to his descendant. Scripture does not say, “And to his descendants,” referring to many, but referring to one man it says, “And to yoʋr descendant,” who is Christ.
17 Abin da nake nufi shi ne, Dokar da aka shigar ita bayan shekaru 430, ba tă kawar da alkawarin da Allah ya yi tun dā ba.
My point is this: The law, which came four hundred and thirty years later, cannot annul a covenant previously ratified by God to Christ, so as to invalidate the promise.
18 Gama da a ce gādon yă dangana a kan doka ne, ai, da ba zai dangana a kan alkawari ba; amma Allah cikin alherinsa ya ba wa Ibrahim gādon ta wurin alkawari.
For if the inheritance comes by the law, it no longer comes by the promise; but God granted it to Abraham by a promise.
19 To, don me aka kawo Doka? An yi ƙari da Doka ne don fitowa da laifi fili har kafin na zuriyan nan ya zo, wanda aka yi wa alkawarin, an ba da doka ta wurin mala’iku ne, aka kuma danƙa ta a hannun matsakanci.
Why then was the law given? It was added because of transgressions, until the descendant should come to whom the promise had been made. It was ordained through angels by the hand of a mediator.
20 Kuma akan bukaci wani a tsakani ne idan da mutum biyu ake zance, Allah kuwa ɗaya ne.
Now a mediator does not represent just one party, but God is one.
21 To, Dokar ce tana gāba da alkawaran Allah ke nan? Sam, ko kaɗan! Gama da a ce an ba da Dokar da tana iya ba da rai, tabbatacce, da sai a sami adalci ta wurin Doka.
Is the law then opposed to the promises of God? Certainly not! For if a law had been given that was able to give life, truly righteousness would have come through the law.
22 Amma Nassi ya kulle kome a ƙarƙashin ikon zunubi, domin abin da aka yi alkawarin nan, da ake bayar ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi, a ba da shi ga waɗanda suka gaskata.
But the Scripture has confined all under sin, so that the promise might be given on the basis of faith in Jesus Christ to those who believe.
23 Kafin bangaskiyan nan tă zo, mun kasance a daure a kurkuku a ƙarƙashin Doka, a kulle sai da bangaskiyar da za tă zo ta bayyana.
Now before faith came, we were kept in custody under the law, confined until the faith that was to come would be revealed.
24 Ta haka aka sa Dokar ta zama jagorarmu zuwa ga Kiristi don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya.
The law, then, was our guardian until Christ came, so that we could be justified by faith.
25 Yanzu da bangaskiya ta zo, ba sauran zamanmu a ƙarƙashin Doka.
But now that faith has come, we are no longer under a guardian,
26 Dukanku’ya’yan Allah ne ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
for you are all sons of God through faith in Christ Jesus.
27 Gama dukanku da aka yi muku baftisma cikin Kiristi, kuna sanye da Kiristi ke nan.
For all of you who were baptized into Christ have put on Christ.
28 Babu bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, bawa da’yantacce, namiji da ta mace, gama dukanku ɗaya ne cikin Kiristi Yesu.
There is neither Jew nor Greek, there is neither slave nor free, there is neither male nor female, for you are all one in Christ Jesus.
29 In kuwa ku na Kiristi ne, to, ku zuriyar Ibrahim ne, magāda kuma bisa ga alkawarin nan.
And if you belong to Christ, then you are Abraham's descendants and heirs according to the promise.