< Galatiyawa 3 >

1 Ya ku Galatiyawa marasa azanci! Wa ya ruɗe ku? A idanunku aka bayyana Yesu Kiristi gicciyeyye a sarari.
O thoughtless Galatians, who bewitched you, not to obey the truth—before whose eyes [it] was previously written [about] Jesus Christ having been crucified?
2 Zan so in san abu guda tak daga gare ku. Kun karɓi Ruhu ta wurin kiyaye Doka ne, ko kuwa ta wurin gaskata abin da kuka ji?
I only wish to learn this from you: did you receive the Spirit by works of the Law, or by the hearing of faith?
3 Ashe, rashin azancinku har ya kai ga haka? Bayan kun fara da Ruhu, a yanzu kuma da halin mutuntaka za ku ƙarasa?
Are you so thoughtless? Having begun in the Spirit, do you now end in the flesh?
4 Ashe, wahaloli dabam-dabam da kuka sha sun zama a banza ke nan? Haka zai yiwu kuwa?
So many things you suffered in vain! If, indeed, even in vain.
5 Allah ya ba ku Ruhunsa yana kuma aikata ayyukan banmamaki a cikinku saboda kuna kiyaye Doka ne, ko kuwa domin kuna gaskatawa abin da kuka ji ne?
He, therefore, who is supplying the Spirit to you and working mighty acts among you—[is it] by works of law or by the hearing of faith?
6 Ku dubi Ibrahim mana, “Ya gaskata Allah, aka kuwa lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
According as Abraham believed God, and it was reckoned to him for righteousness;
7 Ku sani fa, waɗannan waɗanda suka gaskata,’ya’yan Ibrahim ne.
know, then, that those of faith—these are sons of Abraham,
8 Nassi ya hanga cewa Allah zai kuɓutar da Al’ummai ta wurin bangaskiya, ya kuwa sanar wa Ibrahim wannan bisharar tun kafin lokaci yă yi cewa, “Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinka.”
and the Writing, having foreseen that God declares righteous the nations by faith, foretold the good news to Abraham:
9 Saboda haka waɗanda suke da bangaskiya sun sami albarka tare da Ibrahim, mutumin bangaskiya.
“All the nations will be blessed in you”; so that those of faith are blessed with the believing Abraham,
10 Dukan waɗanda suka dogara ga kiyaye Doka la’anannu ne, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda bai ci gaba da yi dukan abubuwan da aka rubuta a Littafin Doka ba.”
for as many as are of works of law are under a curse, for it has been written: “Cursed [is] everyone who is not remaining in all things that have been written in the Scroll of the Law—to do them,”
11 A fili yake ba wanda zai kuɓuta a gaban Allah ta wurin Doka, domin “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
and [it] is evident that in law no one is declared righteous with God, because “The righteous will live by faith”;
12 Doka ba tă dangana ga bangaskiya ba; a maimakon haka, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
and the Law is not by faith, rather, “The man who did them will live in them.”
13 Kiristi ya fanshe mu daga la’anar Doka ta wurin zama la’ana saboda mu, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda aka rataye a kan itace.”
Christ redeemed us from the curse of the Law, having become a curse for us, for it has been written: “Cursed is everyone who is hanging on a tree,”
14 Ya fanshe mu domin albarkar da aka yi wa Ibrahim yă zo ga Al’ummai, ta wurin Kiristi Yesu, domin ta wurin bangaskiya mu karɓi alkawarin Ruhu.
that the blessing of Abraham may come to the nations in Christ Jesus, that we may receive the promise of the Spirit through faith.
15 ’Yan’uwa, bari in yi muku misali da rayuwarmu ta yau da kullum. Kamar dai yadda ba mai kawarwa ko yă ƙara wani abu cikin alkawarin da mutane suka kafa, haka yake a wannan batu.
Brothers, I say [it] as a man, no one even makes void or adds to a confirmed covenant of man,
16 Alkawaran nan fa ga Ibrahim ne aka faɗa da kuma wani zuriyarsa. Nassi bai ce, “da zuriyoyi ba” wanda ya nuna kamar mutane da yawa, amma “ga zuriyarka,” wanda yake nufin mutum ɗaya, wanda shi ne Kiristi.
and to Abraham were the promises spoken, and to his Seed; He does not say, “And to seeds,” as of many, but as of one, “And to your Seed,” which is Christ;
17 Abin da nake nufi shi ne, Dokar da aka shigar ita bayan shekaru 430, ba tă kawar da alkawarin da Allah ya yi tun dā ba.
and this I say, a covenant confirmed before by God to Christ, the Law, that came four hundred and thirty years after, does not set aside, to make void the promise,
18 Gama da a ce gādon yă dangana a kan doka ne, ai, da ba zai dangana a kan alkawari ba; amma Allah cikin alherinsa ya ba wa Ibrahim gādon ta wurin alkawari.
for if the inheritance [is] by law, [it is] no longer by promise, but God granted [it] to Abraham through promise.
19 To, don me aka kawo Doka? An yi ƙari da Doka ne don fitowa da laifi fili har kafin na zuriyan nan ya zo, wanda aka yi wa alkawarin, an ba da doka ta wurin mala’iku ne, aka kuma danƙa ta a hannun matsakanci.
Why, then, the Law? It was added on account of the transgressions, until the Seed might come to which the promise has been made, having been set in order through messengers in the hand of a mediator—
20 Kuma akan bukaci wani a tsakani ne idan da mutum biyu ake zance, Allah kuwa ɗaya ne.
and the mediator is not of one, but God is one.
21 To, Dokar ce tana gāba da alkawaran Allah ke nan? Sam, ko kaɗan! Gama da a ce an ba da Dokar da tana iya ba da rai, tabbatacce, da sai a sami adalci ta wurin Doka.
[Is] the Law, then, against the promises of God? Let it not be! For if a law was given that was able to make alive, truly there would have been righteousness by law,
22 Amma Nassi ya kulle kome a ƙarƙashin ikon zunubi, domin abin da aka yi alkawarin nan, da ake bayar ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi, a ba da shi ga waɗanda suka gaskata.
but the Writing shut up the whole under sin, that the promise by faith of Jesus Christ may be given to those believing.
23 Kafin bangaskiyan nan tă zo, mun kasance a daure a kurkuku a ƙarƙashin Doka, a kulle sai da bangaskiyar da za tă zo ta bayyana.
And before the coming of faith, we were being kept under law, shut up to the faith about to be revealed,
24 Ta haka aka sa Dokar ta zama jagorarmu zuwa ga Kiristi don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya.
so that the Law became our tutor—to Christ, that we may be declared righteous by faith,
25 Yanzu da bangaskiya ta zo, ba sauran zamanmu a ƙarƙashin Doka.
and faith having come, we are no longer under a tutor,
26 Dukanku’ya’yan Allah ne ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
for you are all sons of God through faith in Christ Jesus,
27 Gama dukanku da aka yi muku baftisma cikin Kiristi, kuna sanye da Kiristi ke nan.
for as many as were immersed into Christ put on Christ;
28 Babu bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, bawa da’yantacce, namiji da ta mace, gama dukanku ɗaya ne cikin Kiristi Yesu.
there is neither Jew nor Greek, there is neither servant nor freeman, there is neither male and female, for you are all one in Christ Jesus;
29 In kuwa ku na Kiristi ne, to, ku zuriyar Ibrahim ne, magāda kuma bisa ga alkawarin nan.
and if you [are] of Christ then you are seed of Abraham, and heirs according to promise.

< Galatiyawa 3 >