< Galatiyawa 3 >

1 Ya ku Galatiyawa marasa azanci! Wa ya ruɗe ku? A idanunku aka bayyana Yesu Kiristi gicciyeyye a sarari.
O foolish Galatians, who bewitched you not to obey the truth, before whose eyes Jesus Christ was earlier described among you, crucified?
2 Zan so in san abu guda tak daga gare ku. Kun karɓi Ruhu ta wurin kiyaye Doka ne, ko kuwa ta wurin gaskata abin da kuka ji?
I only want to learn this from you. Did ye receive the Spirit from works of law, or from a listening ear of faith?
3 Ashe, rashin azancinku har ya kai ga haka? Bayan kun fara da Ruhu, a yanzu kuma da halin mutuntaka za ku ƙarasa?
Are ye so foolish, having begun in Spirit, are ye now made perfect by flesh?
4 Ashe, wahaloli dabam-dabam da kuka sha sun zama a banza ke nan? Haka zai yiwu kuwa?
Did ye suffer so many things in vain? If it is indeed in vain.
5 Allah ya ba ku Ruhunsa yana kuma aikata ayyukan banmamaki a cikinku saboda kuna kiyaye Doka ne, ko kuwa domin kuna gaskatawa abin da kuka ji ne?
He therefore who supplies the Spirit to you and who works miracles among you, is it from works of law or from a listening ear of faith?
6 Ku dubi Ibrahim mana, “Ya gaskata Allah, aka kuwa lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
Just as Abraham believed God, and it was reckoned to him for righteousness.
7 Ku sani fa, waɗannan waɗanda suka gaskata,’ya’yan Ibrahim ne.
Ye know therefore that those from faith, these are sons of Abraham.
8 Nassi ya hanga cewa Allah zai kuɓutar da Al’ummai ta wurin bangaskiya, ya kuwa sanar wa Ibrahim wannan bisharar tun kafin lokaci yă yi cewa, “Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinka.”
And the scripture having foreseen that God makes the Gentiles righteous from faith, proclaimed the good news in advance to Abraham: In thee all the nations will be blessed.
9 Saboda haka waɗanda suke da bangaskiya sun sami albarka tare da Ibrahim, mutumin bangaskiya.
So then those from faith are blessed with the faithful Abraham.
10 Dukan waɗanda suka dogara ga kiyaye Doka la’anannu ne, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda bai ci gaba da yi dukan abubuwan da aka rubuta a Littafin Doka ba.”
For as many as are from works of law are under a curse, for it is written, Cursed is every man who does not continue in all things written in the book of the law, to do them.
11 A fili yake ba wanda zai kuɓuta a gaban Allah ta wurin Doka, domin “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
But that no man is made righteous by law before God, is evident, because, The righteous man will live from faith.
12 Doka ba tă dangana ga bangaskiya ba; a maimakon haka, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
And the law is not from faith, but the man who does them will live in them.
13 Kiristi ya fanshe mu daga la’anar Doka ta wurin zama la’ana saboda mu, gama a rubuce yake cewa, “La’ananne ne duk wanda aka rataye a kan itace.”
Christ redeemed us from the curse of the law, having become a curse for us. For it is written, Cursed is every man who hangs on a tree.
14 Ya fanshe mu domin albarkar da aka yi wa Ibrahim yă zo ga Al’ummai, ta wurin Kiristi Yesu, domin ta wurin bangaskiya mu karɓi alkawarin Ruhu.
So that the blessing of Abraham might occur for the Gentiles in Christ Jesus, so that we might receive the promise of the Spirit through the faith.
15 ’Yan’uwa, bari in yi muku misali da rayuwarmu ta yau da kullum. Kamar dai yadda ba mai kawarwa ko yă ƙara wani abu cikin alkawarin da mutane suka kafa, haka yake a wannan batu.
Brothers (I speak according to a man), in the same way of a man, no man annuls or adds to a contract that has been ratified.
16 Alkawaran nan fa ga Ibrahim ne aka faɗa da kuma wani zuriyarsa. Nassi bai ce, “da zuriyoyi ba” wanda ya nuna kamar mutane da yawa, amma “ga zuriyarka,” wanda yake nufin mutum ɗaya, wanda shi ne Kiristi.
Now the promises were spoken to Abraham and to his seed. He does not say, And to the seeds, as of many, but as of one, And to thy seed, who is Christ.
17 Abin da nake nufi shi ne, Dokar da aka shigar ita bayan shekaru 430, ba tă kawar da alkawarin da Allah ya yi tun dā ba.
And I say this, a covenant previously confirmed by God in Christ, the law, which happened four hundred and thirty years after, does not annul in order to make the promise useless.
18 Gama da a ce gādon yă dangana a kan doka ne, ai, da ba zai dangana a kan alkawari ba; amma Allah cikin alherinsa ya ba wa Ibrahim gādon ta wurin alkawari.
For if the inheritance is from law, it is no longer from promise. But God has given it to Abraham through promise.
19 To, don me aka kawo Doka? An yi ƙari da Doka ne don fitowa da laifi fili har kafin na zuriyan nan ya zo, wanda aka yi wa alkawarin, an ba da doka ta wurin mala’iku ne, aka kuma danƙa ta a hannun matsakanci.
Why then the law? It was added on account of transgressions, until the seed would come to whom it was promised, which was arranged through agents in the hand of a mediator.
20 Kuma akan bukaci wani a tsakani ne idan da mutum biyu ake zance, Allah kuwa ɗaya ne.
Now a mediator is not of one, but God is one.
21 To, Dokar ce tana gāba da alkawaran Allah ke nan? Sam, ko kaɗan! Gama da a ce an ba da Dokar da tana iya ba da rai, tabbatacce, da sai a sami adalci ta wurin Doka.
Is the law therefore against the promises of God? May it not happen! For if a law was given that could make alive, truly righteousness would be from law.
22 Amma Nassi ya kulle kome a ƙarƙashin ikon zunubi, domin abin da aka yi alkawarin nan, da ake bayar ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi, a ba da shi ga waɗanda suka gaskata.
But scripture confined all things under sin, so that the promise from faith in Jesus Christ might be given to those who believe.
23 Kafin bangaskiyan nan tă zo, mun kasance a daure a kurkuku a ƙarƙashin Doka, a kulle sai da bangaskiyar da za tă zo ta bayyana.
But before faith came we were kept in custody under law, having been confined for faith that was going to be revealed.
24 Ta haka aka sa Dokar ta zama jagorarmu zuwa ga Kiristi don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya.
So that the law became our schoolmaster for Christ, so that we might be made righteous from faith.
25 Yanzu da bangaskiya ta zo, ba sauran zamanmu a ƙarƙashin Doka.
But faith having come, we are no longer under a schoolmaster.
26 Dukanku’ya’yan Allah ne ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
For ye are all sons of God through faith in Christ Jesus.
27 Gama dukanku da aka yi muku baftisma cikin Kiristi, kuna sanye da Kiristi ke nan.
For as many as were immersed into Christ have put on Christ.
28 Babu bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, bawa da’yantacce, namiji da ta mace, gama dukanku ɗaya ne cikin Kiristi Yesu.
There is no Jew nor Greek, there is no bondman nor freeman, there is no male and female, for ye are all one in Christ Jesus.
29 In kuwa ku na Kiristi ne, to, ku zuriyar Ibrahim ne, magāda kuma bisa ga alkawarin nan.
And if ye are Christ's, then ye are Abraham's seed and heirs according to promise.

< Galatiyawa 3 >