< Galatiyawa 2 >

1 Bayan shekara goma sha huɗu sai na sāke haurawa zuwa Urushalima, a wannan lokaci na tafi tare da Barnabas. Na kuma ɗauki Titus muka tafi tare.
Then fourteen years after I went again to Jerusalem with Barnabas, and took Titus with [me] also.
2 Na tafi ne bisa ga wani wahayi. Da na kai can, sai na bayyana musu bisharar da nake wa’azi a cikin Al’ummai. Na yi haka a keɓance a gaban waɗanda suke shugabanni, don tsoro kada gudun da nake yi, ko kuwa na riga na yi, yă zama a banza.
And I went by revelation, and communicated to them that gospel which I preach among the Gentiles, but privately to them who were of reputation, lest by any means I should run, or had run in vain.
3 Amma ko Titus ma da yake tare da ni, ba a ce dole sai ya yi kaciya ba, ko da yake shi mutumin Al’ummai ne.
But neither Titus, who was with me, being a Greek, was compelled to be circumcised:
4 Wannan zancen kaciya ya taso domin waɗansu’yan’uwan ƙarya sun shiga cikinmu domin su yi leƙe a kan’yancin da muke da shi a cikin Kiristi Yesu, su kuma mai da mu bayi.
And that because of false brethren unawares brought in, who came in privately to spy out our liberty which we have in Christ Jesus, that they might bring us into bondage:
5 Ba mu kuwa ba su zarafi ba ko kaɗan, don gaskiyar bishara ta ci gaba da kasance tare da ku.
To whom we gave place by subjection, no, not for an hour; that the truth of the gospel might continue with you.
6 Game da waɗanda aka ɗauka a dā a kan su wani abu ne, ko wane ne su, duk ɗaya ne a wurina; gama Allah ba ya nuna bambanci, ina dai gaya muku waɗannan da suke wani abu ne a dā, ba su ƙara mini kome ba.
But of these, who seemed to be somewhat, (whatever they were, it maketh no matter to me: God accepteth no man's person: ) for they who seemed [to be somewhat], in conference added nothing to me:
7 A maimakon haka, sun ga cewa an danƙa mini hakkin wa’azin bishara ga Al’ummai, kamar yadda aka danƙa wa Bitrus ga Yahudawa.
But on the contrary, when they saw that the gospel of the uncircumcision was committed to me, as [the gospel] of the circumcision [was] to Peter;
8 Gama Allah wanda ya yi aiki a cikin hidimar Bitrus a matsayin manzo ga Yahudawa, haka ma ya yi aiki a cikin hidimata a matsayin manzo ga Al’ummai.
(For he that wrought effectually in Peter to the apostleship of the circumcision, the same was mighty in me towards the Gentiles: )
9 Yaƙub, Bitrus da Yohanna waɗanda suke fitattun ginshiƙai, sun karɓe ni da Barnabas da hannu biyu biyu sa’ad da suka gane alherin da aka ba ni. Suka kuma yarda cewa ya kamata mu tafi wajen Al’ummai, su kuwa su tafi wajen Yahudawa.
And when James, Cephas, and John, who seemed to be pillars, perceived the grace that was given to me, they gave to me and Barnabas the right hands of fellowship; that we [should go] to the heathen, and they to the circumcision.
10 Abin da dai suka roƙa shi ne ya kamata mu riƙa tuna da matalauta, abin nan da nake marmarin yi.
Only [they would] that we should remember the poor; the same which I also was forward to do.
11 Sa’ad da Bitrus ya zo Antiyok, na tsawata masa ido da ido don laifinsa a fili yake.
But when Peter had come to Antioch, I withstood him to the face, because he was to be blamed.
12 Kafin waɗansu mutane su zo daga wurin Yaƙub, yakan ci abinci tare da Al’ummai. Amma da suka iso, sai ya fara janyewa, ya kuma ware kansa daga wajen Al’ummai domin yana tsoron waɗanda suke ƙungiyar masu kaciya.
For before that certain came from James, he used to eat with the Gentiles: but when they had come, he withdrew, and separated himself, fearing them who were of the circumcision.
13 Sauran Yahudawa suka haɗa kai da shi a munafuncinsa har Barnabas ma ya bauɗe.
And the other Jews dissembled likewise with him; so that Barnabas also was carried away with their dissimulation.
14 Da na ga cewa ba sa yin daidai da gaskiyar bishara, sai na ce wa Bitrus a gabansu duka, “Kai mutumin Yahuda ne, duk da haka kana rayuwa kamar Ba’al’umme ba kamar mutumin Yahuda ba. To, yaya aka yi, kana tilasta Al’ummai su bi al’adun Yahudawa?
But when I saw that they walked not uprightly according to the truth of the gospel, I said to Peter before [them] all, If thou, being a Jew, livest after the manner of Gentiles, and not as do the Jews, why compellest thou the Gentiles to live as do the Jews?
15 “Mu da muke Yahudawa ta wurin haihuwa ba Al’ummai masu zunubi ba,
We [who are] Jews by nature, and not sinners of the Gentiles,
16 mun san cewa mutum ba ya samun kuɓuta ta wurin kiyaye Doka, sai dai ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu. Saboda haka, mu ma, muka sa bangaskiyarmu cikin Kiristi Yesu don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya cikin Kiristi ba ta wurin kiyaye Doka ba, domin ba wanda zai kuɓuta ta wurin bin Doka.
Knowing that a man is not justified by the works of the law, but by the faith of Jesus Christ, even we have believed in Jesus Christ, that we may be justified by the faith of Christ, and not by the works of the law: for by the works of the law shall no flesh be justified.
17 “In kuwa ya zama muna so mu sami zaman marasa laifi a gaban Allah ta wurin dogara ga Kiristi, sa’an nan an same mu mu kanmu ma masu zunubi ne, ashe, ko wannan zai nuna Kiristi yana ƙarfafa zunubi ke nan? A’a, ko kusa!
But if, while we seek to be justified by Christ, we ourselves also are found sinners, [is] therefore Christ the minister of sin? By no means.
18 In na sāke gina abin da na rushe, na zama mai karyar Doka ke nan.
For if I build again the things which I destroyed, I make myself a transgressor.
19 “Gama ta wurin Doka na mutu ga Doka saboda in rayu ga Allah.
For I through the law am dead to the law, that I may live to God.
20 An gicciye ni tare da Kiristi. Yanzu ba ni ne nake raye ba, Kiristi ne yake raye a cikina. Rayuwar da nake yi a jiki, ina rayuwa ce ta wurin bangaskiya cikin Ɗan Allah, wanda ya ƙaunace ni ya kuma ba da kansa domina.
I am crucified with Christ: nevertheless, I live; yet not I, but Christ liveth in me: and the life which I now live in the flesh, I live by the faith of the Son of God, who loved me, and gave himself for me.
21 Ba na ajiyar alherin Allah a gefe, gama da a ce ana samun adalci ta wurin Doka, ai, da Kiristi ya mutu a banza ke nan!”
I do not frustrate the grace of God: for if righteousness is [attainable] by the law, then Christ hath died in vain.

< Galatiyawa 2 >