< Galatiyawa 1 >
1 Bulus manzo, aikakke ba daga wurin mutum ba, ba kuma ta wurin mutane ba, amma ta wurin Yesu Kiristi da kuma Allah Uba, wanda ya tā da Yesu daga matattu.
O PAULO, he lunaolelo, aole na kanaka mai, aole hoi ma ko kanaka, aka, ma o Iesu Kristo la, a ma ke Akua ka Makua nana ia i hoala'e mai ka make mai;
2 Dukan’yan’uwan kuma da suke tare da ni a nan, Suna gai da ikkilisiyoyi a Galatiya.
O ka poe hoahanau no hoi me au, na na ekalesia o Galatia:
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
E alohaia oukou, e maluhia hoi i ke Akua ka Makua, a i ko kakou Haku ia Iesu Kristo,
4 Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, (aiōn )
Nana i haawi mai ia ia iho no ko kakou hala, i hoopakele ae oia ia kakou i keia ao ino nei, e like me ka makemake o ke Akua, ko kakou Makua; (aiōn )
5 a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
Oia ka hoonani mau loa ia'ku Amene. (aiōn )
6 Ina mamaki yadda kuka yi saurin yashe wanda ya kira ku ta wurin alherin Kiristi, kuna juyewa ga wata bishara dabam
Ua kahaha iho no wau i ka emoole o ko oukou haalele ana mai i ka mea i kono aku ia oukou iloko o ka euanelio a Kristo, a lilo i ka euanelio okoa:
7 wadda a gaskiya ba bishara ba ce ko kaɗan. Tabbatacce waɗansu mutane suna birkitar da ku, suna kuma ƙoƙari su karkatar da bisharar Kiristi.
Aole hoi ho euanelio okoa ia; aka, ke hoohihia nei kekahi poe ia oukou, me ka mauao e hookahuli i ka euanelio a Kristo.
8 Amma ko mu, ko mala’ika daga sama ya yi wa’azin wata bishara dabam da wadda muka yi muku, bari yă zama la’ananne har abada!
Ina paha o makou, a he anela paha mai ka lani mai, e hai aku i ka euanelio i ku e i ka makou i hai aku ai ia oukou, e hoomainoinoia oia.
9 Kamar yadda muka riga muka faɗa, haka yanzu ma ina ƙara cewa in wani yana muku wa’azin wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, bari yă zama la’ananne har abada!
Me ka makou i olelo ai mamua, pela hoi au e olelo hou aku nei, a i hai aku kekahi ia oukou i ka olelo ku e i ka mea a oukou i loaa'i, e hoomainoinoia oia.
10 Za a ce, ina ƙoƙarin neman amincewar mutane ne, ko amincewa ta Allah? Ko kuwa ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne? Da a ce har yanzu ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne, ai, da ban zama bawan Kiristi ba.
Ke hoolaulea nei anei au i kanaka, a i ke Akua anei? Ke imi nei anei hoi au e hoolealea i kanaka? no ka mea, a i hoolealea aku au i kanaka, aole au he kauwa na Kristo.
11 Ina so ku sani’yan’uwa, cewa bisharar da nake wa’azi, ba mutum ne ya ƙago ta ba.
Ke hoike aku nei au ia oukou, e na hoahanau, o ka euanelio a'u i hai aku ai, aole ia ma ka ke kanaka.
12 Ban karɓe ta daga wurin wani mutum ba, ba a kuma koya mini ita ba, a maimako, na karɓe ta, ta wurin wahayi daga Yesu Kiristi ne.
No ka mea, aole i loaa ia'u ia na ke kanaka mai, aole hoi au i aoia mai, aka, ma ka hoikeia mai no e Iesu Kristo.
13 Kun dai ji labarin rayuwata ta dā a cikin Yahudanci, yadda na tsananta wa ikkilisiyar Allah ƙwarai, na kuma yi ƙoƙarin hallaka ta.
Ua lohe oukou i kuu noho ana mamua ma ko ka Iudaio manao, he nui loa kuu hoomaau ana'ku i ka ekalesia o ke Akua, me ka luku aku.
14 Na ci gaba a cikin Yahudanci fiye da yawancin Yahudawan da suke tsarana, na kuma yi ƙwazo ƙwarai ga bin al’adun kakannina.
Ua oi aku au ma ko ka Iudaio manao, mamua o ka nui o ka poe hoahanauna o'u, a he nui loa ko'u ikaika ma na mooolelo a o'u mau kupuna.
15 Amma sa’ad da Allah, wanda ya keɓe ni daga mahaifa ya kira ni ta wurin alherinsa, ya kuma gamshe shi
I ka manawa i manao ai ke Akua nana au i hookaawale ae mai ka opu mai o ko'u makuwahine, a koho mai la ia'u ma kona lokomaikai,
16 yă bayyana Ɗansa a cikina, domin in yi wa’azinsa cikin Al’ummai. Ban nemi shawarar wani mutum ba.
E hoike mai i kana Keiki ia'u, i hai aku ai au ia ia i na kanaka e; wikiwiki iho la au, aole au i kuka me ka mea io a me ka mea koko;
17 Ban kuma tafi Urushalima domin in ga waɗanda suka riga ni zaman manzanni ba, sai dai na hanzarta na tafi ƙasar Arabiya, daga baya sai na koma Damaskus.
Aole hoi au i pii aku i Ierusalema, i ka poe lunaolelo mamua o'u: aka, hele aku la au i Arabia, a hoi hou mai la i Damaseko.
18 Bayan shekara uku, sai na haura zuwa Urushalima domin in sadu da Bitrus, na kuwa zauna tare da shi kwana goma sha biyar.
A hala na makahiki ekolu, pii aku la au i Ierusalema e ike ia Petero a noho pu iho la au me ia i na la he umikumamalima.
19 Ban ga wani a ciki sauran manzanni ba, sai dai Yaƙub ɗan’uwan Ubangiji.
O Iakobo hoi ka hoahanau o ka Haku ka'u i ike, aole ka lunaolelo e ae.
20 Ina tabbatar muku a gaban Allah cewa abin da nake rubuta muku ba ƙarya ba ne.
Aia hoi, imua o ke Akua, aole o'u hoopunipuni i na mea a'u e palapala aku nei ia oukou.
21 Daga baya sai na tafi Suriya da Silisiya.
Ma ia hope mai, hele aku la au i na moku o Suria a me Kilikia;
22 Ikkilisiyoyin da suke cikin Kiristi da suke a Yahudiya ba su san ni ba tukuna.
A ua ike maka ole ia au e na ekalesia o Kristo ma Iudea.
23 Sun dai sami labari ne kawai cewa, “Mutumin da dā yake tsananta mana yanzu yana wa’azin bangaskiyar da dā ya yi ƙoƙari yă hallaka.”
He lohe wale no ko lakou, O ka mea nana kakou i hoomaau mai mamua, i neia manawa ke hai aku la ia i ka manao oiaio ana i hoino ai mamua.
24 Sai suka yabi Allah saboda ni.
A hoonani aku la lakou i ke Akua no'u.