< Galatiyawa 1 >
1 Bulus manzo, aikakke ba daga wurin mutum ba, ba kuma ta wurin mutane ba, amma ta wurin Yesu Kiristi da kuma Allah Uba, wanda ya tā da Yesu daga matattu.
Paul an apostle (not from men, nor by man, but by Jesus Christ, and God the Father, who raised Him from the dead),
2 Dukan’yan’uwan kuma da suke tare da ni a nan, Suna gai da ikkilisiyoyi a Galatiya.
and all the brethren that are with me, to the churches of Galatia:
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
grace be to you and peace from God the Father, and from our Lord Jesus Christ,
4 Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, (aiōn )
who gave himself for our sins, that He might deliver us from the present evil world, according to the will of our God and Father: (aiōn )
5 a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
to whom be glory for ever and ever. Amen. (aiōn )
6 Ina mamaki yadda kuka yi saurin yashe wanda ya kira ku ta wurin alherin Kiristi, kuna juyewa ga wata bishara dabam
I wonder that ye are so soon removed from him who called you by the grace of Christ to another gospel: which is not another;
7 wadda a gaskiya ba bishara ba ce ko kaɗan. Tabbatacce waɗansu mutane suna birkitar da ku, suna kuma ƙoƙari su karkatar da bisharar Kiristi.
but there be some that disturb you, and would subvert the gospel of Christ.
8 Amma ko mu, ko mala’ika daga sama ya yi wa’azin wata bishara dabam da wadda muka yi muku, bari yă zama la’ananne har abada!
But tho' we or an angel from heaven should preach to you any other gospel than what we have preached to you; let him be accursed.
9 Kamar yadda muka riga muka faɗa, haka yanzu ma ina ƙara cewa in wani yana muku wa’azin wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, bari yă zama la’ananne har abada!
I say it again, if any one preach to you any other gospel than what ye have received, let him be accursed.
10 Za a ce, ina ƙoƙarin neman amincewar mutane ne, ko amincewa ta Allah? Ko kuwa ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne? Da a ce har yanzu ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne, ai, da ban zama bawan Kiristi ba.
For do I now persuade you to obey men or God? Or do I seek to please men? if I yet pleased men, I should not be the servant of Christ.
11 Ina so ku sani’yan’uwa, cewa bisharar da nake wa’azi, ba mutum ne ya ƙago ta ba.
But I assure you, brethren, that the gospel preached by me is not of human invention.
12 Ban karɓe ta daga wurin wani mutum ba, ba a kuma koya mini ita ba, a maimako, na karɓe ta, ta wurin wahayi daga Yesu Kiristi ne.
For I neither received it, nor was taught it by man, but by the revelation of Jesus Christ.
13 Kun dai ji labarin rayuwata ta dā a cikin Yahudanci, yadda na tsananta wa ikkilisiyar Allah ƙwarai, na kuma yi ƙoƙarin hallaka ta.
For ye have heard of my conversation formerly in Judaism, that I outragiously persecuted the church of God, and laid it waste:
14 Na ci gaba a cikin Yahudanci fiye da yawancin Yahudawan da suke tsarana, na kuma yi ƙwazo ƙwarai ga bin al’adun kakannina.
and I made a proficiency in Judaism above many of the same age with me in my own nation, being excessively zealous for the traditions of my fathers.
15 Amma sa’ad da Allah, wanda ya keɓe ni daga mahaifa ya kira ni ta wurin alherinsa, ya kuma gamshe shi
But when it pleased God, (who separated me from my mother's womb, and called me by his grace, )
16 yă bayyana Ɗansa a cikina, domin in yi wa’azinsa cikin Al’ummai. Ban nemi shawarar wani mutum ba.
to reveal his Son in me, that I might preach Him among the gentiles; immediately I conferred not with flesh and blood,
17 Ban kuma tafi Urushalima domin in ga waɗanda suka riga ni zaman manzanni ba, sai dai na hanzarta na tafi ƙasar Arabiya, daga baya sai na koma Damaskus.
nor went I up to Jerusalem to those that were apostles before me, but I departed into Arabia, and afterwards returned again to Damascus.
18 Bayan shekara uku, sai na haura zuwa Urushalima domin in sadu da Bitrus, na kuwa zauna tare da shi kwana goma sha biyar.
Then after three years I went up to Jerusalem to visit Peter, and I staid with him fifteen days.
19 Ban ga wani a ciki sauran manzanni ba, sai dai Yaƙub ɗan’uwan Ubangiji.
But I saw no other of the apostles, except James the brother of our Lord.
20 Ina tabbatar muku a gaban Allah cewa abin da nake rubuta muku ba ƙarya ba ne.
(Now in what I write to you, behold, before God, I do not lie.)
21 Daga baya sai na tafi Suriya da Silisiya.
Afterwards I came into the regions of Syria and Cilicia,
22 Ikkilisiyoyin da suke cikin Kiristi da suke a Yahudiya ba su san ni ba tukuna.
and was not known in person to the churches of Judea, which were in Christ.
23 Sun dai sami labari ne kawai cewa, “Mutumin da dā yake tsananta mana yanzu yana wa’azin bangaskiyar da dā ya yi ƙoƙari yă hallaka.”
But only they had heard that he who persecuted us before, now preacheth the faith which he formerly would have destroyed.
24 Sai suka yabi Allah saboda ni.
And they glorified God on my account.