< Galatiyawa 1 >
1 Bulus manzo, aikakke ba daga wurin mutum ba, ba kuma ta wurin mutane ba, amma ta wurin Yesu Kiristi da kuma Allah Uba, wanda ya tā da Yesu daga matattu.
Paul, an apostle—appointed not by men nor through man, but by Jesus Christ and God the Father, who raised him from the dead—
2 Dukan’yan’uwan kuma da suke tare da ni a nan, Suna gai da ikkilisiyoyi a Galatiya.
and all the brothers with me, to the churches of Galatia:
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grace to you and peace from God the Father and our Lord Jesus Christ,
4 Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, (aiōn )
who gave himself for our sins to deliver us from the present evil age, according to the will of our God and Father. (aiōn )
5 a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
To him be the glory forever and ever. Amen. (aiōn )
6 Ina mamaki yadda kuka yi saurin yashe wanda ya kira ku ta wurin alherin Kiristi, kuna juyewa ga wata bishara dabam
I am astonished that you are so quickly turning away from him who called you by the grace of Christ and turning to a different gospel,
7 wadda a gaskiya ba bishara ba ce ko kaɗan. Tabbatacce waɗansu mutane suna birkitar da ku, suna kuma ƙoƙari su karkatar da bisharar Kiristi.
not that there is another gospel, but there are some who are troubling you and wish to pervert the gospel of Christ.
8 Amma ko mu, ko mala’ika daga sama ya yi wa’azin wata bishara dabam da wadda muka yi muku, bari yă zama la’ananne har abada!
But even if we or an angel from heaven should preach to you a gospel contrary to the one we preached to you, let him be accursed!
9 Kamar yadda muka riga muka faɗa, haka yanzu ma ina ƙara cewa in wani yana muku wa’azin wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, bari yă zama la’ananne har abada!
As we have said before, so now I say again: If anyone preaches to you a gospel contrary to what you received, let him be accursed!
10 Za a ce, ina ƙoƙarin neman amincewar mutane ne, ko amincewa ta Allah? Ko kuwa ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne? Da a ce har yanzu ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne, ai, da ban zama bawan Kiristi ba.
Am I now seeking the approval of men, or of God? Or am I trying to please men? If I were still trying to please men, I would not be a servant of Christ.
11 Ina so ku sani’yan’uwa, cewa bisharar da nake wa’azi, ba mutum ne ya ƙago ta ba.
But I make known to you, brothers, that the gospel I preached did not originate with man.
12 Ban karɓe ta daga wurin wani mutum ba, ba a kuma koya mini ita ba, a maimako, na karɓe ta, ta wurin wahayi daga Yesu Kiristi ne.
For I did not receive it from man, nor was I taught it, but I received it by a revelation of Jesus Christ.
13 Kun dai ji labarin rayuwata ta dā a cikin Yahudanci, yadda na tsananta wa ikkilisiyar Allah ƙwarai, na kuma yi ƙoƙarin hallaka ta.
For you have heard of my former way of life in Judaism, how I persecuted the church of God beyond measure and tried to destroy it.
14 Na ci gaba a cikin Yahudanci fiye da yawancin Yahudawan da suke tsarana, na kuma yi ƙwazo ƙwarai ga bin al’adun kakannina.
I was advancing in Judaism beyond many of my own age among my people, being far more zealous for the traditions of my fathers.
15 Amma sa’ad da Allah, wanda ya keɓe ni daga mahaifa ya kira ni ta wurin alherinsa, ya kuma gamshe shi
But when God, who set me apart before I was born and called me by his grace, was pleased
16 yă bayyana Ɗansa a cikina, domin in yi wa’azinsa cikin Al’ummai. Ban nemi shawarar wani mutum ba.
to reveal his Son in me so that I could preach good news about him among the Gentiles, I did not immediately confer with flesh and blood,
17 Ban kuma tafi Urushalima domin in ga waɗanda suka riga ni zaman manzanni ba, sai dai na hanzarta na tafi ƙasar Arabiya, daga baya sai na koma Damaskus.
nor did I go up to Jerusalem to those who were apostles before me, but I went away to Arabia and returned again to Damascus.
18 Bayan shekara uku, sai na haura zuwa Urushalima domin in sadu da Bitrus, na kuwa zauna tare da shi kwana goma sha biyar.
Then after three years I went up to Jerusalem to become acquainted with Peter, and I stayed with him for fifteen days.
19 Ban ga wani a ciki sauran manzanni ba, sai dai Yaƙub ɗan’uwan Ubangiji.
But I saw none of the other apostles except James, the brother of the Lord.
20 Ina tabbatar muku a gaban Allah cewa abin da nake rubuta muku ba ƙarya ba ne.
(Now in what I am writing to you, I assure you before God that I am not lying.)
21 Daga baya sai na tafi Suriya da Silisiya.
Then I went into the regions of Syria and Cilicia.
22 Ikkilisiyoyin da suke cikin Kiristi da suke a Yahudiya ba su san ni ba tukuna.
But I was personally unknown to the churches of Judea that are in Christ.
23 Sun dai sami labari ne kawai cewa, “Mutumin da dā yake tsananta mana yanzu yana wa’azin bangaskiyar da dā ya yi ƙoƙari yă hallaka.”
They were only hearing people say, “The man who once persecuted us is now preaching the good news of the faith he once tried to destroy.”
24 Sai suka yabi Allah saboda ni.
So they were glorifying God because of me.