< Galatiyawa 1 >
1 Bulus manzo, aikakke ba daga wurin mutum ba, ba kuma ta wurin mutane ba, amma ta wurin Yesu Kiristi da kuma Allah Uba, wanda ya tā da Yesu daga matattu.
Paul, an apostle, —not from men, nor through man, but through Jesus Christ, and God the Father who raised him from among the dead,
2 Dukan’yan’uwan kuma da suke tare da ni a nan, Suna gai da ikkilisiyoyi a Galatiya.
And all the brethren with me; —unto the assemblies of Galatia:
3 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Favour unto you and peace, from God our Father, and Lord Jesus Christ, —
4 Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, (aiōn )
Who gave himself for our sins, that he might deliver us out of the present evil age, according to the will of our God and Father, — (aiōn )
5 a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
Unto whom be the glory unto the ages of ages: Amen! (aiōn )
6 Ina mamaki yadda kuka yi saurin yashe wanda ya kira ku ta wurin alherin Kiristi, kuna juyewa ga wata bishara dabam
I marvel that, thus quickly, ye are moving away from him that called you in the favour of Christ, unto a different glad-message, —
7 wadda a gaskiya ba bishara ba ce ko kaɗan. Tabbatacce waɗansu mutane suna birkitar da ku, suna kuma ƙoƙari su karkatar da bisharar Kiristi.
Which is not, another, only there are, some, that are troubling you, and wishing to change the glad-message of the Christ.
8 Amma ko mu, ko mala’ika daga sama ya yi wa’azin wata bishara dabam da wadda muka yi muku, bari yă zama la’ananne har abada!
But, even if, we, or, a messenger out of heaven, announce a glad-message [unto you] aside from that which we announced unto you, accursed, let him be!
9 Kamar yadda muka riga muka faɗa, haka yanzu ma ina ƙara cewa in wani yana muku wa’azin wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, bari yă zama la’ananne har abada!
As we have said before, even now, again, I say: If anyone is announcing unto you a glad-message aside from that which ye accepted, accursed, let him be!
10 Za a ce, ina ƙoƙarin neman amincewar mutane ne, ko amincewa ta Allah? Ko kuwa ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne? Da a ce har yanzu ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne, ai, da ban zama bawan Kiristi ba.
For am I, even now, persuading, men, or God? Or am I seeking to please, men? If I had been still pleasing, men, Christ’s servant, had I not been!
11 Ina so ku sani’yan’uwa, cewa bisharar da nake wa’azi, ba mutum ne ya ƙago ta ba.
For I make known unto you, brethren, as to the glad-message which was announced by me, that it is not after man;
12 Ban karɓe ta daga wurin wani mutum ba, ba a kuma koya mini ita ba, a maimako, na karɓe ta, ta wurin wahayi daga Yesu Kiristi ne.
For neither, from man, did I accept it, nor was taught [it], —but through a revealing of Jesus Christ.
13 Kun dai ji labarin rayuwata ta dā a cikin Yahudanci, yadda na tsananta wa ikkilisiyar Allah ƙwarai, na kuma yi ƙoƙarin hallaka ta.
For ye have heard, as to my own manner of life, at one time, in Judaism, how that, exceedingly, was I persecuting the assembly of God, and laying it waste,
14 Na ci gaba a cikin Yahudanci fiye da yawancin Yahudawan da suke tsarana, na kuma yi ƙwazo ƙwarai ga bin al’adun kakannina.
And was making advancement, in Judaism, above many contemporaries in my nation, being, surpassingly zealous, of my paternal instructions.
15 Amma sa’ad da Allah, wanda ya keɓe ni daga mahaifa ya kira ni ta wurin alherinsa, ya kuma gamshe shi
But, when God, who set me apart from my mother’s womb and called me through his favour, was well-pleased
16 yă bayyana Ɗansa a cikina, domin in yi wa’azinsa cikin Al’ummai. Ban nemi shawarar wani mutum ba.
to reveal his Son in me, that I might announce the glad-message regarding him among the nations, straightway, I conferred not with flesh and blood,
17 Ban kuma tafi Urushalima domin in ga waɗanda suka riga ni zaman manzanni ba, sai dai na hanzarta na tafi ƙasar Arabiya, daga baya sai na koma Damaskus.
Neither went I up unto Jerusalem unto them who, before me, were apostles, —but I went away into Arabia, and again returned unto Damascus.
18 Bayan shekara uku, sai na haura zuwa Urushalima domin in sadu da Bitrus, na kuwa zauna tare da shi kwana goma sha biyar.
Then, after three years, went I up unto Jerusalem, to become acquainted with Cephas, and tarried with him fifteen days;
19 Ban ga wani a ciki sauran manzanni ba, sai dai Yaƙub ɗan’uwan Ubangiji.
But, other of the apostles, saw I none, save James the brother of the Lord: —
20 Ina tabbatar muku a gaban Allah cewa abin da nake rubuta muku ba ƙarya ba ne.
Now, as touching the things which I am writing to you, lo! before God, I am not guilty of falsehood: —
21 Daga baya sai na tafi Suriya da Silisiya.
After that, I went into the regions of Syria and Cilicia,
22 Ikkilisiyoyin da suke cikin Kiristi da suke a Yahudiya ba su san ni ba tukuna.
And was still unknown, by face, unto the assemblies of Judaea which were in Christ, —
23 Sun dai sami labari ne kawai cewa, “Mutumin da dā yake tsananta mana yanzu yana wa’azin bangaskiyar da dā ya yi ƙoƙari yă hallaka.”
Only they were hearing—He that was persecuting us formerly, now, is announcing the glad-message of the faith which he formerly laid waste;
24 Sai suka yabi Allah saboda ni.
And they were glorifying, God, in me.