< Ezra 1 >

1 A shekara ta farko ta mulkin sarkin Farisa, wato, sarki Sairus, domin a cika maganar Ubangiji da aka yi ta bakin Irmiya, sai Ubangiji ya taɓa zuciyar Sairus sarkin Farisa ya yi shela a duk fāɗin ƙasarsa, ya kuma rubuta cewa,
Agora, no primeiro ano de Ciro, rei da Pérsia, que a palavra de Javé pela boca de Jeremias poderia ser cumprida, Javé despertou o espírito de Ciro, rei da Pérsia, para que ele fizesse uma proclamação por todo o seu reino, e a colocasse também por escrito, dizendo,
2 “Ga abin da Sairus sarkin Farisa yake shela, “‘Ubangiji Allah na sama ya ba ni iko in yi mulkin duniya duka, ya kuma zaɓe ni in gina masa haikali a Urushalima cikin Yahuda.
“Ciro, rei da Pérsia, diz: 'Javé, o Deus do céu, me deu todos os reinos da terra; e ordenou-me que lhe construísse uma casa em Jerusalém, que está em Judá.
3 Duk wanda yake nasa a cikinku bari Allahnsa yă kasance tare da shi, bari yă tafi Urushalima cikin Yahuda yă gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila, Allah wanda yake a Urushalima.
Quem quer que esteja entre vós de todo seu povo, que seu Deus esteja com ele, e o deixe subir a Jerusalém, que está em Judá, e construir a casa de Javé, o Deus de Israel (ele é Deus), que está em Jerusalém.
4 Duk inda akwai mutumin Yahuda da ya rage, sai mutanen da suke zama kusa da shi, su taimake shi da azurfa, da zinariya, da kaya, da kuma dabbobi, tare da kyautai na yardar rai saboda Gidan Allah wanda yake a Urushalima.’”
Quem ficar, em qualquer lugar onde ele viva, que os homens de seu lugar o ajudem com prata, com ouro, com bens e com animais, além da oferta gratuita pela casa de Deus que está em Jerusalém'”.
5 Sai shugabannin zuriyar Yahuda da na Benyamin, da firistoci da Lawiyawa, duk wanda Allah ya taɓa zuciyarsa, suka shirya don su je su gina haikalin Ubangiji a Urushalima.
Então os chefes de família dos pais de Judá e Benjamim, os sacerdotes e os levitas, todos cujo espírito Deus tinha agitado para subir, levantaram-se para construir a casa de Iavé, que está em Jerusalém.
6 Dukan maƙwabtansu kuwa suka taimake su da gudummawa na kayan azurfa da na zinariya, da kaya, da dabbobi, da kuma kyautai masu daraja bisa bayarwar yardar rai da suka yi.
Todos aqueles que estavam ao seu redor fortaleceram suas mãos com vasos de prata, com ouro, com mercadorias, com animais e com coisas preciosas, além de tudo o que foi oferecido de bom grado.
7 Sai sarki Sairus ya fitar da kayan da suke na haikalin Ubangiji waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga Urushalima ya sa a haikalin allahnsa.
Também o rei Ciro trouxe os vasos da casa de Iavé, que Nabucodonosor tinha trazido de Jerusalém, e tinha colocado na casa de seus deuses;
8 Sairus sarkin Farisa ya sa Mitredat ma’aji ya ƙirga su a gaban Sheshbazzar ɗan sarkin Yahuda.
até mesmo aqueles, Ciro, rei da Pérsia, trazidos pela mão de Mitredath, o tesoureiro, e os contou para Sesbazar, o príncipe de Judá.
9 Ga lissafin kayan. Manyan kwanonin zinariya guda 30 Manyan kwanonin azurfa guda 1,000 Wuƙaƙe guda 29
Este é o número deles: trinta bandejas de ouro, mil bandejas de prata, vinte e nove facas,
10 Waɗansu kwanonin zinariya guda 30 Waɗansu kwanonin azurfa guda 410 da waɗansu kayayyaki guda 1,000
trinta taças de ouro, quatrocentos e dez taças de prata de um segundo tipo, e mil outros recipientes.
11 Dukan kayayyakin zinariya da na azurfa sun kai 5,400. Sheshbazzar ya kawo kayayyakin nan duka tare da shi lokacin da kamammun suka hauro daga Babilon zuwa Urushalima.
Todos os vasos de ouro e de prata eram cinco mil e quatrocentos. Sheshbazzar trouxe todos eles quando os cativos foram trazidos da Babilônia para Jerusalém.

< Ezra 1 >