< Ezra 1 >

1 A shekara ta farko ta mulkin sarkin Farisa, wato, sarki Sairus, domin a cika maganar Ubangiji da aka yi ta bakin Irmiya, sai Ubangiji ya taɓa zuciyar Sairus sarkin Farisa ya yi shela a duk fāɗin ƙasarsa, ya kuma rubuta cewa,
I KA makahiki akahi o Kuro ke alii o Peresia, i hookoia'i ka olelo a Iehova ma ka waha o Ieremia, hoala mai o Iehova i ka naau o Kuro ke alii o Peresia, a kukala aku ia ma kona aupuni a pau, a ma ka palapala hoi, i ka i ana'e,
2 “Ga abin da Sairus sarkin Farisa yake shela, “‘Ubangiji Allah na sama ya ba ni iko in yi mulkin duniya duka, ya kuma zaɓe ni in gina masa haikali a Urushalima cikin Yahuda.
Peneia ka olelo a Kuro ke alii o Peresia, O Iehova ke Akua o ka lani, ua haawi mai ia no'u i na aupuni a pau o ka honua; a ua kauoha mai oia ia'u e hana i hale nona ma Ierusalema i Iuda.
3 Duk wanda yake nasa a cikinku bari Allahnsa yă kasance tare da shi, bari yă tafi Urushalima cikin Yahuda yă gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila, Allah wanda yake a Urushalima.
Owai la ka mea iwaena o oukou no kona poe kanaka a pau? o kona Akua kekahi me ia, a e pii aku ia ma Ierusalema i Iuda, a e hana i ka hale ma Ierusalema no Iehova ke Akua o ka laeraela, oia ke Akua.
4 Duk inda akwai mutumin Yahuda da ya rage, sai mutanen da suke zama kusa da shi, su taimake shi da azurfa, da zinariya, da kaya, da kuma dabbobi, tare da kyautai na yardar rai saboda Gidan Allah wanda yake a Urushalima.’”
A o kela mea keia mea e noho ana ma na wahi a pau ana e noho la, e kokua mai na kanaka o kona wahi ia ia me ke kala, a me ke gula, a me ka waiwai, a me na holoholona, me ka makana no hoi no ka hale o ke Akua ma Ierusalema.
5 Sai shugabannin zuriyar Yahuda da na Benyamin, da firistoci da Lawiyawa, duk wanda Allah ya taɓa zuciyarsa, suka shirya don su je su gina haikalin Ubangiji a Urushalima.
Alaila ku ae la ka poe koikoi o na makua no ka Iuda, a me ka Beniamina, a me na kahuna, a me na Levi, o na mea a pau a ke Akua i hoala mai ai i ko lakou mau naau e pii ae e hana i ka hale no Iehova ma Ierusalema.
6 Dukan maƙwabtansu kuwa suka taimake su da gudummawa na kayan azurfa da na zinariya, da kaya, da dabbobi, da kuma kyautai masu daraja bisa bayarwar yardar rai da suka yi.
A kokua mai no ko lakou poe hoalauna a pau ia lakou me na kiaha kala, a me ke gula, me ka waiwai, a me na holoholona, a me na mea maikai, a he okoa hoi na mea a pau i haawi lokomaikai ia mai.
7 Sai sarki Sairus ya fitar da kayan da suke na haikalin Ubangiji waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga Urushalima ya sa a haikalin allahnsa.
A lawe mai la o Kuro, ke alii, i na kiaha o ka hale o Iehova, na mea a Nebukaneza i lawe ae mai Ierusalema mai, a waiho ia lakou iloko o ka hale o kona mau akua;
8 Sairus sarkin Farisa ya sa Mitredat ma’aji ya ƙirga su a gaban Sheshbazzar ɗan sarkin Yahuda.
Oia mau mea ka Kuro ke alii o Peresia i lawe mai ai iwaho, ma ka lima o Miteredate, ka puukukala, a helu aku la ia mau mea no Sesehazara, ka luna no ka Iuda.
9 Ga lissafin kayan. Manyan kwanonin zinariya guda 30 Manyan kwanonin azurfa guda 1,000 Wuƙaƙe guda 29
A eia ka huina o ia mau mea; he kanakolu ipu gula, a hookahi tausani ipu kala, he iwakaluakumamaiwa pahi,
10 Waɗansu kwanonin zinariya guda 30 Waɗansu kwanonin azurfa guda 410 da waɗansu kayayyaki guda 1,000
He kanakolu bola gula, eha haneri a me ka umi keu na bola kala maikai iki iho, a o na kiaha e ae hookahi tausani.
11 Dukan kayayyakin zinariya da na azurfa sun kai 5,400. Sheshbazzar ya kawo kayayyakin nan duka tare da shi lokacin da kamammun suka hauro daga Babilon zuwa Urushalima.
O na mea gula a pau, a me ke kala, elima tausani a me na haneri eha. O keia mau mea a pau ka Sesehazara i lawe aku ai i ka pii ana o ka poe pio mai Babulona aku a Ierusalema.

< Ezra 1 >