< Ezra 9 >

1 Bayan an yi waɗannan abubuwa duka, sai shugabanni suka zo wurina suka ce, “Mutanen Isra’ila, har da firistoci da Lawiyawa ba su keɓe kansu daga maƙwabtansu ba, ba su kuma keɓe kansu daga irin rayuwar ƙazantar mutanen ƙasar ba, wato, rayuwar irinta Kan’aniyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Yebusiyawa, da Ammonawa, da Mowabawa, da Masarawa da Amoriyawa.
Or sitôt que ces choses-là furent achevées, les principaux du peuple s'approchèrent vers moi, en disant: Le peuple d'Israël, et les Sacrificateurs, et les Lévites ne se sont point séparés des peuples de ces pays, [comme ils le devaient faire] à cause de leurs abominations, [savoir] des Cananéens, des Héthiens, des Phéréziens, des Jébusiens, des Hammonites, des Moabites, des Egyptiens, et des Amorrhéens.
2 Sun auro wa kansu da’ya’yansu’yan mata mutanen nan, ta haka aka kwaɓa zuriyar da aka tsarkake da ta mutanen nan da suke tare da su. Shugabanni da manyan ma’aikata su ne a gaba-gaba a aikata wannan abin kunya.”
Car ils ont pris de leurs filles pour eux et pour leurs fils; et la semence sainte a été mêlée avec les peuples de ces pays; et même il y a des principaux du peuple, et [plusieurs] magistrats, qui ont été les premiers à commettre ce péché.
3 Sa’ad da na ji wannan, sai na yaga rigata da alkyabbata, na tsittsige gashin kaina da na gemuna, na zauna, na rasa abin da yake mini daɗi.
Et sitôt que j'eus entendu cela, je déchirai mes vêtements, et mon manteau, et j'arrachai les cheveux de ma tête, et [les poils] de ma barbe, et je m'assis tout désolé.
4 Sai duk waɗanda suke tsoron maganar Allah na Isra’ila suka kewaye ni don su ji wannan rashin imani wanda waɗanda suka dawo bauta suka yi. Na kuwa zauna a can a rikice, har lokacin miƙa hadaya na yamma.
Et tous ceux qui tremblaient aux paroles du Dieu d'Israël, s'assemblèrent vers moi à cause du crime de ceux de la captivité, et je demeurai assis tout désolé jusqu'à l'oblation du soir.
5 Sa’an nan a lokacin miƙa hadaya na yamma, na tashi da ɓacin raina, da yagaggun kayana, na durƙusa na miƙa hannuwana sama ga Ubangiji Allahna
Et au temps de l'oblation du soir je me levai de mon affliction, et ayant mes vêtements et mon manteau déchirés, je me mis à genoux, et j'étendis mes mains vers l'Eternel mon Dieu,
6 na kuma yi addu’a, na ce, “Ya Allah, ina cike da kunya, ba zan iya ɗaga fuskata gare ka ba, ya Allahna, domin zunubanmu sun fi mu tsayi, tudunsu har ya kai sama.
Et je dis: Mon Dieu! j'ai honte, et je suis trop confus pour [oser] élever, ô mon Dieu! ma face vers toi; car nos iniquités sont multipliées au dessus de nos têtes, et notre crime s'est élevé jusques aux cieux.
7 Tun daga zamanin kakanninmu har zuwa yanzu, zunubanmu suna da yawa. Domin zunubanmu, mu da sarakunanmu, da firistocinmu aka kama mu, aka wulaƙanta mu, muka zama bayi a hannun sarakuna waɗansu ƙasashe.
Depuis les jours de nos pères jusqu'à aujourd'hui nous sommes extrêmement coupables; et nous avons été livrés à cause de nos iniquités, nous, nos Rois, et nos Sacrificateurs, entre les mains des Rois des pays, pour être mis au fil de l'épée, emmenés captifs, pillés, et exposés à l'ignominie, comme il paraît aujourd'hui.
8 “Amma a yanzu a wannan ɗan lokaci Ubangiji Allahnmu ya yi mana jinƙai, ya bar mana saura, ya kuma ba mu wuri a wurinsa mai tsarki, ya kuma ba mu ganin haske, ya ɗan rage mana nauyin bauta.
Mais l'Eternel notre Dieu nous a maintenant fait grâce, comme en un moment, de sorte qu'il a fait que quelques-uns [de nous] sont demeurés de reste, et il nous a donné un clou dans son saint lieu, afin que notre Dieu éclairât nos yeux, et nous donnât quelque petit répit dans notre servitude.
9 Ko da yake mu bayi ne, Allahnmu bai yashe mu cikin daurin talala da muke ciki ba, ya sa sarakunan Farisa suka yi mana kirki. Ya ba mu sabuwar dama don mu sāke gina haikalin Allahnmu, mu kuma gyara katangar, ya kuma ba mu kāriya a Yahuda da Urushalima.
Car nous sommes esclaves, et toutefois notre Dieu ne nous a point abandonnés dans notre servitude; mais il nous a fait trouver grâce devant les Rois de Perse, pour nous donner du répit, afin de relever la maison de notre Dieu, et rétablir ses lieux déserts, et pour nous donner une cloison en Juda, et à Jérusalem.
10 “Amma yanzu, ya Allahnmu, me za mu ce game da wannan? Gama mun ƙi bin
Mais maintenant, ô notre Dieu! que dirons-nous après ces choses? car nous avons abandonné tes commandements,
11 dokokin da ka bayar ta wurin annabawa lokacin da ka ce, ‘Ƙasar da za ku mallaka, ƙasa ce marar tsarki, mutanenta sun ɓata ta da ƙazamin hali, ƙazamin halinsu ya ɓata ko’ina.
Que tu as donnés par tes serviteurs les Prophètes, en disant: Le pays auquel vous allez entrer pour le posséder, est un pays souillé par la souillure des peuples de ces pays-là, à cause des abominations dont ils l'ont rempli, depuis un bout jusqu'à l'autre par leurs impuretés.
12 Saboda haka kada ku aurar musu da’yan matanku, kada kuma ku auro wa’ya’yanku maza’yan matansu. Kada ku yi wata yarjejjeniya ta abokantaka da su. Idan kun yi biyayya za ku yi ƙarfi, ku kuma ci albarkar ƙasar, har ku bar wa’ya’yanku gādo na har abada.’
Maintenant donc, ne donnez point vos filles à leurs fils, et ne prenez point leurs filles pour vos fils, et ne cherchez point leur paix, ni leur bien à jamais; afin que vous soyez affermis, et que vous mangiez les biens du pays, et que vous le fassiez hériter à vos fils pour toujours.
13 “Abubuwan nan sun faru da mu sakamakon mugayen ayyukanmu ne, amma duk da haka ya Allahnmu, ba ka ba mu horo bisa ga yawan zunubanmu ba, ka kuma bar mana saura.
Or après toutes les choses qui nous sont arrivées à cause de nos mauvaises œuvres, et du grand crime qui s'est trouvé en nous; [et] parce, ô notre Dieu! que tu es demeuré [dans tes punitions] au dessous de ce que nos péchés [méritaient], et que tu nous as donné un résidu tel qu'est celui-ci;
14 Za mu sāke ƙin yin biyayya da umarninka mu yi auratayya da mutanen nan da suke aikata waɗannan abubuwan banƙyama? Ba za ka yi fushi da mu, ka ƙone mu da fushinka har babu ɗan saura ba?
Retournerions-nous à enfreindre tes commandements, et à faire alliance avec ces peuples abominables? Ne serais-tu pas irrité contre nous, jusqu'à nous consumer, en sorte qu'il n'y aurait plus aucun résidu, ni aucune ressource?
15 Ya Ubangiji Allah na Isra’ila, kai mai adalci ne! Yau an bar mu da sauran da ya tsira. Ga mu nan a gabanka masu zunubi, gama ba wanda zai iya tsayawa a gabanka.”
Eternel Dieu d'Israël! tu es juste; car nous sommes demeurés de reste, comme il se [voit] aujourd'hui. Voici, nous sommes devant toi avec notre crime; quoiqu'il n'y ait pas moyen de subsister devant toi à cause de ce [que nous avons fait].

< Ezra 9 >