< Ezra 9 >
1 Bayan an yi waɗannan abubuwa duka, sai shugabanni suka zo wurina suka ce, “Mutanen Isra’ila, har da firistoci da Lawiyawa ba su keɓe kansu daga maƙwabtansu ba, ba su kuma keɓe kansu daga irin rayuwar ƙazantar mutanen ƙasar ba, wato, rayuwar irinta Kan’aniyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Yebusiyawa, da Ammonawa, da Mowabawa, da Masarawa da Amoriyawa.
Forsothe after that these thingis weren fillid, the princes neiyeden to me, and seiden, The puple of Israel, and the prestis, and dekenes, ben not depertid fro the `puplis of londis, and fro abhominaciouns of hem, that is, of Cananei, of Ethei, and of Pheresei, and of Jebusei, and of Amonytis, and of Moabitis, and of Egipcians, and of Ammorreis.
2 Sun auro wa kansu da’ya’yansu’yan mata mutanen nan, ta haka aka kwaɓa zuriyar da aka tsarkake da ta mutanen nan da suke tare da su. Shugabanni da manyan ma’aikata su ne a gaba-gaba a aikata wannan abin kunya.”
For thei han take `of her douytris wyues to hem silf, and to her sones, and thei han medlid hooli seed with the puplis of londis; also the hond of princes and of magistratis was the firste in this trespassyng.
3 Sa’ad da na ji wannan, sai na yaga rigata da alkyabbata, na tsittsige gashin kaina da na gemuna, na zauna, na rasa abin da yake mini daɗi.
And whanne Y hadde herd this word, Y torente my mentil and coote, and Y pullide awei the heeris of myn heed and berd, and Y sat morenynge.
4 Sai duk waɗanda suke tsoron maganar Allah na Isra’ila suka kewaye ni don su ji wannan rashin imani wanda waɗanda suka dawo bauta suka yi. Na kuwa zauna a can a rikice, har lokacin miƙa hadaya na yamma.
Forsothe alle that dredden the word of God of Israel camen togidere to me, for the trespassyng of hem that weren comun fro caitifte; and Y sat sori `til to the sacrifice of euentid.
5 Sa’an nan a lokacin miƙa hadaya na yamma, na tashi da ɓacin raina, da yagaggun kayana, na durƙusa na miƙa hannuwana sama ga Ubangiji Allahna
And in the sacrifice of euentid Y roos fro myn afflicioun, and aftir that Y to-rente the mentil and coote, Y bowide my knees, and I spredde abrood myn hondis to `my Lord God,
6 na kuma yi addu’a, na ce, “Ya Allah, ina cike da kunya, ba zan iya ɗaga fuskata gare ka ba, ya Allahna, domin zunubanmu sun fi mu tsayi, tudunsu har ya kai sama.
and Y seide, My God, Y am confoundid and aschamed to reise my face to thee, for oure wickidnessis ben multiplied `on myn heed, and oure trespassis encreessiden `til to heuene,
7 Tun daga zamanin kakanninmu har zuwa yanzu, zunubanmu suna da yawa. Domin zunubanmu, mu da sarakunanmu, da firistocinmu aka kama mu, aka wulaƙanta mu, muka zama bayi a hannun sarakuna waɗansu ƙasashe.
fro the daies of oure fadris; but also we vs silf han synned greuousli `til to this dai, and for our wickidnessis we, and oure kyngis, and oure prestis ben bitakun in the hondis of kyngis of londis, bothe in to swerd, and in to caitifte, in to raueyn, and in to schenship of cheer, as also in this dai.
8 “Amma a yanzu a wannan ɗan lokaci Ubangiji Allahnmu ya yi mana jinƙai, ya bar mana saura, ya kuma ba mu wuri a wurinsa mai tsarki, ya kuma ba mu ganin haske, ya ɗan rage mana nauyin bauta.
And now as at a litil and at a moment oure preier is maad anentis `oure Lord God, that relikis schulden be left to vs, and that `his pees schulde be youun in his hooli place, and that oure God schulde liytne oure iyen, and yyue to vs a litil lijf in oure seruage.
9 Ko da yake mu bayi ne, Allahnmu bai yashe mu cikin daurin talala da muke ciki ba, ya sa sarakunan Farisa suka yi mana kirki. Ya ba mu sabuwar dama don mu sāke gina haikalin Allahnmu, mu kuma gyara katangar, ya kuma ba mu kāriya a Yahuda da Urushalima.
For we ben seruauntis, and oure God forsoke vs not in oure seruage; and he bowide merci on vs bifor the king of Persis, that he schulde yyue lijf to vs, and enhaunse the hows of oure God, and that he schulde bilde the wildernessis therof, and yyue to vs hope in Juda and in Jerusalem.
10 “Amma yanzu, ya Allahnmu, me za mu ce game da wannan? Gama mun ƙi bin
And now, `oure Lord God, what schulen we seie after these thingis? For we han forsake thi comaundementis,
11 dokokin da ka bayar ta wurin annabawa lokacin da ka ce, ‘Ƙasar da za ku mallaka, ƙasa ce marar tsarki, mutanenta sun ɓata ta da ƙazamin hali, ƙazamin halinsu ya ɓata ko’ina.
whiche thou comaundidist in the hond of thi seruauntis profetis, and seidist, The lond, to which ye schulen entre, to holde it in possessioun, is an vnclene lond, bi the vnclennesse of puplis, and of othere londis, in the abhomynaciouns of hem, that filliden it with her defoulyng, fro the mouth `til to the mouth.
12 Saboda haka kada ku aurar musu da’yan matanku, kada kuma ku auro wa’ya’yanku maza’yan matansu. Kada ku yi wata yarjejjeniya ta abokantaka da su. Idan kun yi biyayya za ku yi ƙarfi, ku kuma ci albarkar ƙasar, har ku bar wa’ya’yanku gādo na har abada.’
Now therfor yiue ye not youre douytris to her sones, and take ye not her douytris to youre sones; and seke ye not the pees of hem and the prosperite `of hem `til in to with outen ende; that ye be coumfortid, and ete the goodis, that ben of the lond, and that ye haue eiris, youre sones, `til in to `the world.
13 “Abubuwan nan sun faru da mu sakamakon mugayen ayyukanmu ne, amma duk da haka ya Allahnmu, ba ka ba mu horo bisa ga yawan zunubanmu ba, ka kuma bar mana saura.
And after alle thingis that camen on vs in oure werste werkis, and in oure grete trespas, for thou, oure God, hast delyuered vs fro oure wickidnesse, and hast youe helthe to vs,
14 Za mu sāke ƙin yin biyayya da umarninka mu yi auratayya da mutanen nan da suke aikata waɗannan abubuwan banƙyama? Ba za ka yi fushi da mu, ka ƙone mu da fushinka har babu ɗan saura ba?
as `it is to dai, that we schulden not be turned, and make voide thi comaundementis, and that we schulden not ioyne matrimonyes with the puplis of these abhomynacouns. Whether thou art wrooth to vs `til to the endyng, that thou schuldist not leeue to us remenauntis, and helthe?
15 Ya Ubangiji Allah na Isra’ila, kai mai adalci ne! Yau an bar mu da sauran da ya tsira. Ga mu nan a gabanka masu zunubi, gama ba wanda zai iya tsayawa a gabanka.”
Lord God of Israel, thou art iust; for we ben left, that schulden be sauyd as in this day, lo! we ben bifor thee in oure synne; for me may `not stonde bifor thee on this thing.