< Ezra 9 >
1 Bayan an yi waɗannan abubuwa duka, sai shugabanni suka zo wurina suka ce, “Mutanen Isra’ila, har da firistoci da Lawiyawa ba su keɓe kansu daga maƙwabtansu ba, ba su kuma keɓe kansu daga irin rayuwar ƙazantar mutanen ƙasar ba, wato, rayuwar irinta Kan’aniyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Yebusiyawa, da Ammonawa, da Mowabawa, da Masarawa da Amoriyawa.
Now when these things were accomplished, the princes approached me, saying, The people of Israel, and the priests, and the Levites, have not separated themselves from the nations of the lands, notwithstanding their abominations, from the Canaanites, the Hittites, the Perizzites, the Jebusites, the 'Ammonites, the Moabites, the Egyptians, and the Emorites;
2 Sun auro wa kansu da’ya’yansu’yan mata mutanen nan, ta haka aka kwaɓa zuriyar da aka tsarkake da ta mutanen nan da suke tare da su. Shugabanni da manyan ma’aikata su ne a gaba-gaba a aikata wannan abin kunya.”
For they have taken of their daughters for themselves and for their sons; and the holy seed have mingled themselves with the nations of these lands; and the hand of the princes and rulers hath been the first in this trespass.
3 Sa’ad da na ji wannan, sai na yaga rigata da alkyabbata, na tsittsige gashin kaina da na gemuna, na zauna, na rasa abin da yake mini daɗi.
And when I heard this thing, I rent my garment and my mantle, and I plucked out some of the hair of my head and of my beard, and sat down astounded.
4 Sai duk waɗanda suke tsoron maganar Allah na Isra’ila suka kewaye ni don su ji wannan rashin imani wanda waɗanda suka dawo bauta suka yi. Na kuwa zauna a can a rikice, har lokacin miƙa hadaya na yamma.
And then assembled themselves unto me every one that trembled at the words of the God of Israel, because of the trespass of the exiles; and I sat astounded until the evening sacrifice.
5 Sa’an nan a lokacin miƙa hadaya na yamma, na tashi da ɓacin raina, da yagaggun kayana, na durƙusa na miƙa hannuwana sama ga Ubangiji Allahna
And at the evening sacrifice I rose up from my fasting, and while rending my garment and my mantle, I knelt down upon my knees, and spread out my hands unto the Lord my God.
6 na kuma yi addu’a, na ce, “Ya Allah, ina cike da kunya, ba zan iya ɗaga fuskata gare ka ba, ya Allahna, domin zunubanmu sun fi mu tsayi, tudunsu har ya kai sama.
And I said, O my God, I am ashamed and confounded to lift up my face unto thee, my God! for our iniquities are increased above our head, and our guiltiness is grown up as far as the heavens.
7 Tun daga zamanin kakanninmu har zuwa yanzu, zunubanmu suna da yawa. Domin zunubanmu, mu da sarakunanmu, da firistocinmu aka kama mu, aka wulaƙanta mu, muka zama bayi a hannun sarakuna waɗansu ƙasashe.
From the days of our fathers have we been in a great guiltiness even until this day; and through our iniquities have we been delivered, we, our kings, and our priests, into the hand of the kings of the lands, to the sword, to captivity, and to a spoil, and to the shame of face, as it is this day.
8 “Amma a yanzu a wannan ɗan lokaci Ubangiji Allahnmu ya yi mana jinƙai, ya bar mana saura, ya kuma ba mu wuri a wurinsa mai tsarki, ya kuma ba mu ganin haske, ya ɗan rage mana nauyin bauta.
And now for a little moment hath grace been extended from the Lord our God, to preserve us a remnant to escape, and to give us a stake in his holy place, that our God might enlighten our eyes, and give us a little reviving in our bondage.
9 Ko da yake mu bayi ne, Allahnmu bai yashe mu cikin daurin talala da muke ciki ba, ya sa sarakunan Farisa suka yi mana kirki. Ya ba mu sabuwar dama don mu sāke gina haikalin Allahnmu, mu kuma gyara katangar, ya kuma ba mu kāriya a Yahuda da Urushalima.
For we are bondmen: yet in our bondage hath our God not forsaken us, but hath extended unto us kindness before the kings of Persia, to give us a reviving, to exalt the house of our God, and to erect again its ruins, and to give us a fence in Judah and in Jerusalem.
10 “Amma yanzu, ya Allahnmu, me za mu ce game da wannan? Gama mun ƙi bin
And now what shall we say, O our God, after this? for we have forsaken thy commandments,
11 dokokin da ka bayar ta wurin annabawa lokacin da ka ce, ‘Ƙasar da za ku mallaka, ƙasa ce marar tsarki, mutanenta sun ɓata ta da ƙazamin hali, ƙazamin halinsu ya ɓata ko’ina.
Which thou hast commanded through means of thy servants the prophets, saying, The land, unto which ye go to take possession thereof, is a land defiled through the defilement of the nations of the lands, through their abominations, with which they have filled it from one end to another through their uncleanness.
12 Saboda haka kada ku aurar musu da’yan matanku, kada kuma ku auro wa’ya’yanku maza’yan matansu. Kada ku yi wata yarjejjeniya ta abokantaka da su. Idan kun yi biyayya za ku yi ƙarfi, ku kuma ci albarkar ƙasar, har ku bar wa’ya’yanku gādo na har abada.’
And now your daughters shall ye not give unto their sons, and their daughters shall ye not take for your sons, and ye shall not seek their peace and their welfare unto eternity: in order that ye may be strong, and eat the best of the land, and leave it for an inheritance to your children unto eternity.
13 “Abubuwan nan sun faru da mu sakamakon mugayen ayyukanmu ne, amma duk da haka ya Allahnmu, ba ka ba mu horo bisa ga yawan zunubanmu ba, ka kuma bar mana saura.
And after all that is come over us for our evil deeds, and for our great guiltiness, seeing that thou our God hast spared us [punishing us] less than our iniquities [deserved], and hast given us such deliverance as this:
14 Za mu sāke ƙin yin biyayya da umarninka mu yi auratayya da mutanen nan da suke aikata waɗannan abubuwan banƙyama? Ba za ka yi fushi da mu, ka ƙone mu da fushinka har babu ɗan saura ba?
Should we again make void thy commandments, and make marriage with these people of abominations? wouldst thou not be angry with us even to make an end of us, so that there would not be any remnant or escape?
15 Ya Ubangiji Allah na Isra’ila, kai mai adalci ne! Yau an bar mu da sauran da ya tsira. Ga mu nan a gabanka masu zunubi, gama ba wanda zai iya tsayawa a gabanka.”
O Lord, God of Israel, thou art righteous; for we have been left a remnant that hath escaped, as it is this day; behold, we are before thee in our guiltiness; for there is no standing before thee because of this.