< Ezra 8 >

1 Waɗannan su ne shugabannin iyalai, da kuma waɗanda suka dawo tare da ni daga Babilon a zamanin mulkin Sarki Artazerzes.
Ti so torej vodje njihovih očetov in to je rodovnik tistih, ki so z menoj odšli gor iz Babilona, v kraljevanju kralja Artakserksa.
2 Daga zuriyar Finehas, Gershom ne shugaba; daga zuriyar Itamar, Daniyel ne shugaba; daga zuriyar Dawuda, Hattush
Od Pinhásovih sinov Geršóm. Od Itamárjevih sinov Daniel. Od Davidovih sinov Hatúš.
3 ɗan zuriyar Shekaniya ne shugaba, daga zuriyar Farosh, Zakariya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 150;
Od Šehanjájevih sinov, od Paróševih sinov Zeharjá, in z njim je bilo po rodovniku preštetih sto petdeset moških.
4 daga Fahat-Mowab, Eliyehoyenai ɗan Zerahiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 200;
Od Pahat Moábovih sinov Eljoenáj, Zerahjájev sin in z njim dvesto moških.
5 daga zuriyar Zattu, Shekaniya ɗan Yahaziyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 300;
Od Šehanjájevih sinov Jahaziélov sin in z njim tristo moških.
6 daga zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 50;
Tudi od Adínovih sinov Jonatanov sin Ebed in z njim petdeset moških.
7 daga zuriyar Elam, Yeshahiya ɗan Ataliya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 70;
Od Elámovih sinov Ataljájin sin Ješajá in z njim sedemdeset moških.
8 daga zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mika’ilu ne shugaba, tare da shi akwai mutum 80;
Od Šefatjájevih sinov Mihaelov sin Zebadjá in z njim osemdeset moških.
9 daga iyalin Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 218;
Od Joábovih sinov Jehiélov sin Obadjá in z njim dvesto osemnajst moških.
10 daga Bani, Shelomit ɗan Yosifiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 160;
Od Šelomítovih sinov Josifjájev sin in z njim sto šestdeset moških.
11 daga Bebai, Zakariya ɗan Bebai ne shugaba, tare da shi akwai mutum 28;
Od Bebájevih sinov Bebájev sin Zeharjá in z njim osemindvajset moških.
12 daga iyalin Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 110;
Od Azgádovih sinov Katánov sin Johanán in z njim sto deset moških.
13 zuriya ta Adonikam ne suka zo daga ƙarshe, sunayensu kuwa su ne Elifelet, Yehiyel da Shemahiya, tare da su akwai mutum 60;
Od zadnjih sinov Adonikáma, katerih imena so ta: Elifélet, Jeiél, Šemajá in z njimi šestdeset moških.
14 daga zuriyar Bigwai, Uttai da Zakkur ne shugabanni, tare da su akwai mutum 70.
Tudi od Bigvájevih sinov Utáj in Zabúd in z njima sedemdeset moških.
15 Na kuma tattara su a bakin rafi wanda yake gangarawa zuwa Ahawa, muka kafa sansani a can kwana uku. Da na bincika cikin mutane da firistoci, sai na tarar babu Lawiyawa.
Zbral sem jih skupaj k reki, ki teče proti Ahaváju in tam smo tri dni ostali v šotorih in opazoval sem ljudstvo in duhovnike, pa tam nisem našel nobenega izmed Lévijevih sinov.
16 Saboda haka sai na aika a kira Eliyezer, da Ariyel, da Shemahiya, da Elnatan, da Yarib, da Natan, da Zakariya, da Meshullam waɗanda su ne shugabanni. Na kuma sa a kira Yohiyarib da Elnatan waɗanda masana ne.
Potem sem poslal po Eliézerja, po Ariéla, po Šemajája, po Elnatána, po Jaríba, po Elnatána, po Natána, po Zeharjá in po Mešuláma, vodilne može. Tudi po Jojaríba in po Elnatána, razumna moža.
17 Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.
Poslal sem jih z zapovedjo k Idóju, vodju pri kraju Kasífja in povedal sem jim, kaj naj rečejo Idóju in njegovim bratom Netinimcem na kraju Kasífja, da naj bi k nam privedli služabnike za hišo našega Boga.
18 Da yake Allah yana tare da mu, sai suka aiko mana da Sherebiya, wanda ya iya aiki, shi daga zuriyar Mali ɗan Lawi ne, ɗan Isra’ila. Sai ya zo tare da’ya’yansa da kuma’yan’uwansa. Dukansu dai mutum 18 ne.
Z dobro roko našega Boga nad nami so nam privedli razumnega moža izmed Mahlíjevih sinov, sinú Lévijevega, sinú Izraelovega in Šerebjá z njegovimi sinovi in njegovimi brati, osemnajst;
19 Suka kuma aika da Hashabiya tare da Yeshahiya daga zuriyar Merari, da’yan’uwansu da kuma’ya’yansu, su kuma mutum 20 ne.
in Hašabjá in z njim Ješajá izmed Meraríjevih sinov, njegove brate in njegove sinove, dvajset.
20 Sun kuma kawo masu aiki a haikali mutum 220, ƙungiyar da Dawuda da abokan aikinsa suka keɓe don su taimaki Lawiyawa aiki. Duk aka rubuta waɗannan da sunayensu.
Tudi od Netinimcev, ki so jih David in princi določili za službo Lévijevcem, dvesto in dvajset Netinimcev. Vsi izmed njih so bili določeni po imenu.
21 A can, a bakin rafin Ahawa, na sa mu yi azumi, domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu kuma roƙe shi yă kiyaye mana hanya, da mu da’ya’yanmu da kayanmu duka.
Potem sem tam, pri reki Ahavá, razglasil post, da bi se lahko užalostili pred našim Bogom, da od njega iščemo pravo pot za sebe in za svoje malčke in za vse svoje imetje.
22 Na ji kunya in roƙi sarki yă haɗa mu da sojoji da masu dawakai don su yi mana rakiya su kāre mu daga magabta a kan hanya, gama mun ce wa sarki, “Alherin Allah yana tare da duk wanda yake dogara gare shi, amma kuma fushinsa yana kan duk wanda ya juya masa baya.”
Kajti sram me je bilo, da od kralja zahtevam četo vojakov in konjenikov, da nam pomagajo zoper sovražnika na poti, ker smo kralju govorili, rekoč: »Roka našega Boga je za dobro nad vsemi tistimi, ki ga iščejo, toda njegova moč in njegov bes sta proti vsem tem, ki ga zapustijo.«
23 Saboda haka sai muka yi azumi, muka kai roƙonmu a wurin Allah, ya kuwa amsa mana.
Tako smo se postili in glede tega iskali svojega Boga in on je bil izprošen od nas.
24 Sai na keɓe manyan firistoci guda goma sha biyu tare da Sherebiya, Hashabiya da kuma’yan’uwansu guda goma.
Potem sem ločil dvanajst izmed vodij duhovnikov: Šerebjája, Hašabjája in deset od njihovih bratov z njimi
25 Na auna musu zinariya da azurfa, da kwanoni waɗanda sarki da mashawartansa, da sauran abokan aikinsa, da Isra’ilawan da suke can suka bayar domin haikalin Allahnmu.
in jim odtehtal srebro, zlato in posode, celó daritev hiše našega Boga, ki so jih kralj, njegovi svetovalci, njegovi poveljniki in ves tam prisoten Izrael, darovali.
26 Na auna musu talenti 650 na azurfa, talenti ɗari na kwanonin azurfa, talenti 100 na zinariya,
V njihove roke sem celo odtehtal šeststo petdeset talentov srebra in sto talentov srebrnih posod in sto talentov zlata,
27 kwanonin zinariya guda 20 da darajarsu ya kai darik 1,000, da kwanoni biyu na gogaggen tagulla, wanda yake darajarsa daidai da zinariya.
tudi dvajset umivalnikov iz zlata za tisoč darejkov in dve posodi iz finega bakra, dragoceni kakor zlato.
28 Na ce masa, “Ku da kayan nan tsarkaka ne ga Ubangiji. Azurfa da zinariya ɗin, bayarwa ce ta yardar rai ga Ubangiji, Allah na kakanninku.
Rekel sem jim: »Vi ste sveti Gospodu. Tudi posode so svete in srebro in zlato sta prostovoljno darovana Gospodu, Bogu vaših očetov.
29 Ku lura da su da kyau har sai kun isa Urushalima. Ku auna su a shirayin haikalin Ubangiji a Urushalima, a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai na Isra’ila.”
Pazite in varujte jih, dokler jih ne stehtamo pred vodji duhovnikov in Lévijevcev in vodji Izraelovih očetov v Jeruzalemu, v sobah Gospodove hiše.«
30 Sa’an nan sai firistoci, da Lawiyawa suka karɓi azurfa da zinariya da kuma tsarkakan kwanonin da aka auna don a kai haikalin Allahnmu a Urushalima.
Tako so duhovniki in Lévijevci vzeli težo srebra, zlata in posod, da jih prinesejo v Jeruzalem, v hišo našega Boga.
31 A rana ta goma sha biyu ga watan farko, muka tashi daga bakin rafin Ahawa don mu tafi Urushalima. Alherin Allahnmu yana tare da mu, ya kuma kāre mu daga magabta da’yan fashi.
Potem smo se na dvanajsti dan prvega meseca odpravili od reke Ahavá, da gremo v Jeruzalem in roka našega Boga je bila nad nami in osvobodil nas je iz roke sovražnika in takih, ki ob poti prežijo v zasedi.
32 Muka iso Urushalima, inda muka huta kwana uku.
In prišli smo v Jeruzalem ter tam ostali tri dni.
33 A rana ta huɗu muka tafi haikalin Allah, muka auna azurfa, da zinariya, da tsarkakan kwanonin, muka ba Meremot ɗan Uriya firist, da Eleyazar ɗan Finehas yana tare da shi, da kuma Lawiyawan nan, wato, Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi.
Torej na četrti dan so bile po roki Urijájevega sina Meremóta, duhovnika, srebro, zlato in posode stehtane v hiši našega Boga in z njim je bil Pinhásov sin Eleazar in z njim sta bila Lévijevca Ješúov sin Jozabád in Binújev sin Noádja,
34 Aka yi lissafi aka auna kome aka tarar yana nan daidai, aka kuma rubuta yawan nauyin a lokacin.
po številu in po teži vsake in vsa teža je bila ob tistem času zapisana.
35 Sa’an nan sai waɗanda suka dawo daga bauta suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na Isra’ila. Wato, bijimai guda goma sha biyu don Isra’ilawa duka, raguna tasa’in da shida,’yan raguna saba’in da bakwai, bunsurai kuma guda goma sha biyu. Aka miƙa su hadaya don zunubi. Wannan duka hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji.
Tudi otroci tistih, ki so bili odvedeni proč, ki so prišli iz ujetništva, so darovali žgalne daritve Izraelovemu Bogu: dvanajst bikcev za ves Izrael, šestindevetdeset ovnov, sedeminsedemdeset jagnjet, dvanajst kozlov za daritev za greh. Vse to je bila žgalna daritev Gospodu.
36 Suka kuma kai saƙon sarki zuwa ga wakilansa, da kuma gwamnoni na Kewayen Kogin Yuferites waɗanda suka taimaki mutane da kuma gidan Allah.
Kraljeva naročila so izročili kraljevim poročnikom in voditeljem na tej strani reke in ti so podpirali ljudstvo in Božjo hišo.

< Ezra 8 >