< Ezra 8 >
1 Waɗannan su ne shugabannin iyalai, da kuma waɗanda suka dawo tare da ni daga Babilon a zamanin mulkin Sarki Artazerzes.
И сии князие отечеств их вождеве, иже взыдоша со мною в царство Артаксеркса царя Вавилонска:
2 Daga zuriyar Finehas, Gershom ne shugaba; daga zuriyar Itamar, Daniyel ne shugaba; daga zuriyar Dawuda, Hattush
от сынов Финеесовых Гирсон, от сынов Ифамарих Даниил, от сынов Давидовых Аттус,
3 ɗan zuriyar Shekaniya ne shugaba, daga zuriyar Farosh, Zakariya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 150;
от сынов Саханииных, от сынов Форосовых Захариа, и с ним мужей сто пятьдесят,
4 daga Fahat-Mowab, Eliyehoyenai ɗan Zerahiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 200;
от сынов Фааф-Моава Елиана сын Сараиев, и с ним двести мужей,
5 daga zuriyar Zattu, Shekaniya ɗan Yahaziyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 300;
и от сынов Зафоисовых Ехениа сын Азиилев, и с ним триста мужей,
6 daga zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 50;
и от сынов Адиных Овин сын Ионафанов, и с ним пятьдесят мужей,
7 daga zuriyar Elam, Yeshahiya ɗan Ataliya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 70;
и от сынов Едамлих Исаиа сын Афелиин, и с ним седмьдесят мужей,
8 daga zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mika’ilu ne shugaba, tare da shi akwai mutum 80;
и от сынов Сафатиевых Завдиа сын Михаилов, и с ним осмьдесят мужей,
9 daga iyalin Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 218;
и от сынов Иоавлих Авдиа сын Иеиилев и с ним двести осмьнадесять мужей,
10 daga Bani, Shelomit ɗan Yosifiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 160;
и от сынов Вааниевых Селимуф сын Иосефиев, и с ним сто шестьдесят мужей,
11 daga Bebai, Zakariya ɗan Bebai ne shugaba, tare da shi akwai mutum 28;
и от сынов Вавиевых Захариа сын Вавиев, и с ним двадесять осмь мужей,
12 daga iyalin Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 110;
и от сынов Азгадовых Ионан сын Икатанов, и с ним сто десять мужей,
13 zuriya ta Adonikam ne suka zo daga ƙarshe, sunayensu kuwa su ne Elifelet, Yehiyel da Shemahiya, tare da su akwai mutum 60;
и от сынов Адоникамлих последнии, и сия имена их: Едифалаф, Иеиил и Самаиа, и с ним шестьдесят мужей,
14 daga zuriyar Bigwai, Uttai da Zakkur ne shugabanni, tare da su akwai mutum 70.
и от сынов Вагуаевых Уфай и Завуд, и с ними седмьдесят мужей.
15 Na kuma tattara su a bakin rafi wanda yake gangarawa zuwa Ahawa, muka kafa sansani a can kwana uku. Da na bincika cikin mutane da firistoci, sai na tarar babu Lawiyawa.
Собрах же их к реце текущей ко Евии, и пребыхом ту три дни: исках же в людех и во священницех, и от сынов Левииных не обретох тамо.
16 Saboda haka sai na aika a kira Eliyezer, da Ariyel, da Shemahiya, da Elnatan, da Yarib, da Natan, da Zakariya, da Meshullam waɗanda su ne shugabanni. Na kuma sa a kira Yohiyarib da Elnatan waɗanda masana ne.
И послах ко Елеазару, Ариилу, Семеию и к Маонану, и Иериву и Елнафаму, и Нафану и Захарии и Месолламу, и ко Иоариму и Елнафану, премудрых,
17 Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.
и изведох их ко Адаю началнику на месте Касфиа и вложих во уста их словеса глаголати ко Адаю и братии его афинимом на месте Касфии, привести нам поющих в дом Бога нашего.
18 Da yake Allah yana tare da mu, sai suka aiko mana da Sherebiya, wanda ya iya aiki, shi daga zuriyar Mali ɗan Lawi ne, ɗan Isra’ila. Sai ya zo tare da’ya’yansa da kuma’yan’uwansa. Dukansu dai mutum 18 ne.
И приидоша к нам, понеже рука Бога нашего бе блага на нас, муж сахон от сынов Моолиевых сына Левиина, сына Израилева, и Саравиа, и сынове его и братия его осмьнадесять:
19 Suka kuma aika da Hashabiya tare da Yeshahiya daga zuriyar Merari, da’yan’uwansu da kuma’ya’yansu, su kuma mutum 20 ne.
и Асевиа, и Исаиа от сынов Мерариных и братия его и сынове его двадесять:
20 Sun kuma kawo masu aiki a haikali mutum 220, ƙungiyar da Dawuda da abokan aikinsa suka keɓe don su taimaki Lawiyawa aiki. Duk aka rubuta waɗannan da sunayensu.
и от нафинимов, ихже даде Давид и князие ко службе левитом, нафинимов двести двадесять, вси собрашася по именом.
21 A can, a bakin rafin Ahawa, na sa mu yi azumi, domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu kuma roƙe shi yă kiyaye mana hanya, da mu da’ya’yanmu da kayanmu duka.
И проповедах тамо пост близ реки Ауи, еже смиритися пред Господем Богом нашим, просити от Него пути праваго нам и чадом нашым и всему стяжанию нашему:
22 Na ji kunya in roƙi sarki yă haɗa mu da sojoji da masu dawakai don su yi mana rakiya su kāre mu daga magabta a kan hanya, gama mun ce wa sarki, “Alherin Allah yana tare da duk wanda yake dogara gare shi, amma kuma fushinsa yana kan duk wanda ya juya masa baya.”
устыдехся бо испросити от царя силы и конник защитити нас от врага на пути, понеже рехом царю глаголюще: рука Бога нашего есть на всех ищущих Его во благое и крепость Его, ярость же Его на всех оставляющих Его.
23 Saboda haka sai muka yi azumi, muka kai roƙonmu a wurin Allah, ya kuwa amsa mana.
Постихомся же и молихомся Богу нашему о сем, и услыша нас.
24 Sai na keɓe manyan firistoci guda goma sha biyu tare da Sherebiya, Hashabiya da kuma’yan’uwansu guda goma.
И отлучих от князей священнических дванадесять, Сараию, Асавию и с ними от братии их десять:
25 Na auna musu zinariya da azurfa, da kwanoni waɗanda sarki da mashawartansa, da sauran abokan aikinsa, da Isra’ilawan da suke can suka bayar domin haikalin Allahnmu.
возвеснх же им сребро и злато и сосуды начатков дому Бога нашего, яже вознесе царь и советницы его и князие его, и весь Израиль обретаяйся,
26 Na auna musu talenti 650 na azurfa, talenti ɗari na kwanonin azurfa, talenti 100 na zinariya,
и дах весом в руки их сребра талантов шесть сот пятьдесят, и сосудов сребряных сто, и злата сто талант,
27 kwanonin zinariya guda 20 da darajarsu ya kai darik 1,000, da kwanoni biyu na gogaggen tagulla, wanda yake darajarsa daidai da zinariya.
и чаш златых двадесять, драхм тысящу, и сосуды меди светлыя добрыя различныя, драгоценныя яко злато,
28 Na ce masa, “Ku da kayan nan tsarkaka ne ga Ubangiji. Azurfa da zinariya ɗin, bayarwa ce ta yardar rai ga Ubangiji, Allah na kakanninku.
и рекох им: вы святи Господу Богу, и сосуди святи и сребро и злато, еже волею вдано есть Господу Богу отец наших:
29 Ku lura da su da kyau har sai kun isa Urushalima. Ku auna su a shirayin haikalin Ubangiji a Urushalima, a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai na Isra’ila.”
бдите и стрегите, дондеже весом отдадите пред князи священников и левитов и пред князи отечеств Израилевых во Иерусалиме, во скиниих дому Господня.
30 Sa’an nan sai firistoci, da Lawiyawa suka karɓi azurfa da zinariya da kuma tsarkakan kwanonin da aka auna don a kai haikalin Allahnmu a Urushalima.
И прияша священницы и левити вес сребра и злата и сосудов, да вознесут во Иерусалим в дом Бога нашего.
31 A rana ta goma sha biyu ga watan farko, muka tashi daga bakin rafin Ahawa don mu tafi Urushalima. Alherin Allahnmu yana tare da mu, ya kuma kāre mu daga magabta da’yan fashi.
И воздвигохомся от реки Ауи во вторыйнадесять день месяца перваго, да идем во Иерусалим: и рука Бога нашего бе на нас и избави нас от рук вражиих и ратников на пути,
32 Muka iso Urushalima, inda muka huta kwana uku.
и приидохом во Иерусалим и пребыхом ту три дни.
33 A rana ta huɗu muka tafi haikalin Allah, muka auna azurfa, da zinariya, da tsarkakan kwanonin, muka ba Meremot ɗan Uriya firist, da Eleyazar ɗan Finehas yana tare da shi, da kuma Lawiyawan nan, wato, Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi.
И бысть в день четвертый, отдахом весом сребро и злато и сосуды в дому Бога нашего под руку Маримофа сына Урии священника, и с ним Елеазар сын Финеесов, и с ними Иозавад сын Иисусов и Ноадиа сын Ванаиев левити,
34 Aka yi lissafi aka auna kome aka tarar yana nan daidai, aka kuma rubuta yawan nauyin a lokacin.
по числу и весу вся: и написан бысть весь вес.
35 Sa’an nan sai waɗanda suka dawo daga bauta suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na Isra’ila. Wato, bijimai guda goma sha biyu don Isra’ilawa duka, raguna tasa’in da shida,’yan raguna saba’in da bakwai, bunsurai kuma guda goma sha biyu. Aka miƙa su hadaya don zunubi. Wannan duka hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji.
Во время то, иже приидоша от пленения сынове преселения, принесоша всесожжения Богу Израилеву, телцев дванадесять за всего Израиля, овнов девятьдесят шесть, агнцев седмьдесят седмь, козлов за грехи дванадесять, вся во всесожжение Господу.
36 Suka kuma kai saƙon sarki zuwa ga wakilansa, da kuma gwamnoni na Kewayen Kogin Yuferites waɗanda suka taimaki mutane da kuma gidan Allah.
И даша повеление царево правителем царским и князем, иже за рекою: и прославиша людий и дом Божий.