< Ezra 8 >
1 Waɗannan su ne shugabannin iyalai, da kuma waɗanda suka dawo tare da ni daga Babilon a zamanin mulkin Sarki Artazerzes.
Voici les chefs des pères et l'enregistrement généalogique de ceux qui montèrent avec moi de Babylone, pendant le règne du roi Artaxerxès.
2 Daga zuriyar Finehas, Gershom ne shugaba; daga zuriyar Itamar, Daniyel ne shugaba; daga zuriyar Dawuda, Hattush
Des enfants de Phinées, Guershom; des enfants d'Ithamar, Daniel; des enfants de David, Hattush;
3 ɗan zuriyar Shekaniya ne shugaba, daga zuriyar Farosh, Zakariya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 150;
Des enfants de Shécania, des enfants de Parosh, Zacharie, et avec lui cent cinquante hommes enregistrés;
4 daga Fahat-Mowab, Eliyehoyenai ɗan Zerahiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 200;
Des enfants de Pachath-Moab, Eljoénaï, fils de Zérachia, et avec lui deux cents hommes;
5 daga zuriyar Zattu, Shekaniya ɗan Yahaziyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 300;
Des enfants de Shécania, le fils de Jachaziel, et avec lui trois cents hommes;
6 daga zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 50;
Des enfants d'Adin, Ébed, fils de Jonathan, et avec lui cinquante hommes;
7 daga zuriyar Elam, Yeshahiya ɗan Ataliya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 70;
Des enfants d'Élam, Ésaïe, fils d'Athalia, et avec lui soixante-dix hommes;
8 daga zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mika’ilu ne shugaba, tare da shi akwai mutum 80;
Des enfants de Shéphatia, Zébadia, fils de Micaël, et avec lui quatre-vingts hommes;
9 daga iyalin Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 218;
Des enfants de Joab, Abdias, fils de Jéhiel, et avec lui deux cent dix-huit hommes;
10 daga Bani, Shelomit ɗan Yosifiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 160;
Des enfants de Shélomith, le fils de Josiphia, et avec lui soixante hommes;
11 daga Bebai, Zakariya ɗan Bebai ne shugaba, tare da shi akwai mutum 28;
Des enfants de Bébaï, Zacharie, fils de Bébaï, et avec lui vingt-huit hommes;
12 daga iyalin Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 110;
Des enfants d'Azgad, Jochanan, fils de Haccatan, et avec lui cent dix hommes;
13 zuriya ta Adonikam ne suka zo daga ƙarshe, sunayensu kuwa su ne Elifelet, Yehiyel da Shemahiya, tare da su akwai mutum 60;
Des enfants d'Adonicam, les derniers, dont les noms sont, Éliphélet, Jéhiel et Shémaja, et avec eux soixante hommes;
14 daga zuriyar Bigwai, Uttai da Zakkur ne shugabanni, tare da su akwai mutum 70.
Des enfants de Bigvaï, Uthaï et Zabbud, et avec eux soixante-dix hommes.
15 Na kuma tattara su a bakin rafi wanda yake gangarawa zuwa Ahawa, muka kafa sansani a can kwana uku. Da na bincika cikin mutane da firistoci, sai na tarar babu Lawiyawa.
Je les assemblai près du fleuve qui coule vers Ahava, et nous y campâmes trois jours. Puis je portai mon attention sur le peuple et sur les sacrificateurs, et je n'y trouvai personne des enfants de Lévi.
16 Saboda haka sai na aika a kira Eliyezer, da Ariyel, da Shemahiya, da Elnatan, da Yarib, da Natan, da Zakariya, da Meshullam waɗanda su ne shugabanni. Na kuma sa a kira Yohiyarib da Elnatan waɗanda masana ne.
Alors j'envoyai chercher Éliézer, Ariel, Shémaja, Elnathan, Jarib, Elnathan, Nathan, Zacharie et Méshullam, d'entre les principaux, et Jojarib et Elnathan, docteurs.
17 Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.
Et je leur donnai des ordres pour Iddo, le chef, qui demeurait dans le lieu de Casiphia; et je mis dans leur bouche ce qu'ils devaient dire à Iddo et à son frère, Néthiniens, dans le lieu de Casiphia, afin qu'ils nous fissent venir des gens pour servir dans la maison de notre Dieu.
18 Da yake Allah yana tare da mu, sai suka aiko mana da Sherebiya, wanda ya iya aiki, shi daga zuriyar Mali ɗan Lawi ne, ɗan Isra’ila. Sai ya zo tare da’ya’yansa da kuma’yan’uwansa. Dukansu dai mutum 18 ne.
Et parce que la bonne main de notre Dieu était sur nous, ils nous amenèrent un homme intelligent, d'entre les enfants de Machli, fils de Lévi, fils d'Israël, savoir, Shérébia, et ses fils, et ses frères au nombre de dix-huit;
19 Suka kuma aika da Hashabiya tare da Yeshahiya daga zuriyar Merari, da’yan’uwansu da kuma’ya’yansu, su kuma mutum 20 ne.
Et Hashabia, et avec lui Ésaïe, d'entre les fils de Mérari, ses frères, et leurs fils, au nombre de vingt;
20 Sun kuma kawo masu aiki a haikali mutum 220, ƙungiyar da Dawuda da abokan aikinsa suka keɓe don su taimaki Lawiyawa aiki. Duk aka rubuta waɗannan da sunayensu.
Et des Néthiniens, que David et les principaux du peuple avaient assujettis au service des Lévites, deux cent vingt Néthiniens, tous désignés par leurs noms.
21 A can, a bakin rafin Ahawa, na sa mu yi azumi, domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu kuma roƙe shi yă kiyaye mana hanya, da mu da’ya’yanmu da kayanmu duka.
Là, près du fleuve d'Ahava, je publiai un jeûne, afin de nous humilier devant notre Dieu, en le priant de nous donner un heureux voyage, pour nous et pour nos petits enfants, et pour tous nos biens.
22 Na ji kunya in roƙi sarki yă haɗa mu da sojoji da masu dawakai don su yi mana rakiya su kāre mu daga magabta a kan hanya, gama mun ce wa sarki, “Alherin Allah yana tare da duk wanda yake dogara gare shi, amma kuma fushinsa yana kan duk wanda ya juya masa baya.”
Car j'aurais eu honte de demander au roi des troupes et des cavaliers, pour nous défendre des ennemis par le chemin; car nous avions dit au roi: La main de notre Dieu est favorable à tous ceux qui le cherchent; mais sa force et sa colère sont contre tous ceux qui l'abandonnent.
23 Saboda haka sai muka yi azumi, muka kai roƙonmu a wurin Allah, ya kuwa amsa mana.
Nous jeûnâmes donc, et nous implorâmes le secours de notre Dieu pour cela, et il nous exauça.
24 Sai na keɓe manyan firistoci guda goma sha biyu tare da Sherebiya, Hashabiya da kuma’yan’uwansu guda goma.
Alors je séparai douze des principaux des sacrificateurs, Shérébia, Hashabia, et avec eux dix de leurs frères.
25 Na auna musu zinariya da azurfa, da kwanoni waɗanda sarki da mashawartansa, da sauran abokan aikinsa, da Isra’ilawan da suke can suka bayar domin haikalin Allahnmu.
Et je leur pesai l'argent, l'or et les ustensiles, qui étaient l'offrande que le roi, ses conseillers, ses princes et tous ceux qui s'étaient trouvés d'Israël, avaient faite à la maison de notre Dieu.
26 Na auna musu talenti 650 na azurfa, talenti ɗari na kwanonin azurfa, talenti 100 na zinariya,
Je leur pesai donc et leur délivrai six cent cinquante talents d'argent, et des ustensiles d'argent pour cent talents, cent talents d'or,
27 kwanonin zinariya guda 20 da darajarsu ya kai darik 1,000, da kwanoni biyu na gogaggen tagulla, wanda yake darajarsa daidai da zinariya.
Vingt coupes d'or valant mille dariques, et deux vases d'un bel airain fin, brillant comme l'or, et aussi précieux que l'or.
28 Na ce masa, “Ku da kayan nan tsarkaka ne ga Ubangiji. Azurfa da zinariya ɗin, bayarwa ce ta yardar rai ga Ubangiji, Allah na kakanninku.
Et je leur dis: Vous êtes consacrés à l'Éternel, et ces ustensiles sont consacrés; cet argent aussi et cet or sont une offrande volontaire à l'Éternel, le Dieu de vos pères.
29 Ku lura da su da kyau har sai kun isa Urushalima. Ku auna su a shirayin haikalin Ubangiji a Urushalima, a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai na Isra’ila.”
Veillez, et gardez-les jusqu'à ce que vous les pesiez en la présence des principaux des sacrificateurs et des Lévites, et devant les principaux des pères d'Israël, à Jérusalem, dans les chambres de la maison de l'Éternel.
30 Sa’an nan sai firistoci, da Lawiyawa suka karɓi azurfa da zinariya da kuma tsarkakan kwanonin da aka auna don a kai haikalin Allahnmu a Urushalima.
Les sacrificateurs et les Lévites reçurent donc au poids l'argent, l'or et les ustensiles, pour les porter à Jérusalem dans la maison de notre Dieu.
31 A rana ta goma sha biyu ga watan farko, muka tashi daga bakin rafin Ahawa don mu tafi Urushalima. Alherin Allahnmu yana tare da mu, ya kuma kāre mu daga magabta da’yan fashi.
Nous partîmes du fleuve d'Ahava le douze du premier mois, pour aller à Jérusalem; et la main de notre Dieu fut sur nous, et il nous délivra de la main des ennemis et de leurs embûches sur le chemin.
32 Muka iso Urushalima, inda muka huta kwana uku.
Puis nous arrivâmes à Jérusalem; et nous y étant reposés trois jours,
33 A rana ta huɗu muka tafi haikalin Allah, muka auna azurfa, da zinariya, da tsarkakan kwanonin, muka ba Meremot ɗan Uriya firist, da Eleyazar ɗan Finehas yana tare da shi, da kuma Lawiyawan nan, wato, Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi.
Au quatrième jour nous pesâmes l'argent et l'or et les ustensiles, dans la maison de notre Dieu, et nous les remîmes à Mérémoth, fils d'Urie, le sacrificateur (avec lequel était Éléazar, fils de Phinées; et avec eux Jozabad, fils de Jéshua, et Noadia, fils de Binnuï, Lévites),
34 Aka yi lissafi aka auna kome aka tarar yana nan daidai, aka kuma rubuta yawan nauyin a lokacin.
Selon le nombre et le poids de toutes les choses. Et, en même temps, tout le poids en fut mis par écrit.
35 Sa’an nan sai waɗanda suka dawo daga bauta suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na Isra’ila. Wato, bijimai guda goma sha biyu don Isra’ilawa duka, raguna tasa’in da shida,’yan raguna saba’in da bakwai, bunsurai kuma guda goma sha biyu. Aka miƙa su hadaya don zunubi. Wannan duka hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji.
Les enfants de la déportation, revenus de la captivité, offrirent en holocauste au Dieu d'Israël, douze taureaux pour tout Israël, quatre-vingt-seize béliers, soixante et dix-sept agneaux, et douze boucs pour le péché; le tout en holocauste à l'Éternel.
36 Suka kuma kai saƙon sarki zuwa ga wakilansa, da kuma gwamnoni na Kewayen Kogin Yuferites waɗanda suka taimaki mutane da kuma gidan Allah.
Et ils remirent les ordres du roi aux satrapes du roi, et aux gouverneurs de ce côté-ci du fleuve, qui favorisèrent le peuple et la maison de Dieu.