< Ezra 8 >
1 Waɗannan su ne shugabannin iyalai, da kuma waɗanda suka dawo tare da ni daga Babilon a zamanin mulkin Sarki Artazerzes.
This is a list of the family leaders and genealogical records of those who came back with me from Babylon during the reign of King Artaxerxes:
2 Daga zuriyar Finehas, Gershom ne shugaba; daga zuriyar Itamar, Daniyel ne shugaba; daga zuriyar Dawuda, Hattush
From the sons of Phinehas, Gershom. From the sons of Ithamar, Daniel. From the sons of David, Hattush,
3 ɗan zuriyar Shekaniya ne shugaba, daga zuriyar Farosh, Zakariya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 150;
son of Shecaniah. From the sons of Parosh, Zechariah, and with him 150 men were registered.
4 daga Fahat-Mowab, Eliyehoyenai ɗan Zerahiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 200;
From the sons of Pahath-moab, Eliehoenai, son of Zerahiah, and with him 200 men.
5 daga zuriyar Zattu, Shekaniya ɗan Yahaziyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 300;
From the sons of Zattu, Shecaniah, son of Jahaziel, and with him 300 men.
6 daga zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 50;
From the sons of Adin, Ebed, son of Jonathan, and with him 50 men.
7 daga zuriyar Elam, Yeshahiya ɗan Ataliya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 70;
From the sons of Elam, Jeshaiah, son of Athaliah, and with him 70 men.
8 daga zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mika’ilu ne shugaba, tare da shi akwai mutum 80;
From the sons of Shephatiah, Zebadiah, son of Michael, and with him 80 men.
9 daga iyalin Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 218;
From the sons of Joab, Obadiah, son of Jehiel, and with him 218 men.
10 daga Bani, Shelomit ɗan Yosifiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 160;
From the sons of Bani, Shelomith, son of Josiphiah, and with him 160 men.
11 daga Bebai, Zakariya ɗan Bebai ne shugaba, tare da shi akwai mutum 28;
From the sons of Bebai, Zechariah, son of Bebai, and with him 28 men.
12 daga iyalin Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 110;
From the sons of Azgad, Johanan, son of Hakkatan, and with him 110 men.
13 zuriya ta Adonikam ne suka zo daga ƙarshe, sunayensu kuwa su ne Elifelet, Yehiyel da Shemahiya, tare da su akwai mutum 60;
From the sons of Adonikam, those who were last, their names being Eliphelet, Jeuel, and Shemaiah, and with them 60 men.
14 daga zuriyar Bigwai, Uttai da Zakkur ne shugabanni, tare da su akwai mutum 70.
From the sons of Bigvai, Uthai and Zaccur, and with them 70 men.
15 Na kuma tattara su a bakin rafi wanda yake gangarawa zuwa Ahawa, muka kafa sansani a can kwana uku. Da na bincika cikin mutane da firistoci, sai na tarar babu Lawiyawa.
I gathered the returning exiles together at the Ahava Canal. We camped there for three days while I reviewed who had come—the ordinary people, the priests, and the Levites. I discovered there wasn't a single Levite
16 Saboda haka sai na aika a kira Eliyezer, da Ariyel, da Shemahiya, da Elnatan, da Yarib, da Natan, da Zakariya, da Meshullam waɗanda su ne shugabanni. Na kuma sa a kira Yohiyarib da Elnatan waɗanda masana ne.
so I sent for Eliezer, Ariel, Shemaiah, Elnathan, Jarib, Elnathan, Nathan, Zechariah, and Meshullam, who were leaders, and for Joiarib and Elnathan, who were men with good insight.
17 Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.
I told them to go to Iddo, the leader of the Temple servants at Casiphia, asking him and his relatives to send us ministers for the Temple of our God.
18 Da yake Allah yana tare da mu, sai suka aiko mana da Sherebiya, wanda ya iya aiki, shi daga zuriyar Mali ɗan Lawi ne, ɗan Isra’ila. Sai ya zo tare da’ya’yansa da kuma’yan’uwansa. Dukansu dai mutum 18 ne.
Since our gracious God was with us, they brought us Sherebiah, a man with good insight from the sons of Mahli, son of Levi, son of Israel, together with his sons and brothers, a total of eighteen men;
19 Suka kuma aika da Hashabiya tare da Yeshahiya daga zuriyar Merari, da’yan’uwansu da kuma’ya’yansu, su kuma mutum 20 ne.
and Hashabiah, along with Jeshaiah, from the sons of Merari, and his brothers and their sons, a total of twenty men.
20 Sun kuma kawo masu aiki a haikali mutum 220, ƙungiyar da Dawuda da abokan aikinsa suka keɓe don su taimaki Lawiyawa aiki. Duk aka rubuta waɗannan da sunayensu.
In addition they brought 220 of the Temple servants, a group appointed by David and his officials to help the Levites. These were all registered by name.
21 A can, a bakin rafin Ahawa, na sa mu yi azumi, domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu kuma roƙe shi yă kiyaye mana hanya, da mu da’ya’yanmu da kayanmu duka.
At the Ahava Canal I called for a fast so we could confess our sins before God and ask him for a safe journey for us and our children, along with all our possessions.
22 Na ji kunya in roƙi sarki yă haɗa mu da sojoji da masu dawakai don su yi mana rakiya su kāre mu daga magabta a kan hanya, gama mun ce wa sarki, “Alherin Allah yana tare da duk wanda yake dogara gare shi, amma kuma fushinsa yana kan duk wanda ya juya masa baya.”
I had been reluctant to ask the king to give us a military escort to protect us from enemies on the way. We had told the king, “Our gracious God takes care of everyone who follows him, but shows his anger against anyone who abandons him.”
23 Saboda haka sai muka yi azumi, muka kai roƙonmu a wurin Allah, ya kuwa amsa mana.
So we fasted and asked God to protect us, and he answered our prayers.
24 Sai na keɓe manyan firistoci guda goma sha biyu tare da Sherebiya, Hashabiya da kuma’yan’uwansu guda goma.
Then I designated twelve of the leading priests, and Sherebiah, Hashabiah, and ten of their brothers,
25 Na auna musu zinariya da azurfa, da kwanoni waɗanda sarki da mashawartansa, da sauran abokan aikinsa, da Isra’ilawan da suke can suka bayar domin haikalin Allahnmu.
and I weighed out and handed them the donations of silver and gold, and the items that the king, his counselors, his leaders, and all the people of Israel there had given for the Temple of our God.
26 Na auna musu talenti 650 na azurfa, talenti ɗari na kwanonin azurfa, talenti 100 na zinariya,
I weighed out and placed in their hands 650 talents of silver, silver Temple items weighing 100 talents, 100 talents of gold,
27 kwanonin zinariya guda 20 da darajarsu ya kai darik 1,000, da kwanoni biyu na gogaggen tagulla, wanda yake darajarsa daidai da zinariya.
20 gold bowls worth 1,000 darics, and two articles of highly-polished bronze, as valuable as gold.
28 Na ce masa, “Ku da kayan nan tsarkaka ne ga Ubangiji. Azurfa da zinariya ɗin, bayarwa ce ta yardar rai ga Ubangiji, Allah na kakanninku.
I told them, “You are set apart for the Lord, and these Temple items are too. The silver and gold are a voluntary offering to the Lord, the God of your forefathers.
29 Ku lura da su da kyau har sai kun isa Urushalima. Ku auna su a shirayin haikalin Ubangiji a Urushalima, a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai na Isra’ila.”
You are to guard them and keep them safe until you hand them over, weighing them before the high priests, the Levites and the family leaders in Israel at Jerusalem, in the treasury rooms within the Lord's Temple.”
30 Sa’an nan sai firistoci, da Lawiyawa suka karɓi azurfa da zinariya da kuma tsarkakan kwanonin da aka auna don a kai haikalin Allahnmu a Urushalima.
The priests and Levites took responsibility for the silver and gold and the Temple items that had been weighed out to be brought to the Temple of our God in Jerusalem.
31 A rana ta goma sha biyu ga watan farko, muka tashi daga bakin rafin Ahawa don mu tafi Urushalima. Alherin Allahnmu yana tare da mu, ya kuma kāre mu daga magabta da’yan fashi.
On the twelfth day of the first month, we left the Ahava Canal to go to Jerusalem, and our God was with us to protect us from enemy ambushes along the way.
32 Muka iso Urushalima, inda muka huta kwana uku.
Eventually we arrived in Jerusalem and rested there for three days.
33 A rana ta huɗu muka tafi haikalin Allah, muka auna azurfa, da zinariya, da tsarkakan kwanonin, muka ba Meremot ɗan Uriya firist, da Eleyazar ɗan Finehas yana tare da shi, da kuma Lawiyawan nan, wato, Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi.
On the fourth day the silver and the gold and the Temple items were weighed out in the Temple of our God and handed over to Meremoth, son of Uriah the priest, accompanied by Eleazar, son of Phinehas. Also present were the Levites, Jozabad, son of Jeshua, and Noadiah, son of Binnui.
34 Aka yi lissafi aka auna kome aka tarar yana nan daidai, aka kuma rubuta yawan nauyin a lokacin.
Everything was checked, both by number and weight, and the total weight was written down at the time.
35 Sa’an nan sai waɗanda suka dawo daga bauta suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na Isra’ila. Wato, bijimai guda goma sha biyu don Isra’ilawa duka, raguna tasa’in da shida,’yan raguna saba’in da bakwai, bunsurai kuma guda goma sha biyu. Aka miƙa su hadaya don zunubi. Wannan duka hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji.
Then the exiles who had returned from captivity sacrificed burnt offerings to the God of Israel—twelve bulls for all of Israel, ninety-six rams, seventy-seven lambs, and a sin offering of twelve goats. All were sacrificed as a burnt offering to the Lord.
36 Suka kuma kai saƙon sarki zuwa ga wakilansa, da kuma gwamnoni na Kewayen Kogin Yuferites waɗanda suka taimaki mutane da kuma gidan Allah.
They also delivered the king's decrees to the chief officers of the king and the governors of the province west of the Euphrates, who then provided assistance to the people and to God's Temple.