< Ezra 7 >
1 Bayan waɗannan abubuwa, a zamanin Artazerzes sarkin Farisa, sai Ezra ɗan Serahiya, ɗan Azariya, ɗan Hilkiya,
По сих же словесех, в царство Артаксеркса царя Персскаго, взыде Ездра сын Сареа, сына Азариева, сына Хелкиева,
2 ɗan Shallum, ɗan Zadok, ɗan Ahitub,
сына Селлумля, сына Саддукова, сына Ахитовля,
3 ɗan Amariya, ɗan Azariya, ɗan Merahiyot,
сына Самариева, сына Есриева, сына Мареофова,
4 ɗan Zerahiya, ɗan Uzzi, ɗan Bukki,
сына Зараиева, сына Езеиева, сына Воккиева,
5 ɗan Abishuwa, ɗan Finehas, ɗan Eleyazar, ɗan Haruna babban firist.
сына Ависуева, сына Финеесова, сына Елеазарова, сына Аарона священника перваго:
6 Shi Ezra ɗin ya zo daga Babilon. Shi malami ne ya kuma san Dokar Musa sosai wadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya bayar. Sarki ya ba shi duk abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
сей Ездра взыде от Вавилона и сей писец скор в законе Моисеове, егоже даде Господь Бог Израилю. И даде ему царь, яко рука Господа Бога его на нем бе во всех, яже искаше он.
7 Waɗansu Isra’ilawa, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da masu aiki a haikali su ma suka zo Urushalima a shekara ta bakwai a zamanin mulkin sarki Artazerzes.
И взыдоша от сынов Израилевых и от священников и от левитов, и певцы и придверницы и нафиними во Иерусалим, в лето седмое Артаксеркса царя,
8 Ezra ya iso Urushalima a wata na biyar na shekara ta bakwai na kama mulkin sarkin.
и приидоша во Иерусалим месяца пятаго: сие есть лето седмое царево:
9 Ya fara tafiyarsa daga Babilon a rana ta farko ga watan farko, ya kuma iso Urushalima a rana ta farko ga watan biyar, gama alherin Allahnsa yana tare da shi.
зане в первый день месяца перваго той нача восходити от Вавилона, и в первый день месяца пятаго приидоша во Иерусалим, яко рука Бога его блага на нем бе:
10 Gama Ezra ya miƙa kansa ga bincike da kuma kiyaye Dokar Ubangiji, da kuma koya wa Isra’ilawa dokoki da kuma umarnan Ubangiji.
Ездра бо уготова сердце свое, да взыщет закона (Господня) и да творит и учит во Израили повелением и судбам.
11 Ga wasiƙar da sarki Artazerzes ya ba Ezra wanda yake firist da kuma malami, mutumin da yake cike da sani game da dokoki da kuma umarnan Ubangiji wa Isra’ila.
И сие есть сказание послания еже даде царь Артаксеркс Ездре священнику, писцу книги словес заповедий Господних и повелений Его во Израили:
12 Artazerzes, sarkin sarakuna. Zuwa ga Ezra firist, malamin Dokar Allah na sama. Gaisuwa.
Артаксеркс царь царей Ездре священнику, писцу закона Господа Бога небеснаго: да совершится слово и ответ:
13 Yanzu ina ba da umarni cewa duk wani mutumin Isra’ilan da yake cikin mulkina, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da suke so su tafi tare da kai zuwa Urushalima za su iya tafiya.
от мене повелено есть, да кийждо, иже имать усердие благо во царстве моем от людий Израилевых и от священников и от левитов поити во Иерусалим, с тобою да идет:
14 Sarki ne da mashawartansa guda bakwai suka aike ka don ka je ka ga halin da Yahuda da Urushalima suke ciki game da dokokin Allahnka, waɗanda suke a hannunka.
от лица царева и седми советников его послан еси, да посетиши Иудею и Иерусалим в законе Бога их, сущем в руку твоею,
15 Za ka kuma tafi da zinariya da azurfa waɗanda sarki da mashawartansa suka ba da kyautar yardar rai ga Allah na Isra’ila, wanda haikalinsa ke a Urushalima,
и да отнесеши в дом Господень сребро и злато, еже царь и советницы его со усердием даша Богу Израилеву, Иже во Иерусалиме обитает,
16 haɗe da duk zinariya da azurfan da za ka iya samu a Babilon, da kuma duk bayarwar yardar rai daga mutane da firistoci, domin haikalin Allahnsu da yake a Urushalima.
и все злато и сребро, еже аще обрящеши во всей области Вавилонстей, с добровольным даянием людским и священников, волею приносящих в дом Божий, иже во Иерусалиме:
17 Ka tabbata ka yi amfani da kuɗin nan don ka sayi bijimai, da raguna, da’yan raguna, da hadayu na gari, da na sha, ka kuma miƙa su a kan bagade na haikalin Allahnka a Urushalima.
и всякий доход той усердно впиши в книгу сию: телцы, овны, агнцы, и жертвы их и возлияния их: и принеси та на олтарь дому Бога вашего, иже есть во Иерусалиме:
18 Sa’an nan kai da’yan’uwanka Yahudawa ku yi abin da kuka ga ya fi kyau da sauran zinariya da azurfa ɗin bisa ga nufin Allah.
и аще что тебе и братии твоей благо возмнится от оставшагося сребра и злата сотворити, якоже угодно Богу вашему, сотворите:
19 Ka kai wa Allah na Urushalima duk kayan da aka ba ka amanarsu don yin sujada a haikalin Allahnka.
и сосуды, иже даны тебе в службу дому Божия, вдаждь пред Богом во Иерусалиме:
20 Duk kuma wani abin da ake bukata domin haikalin Allahnka, daga ɗakunan ajiya sarki za ka fitar da kuɗin.
и прочыя потребы дому Бога твоего, еже аще возмнится тебе дати, да даси из домов сокровища царева
21 Yanzu fa ni, Sarki Artazerzes, ina ba da umarni ga kowane ma’aji na Kewayen Kogin Yuferites su tanada duk abin da Ezra firist, wanda kuma yake malamin Dokar Allah na sama zai bukaci,
и от мене аз Артаксеркс царь уставих повеление всем хранителем сокровищ, иже суть за рекою, да все, еже аще воспросит от вас Ездра священник и писец закона Бога небеснаго, готово да будет:
22 har zuwa talenti ɗari na azurfa, da mudu ɗari na alkama, da garwa ɗari na ruwan inabi, da garwa ɗari na man zaitun, da kuma gishiri ba iyaka.
сребра даже до ста талант, и пшеницы даже до ста мер, и вина даже до ста бочек, и елеа даже до ста чванов, а соли без записания:
23 A yi duk abin da Allah na sama ya ce don haikalin Allah na sama, sai a yi shi da himma. Me zai sa a jawo wa sarki da’ya’yansa fushin Allah?
все, еже есть по воли Бога небеснаго, да будет в дому Бога небеснаго: вонмите, да не кто прострет руку на дом Бога небеснаго, да не когда будет гнев на царство царево и сынов его:
24 Ku kuma san cewa, ba ku da ikon sa firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofin haikali, da masu aiki a gidan Allah, ko waɗansu masu aiki a haikali su biya haraji, ko kuɗin shiga.
и вам знаемо творим сие, от всех священников и левитов, певцев, дверников, нафинимов и слуг дому Божия дань да не будет тебе, ниже имейте власти порабощати их:
25 Kai kuma Ezra, bisa ga hikimar da Allah ya ba ka, sai ka zaɓi mahukunta da alƙalai waɗanda za su zama masu yanke hukunci ga dukan mutanen Kewayen Kogin Yuferites, duk waɗanda suka san dokokin Allahnka, ka kuma koya wa duk waɗanda ba su san dokokin ba.
ты же, Ездра, по премудрости Бога твоего, яже в руце твоей, постави книжники и судии, да судят вся люди, иже суть за рекою, всем знающым закон Бога твоего, и не ведающему ведати сотворите:
26 Ba shakka duk wanda bai yi biyayya da dokokin Allahnka ba, da kuma dokokin sarki ba dole a yanke masa hukuncin kisa, ko hukuncin kora, ko hukuncin raba shi da mallakarsa, ko kuma hukuncin kulle shi a kurkuku.
и всяк, иже не сотворит закона Бога твоего и закона царева усердно, суд да будет сотворен на него, аще в смерть, или в наказание, или во отщетение живота, или в темницу.
27 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na kakanninmu, ya taɓa zuciyar sarki don yă kawo ɗaukaka ga haikalin Allah a Urushalima ta wannan hanya.
Благословен Господь Бог отец наших, иже даде сице в сердце царево, да прославит дом Господень, иже во Иерусалиме,
28 Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a gaban sarki da mashawartansa, da kuma duk manyan masu muƙami nasa. Gama Ubangiji Allahna yana tare da ni, sai na sami ƙarfin hali na tattara shugabannin mutane daga Isra’ila, don mu tafi tare.
и на мя уклони милосердие пред очима царя и советников его и всех князей царевых сильных: и аз укреплен бых, яко рука Божия благая на мне, и собрах от Израиля князей взыти со мною.