< Ezra 7 >

1 Bayan waɗannan abubuwa, a zamanin Artazerzes sarkin Farisa, sai Ezra ɗan Serahiya, ɗan Azariya, ɗan Hilkiya,
در زمان سلطنت اردشیر، پادشاه پارس، مردی زندگی می‌کرد به نام عِزرا. عِزرا پسر سرایا بود، سرایا پسر عزریا، عزریا پسر حلقیا،
2 ɗan Shallum, ɗan Zadok, ɗan Ahitub,
حلقیا پسر شلوم، شلوم پسر صادوق، صادوق پسر اخیطوب،
3 ɗan Amariya, ɗan Azariya, ɗan Merahiyot,
اخیطوب پسر امریا، امریا پسر عزریا، عزریا پسر مرایوت،
4 ɗan Zerahiya, ɗan Uzzi, ɗan Bukki,
مرایوت پسر زرحیا، زرحیا پسر عزی، عزی پسر بقی،
5 ɗan Abishuwa, ɗan Finehas, ɗan Eleyazar, ɗan Haruna babban firist.
بقی پسر ابیشوع، ابیشوع پسر فینحاس، فینحاس پسر العازار و العازار پسر هارون کاهن اعظم.
6 Shi Ezra ɗin ya zo daga Babilon. Shi malami ne ya kuma san Dokar Musa sosai wadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya bayar. Sarki ya ba shi duk abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
عِزرا از علمای دین یهود بود و کتاب تورات را که خداوند به‌وسیلۀ موسی به قوم اسرائیل داده بود، خوب می‌دانست. اردشیر پادشاه هر چه عِزرا می‌خواست به وی می‌داد، زیرا خداوند، خدایش با او بود. عِزرا بابِل را ترک گفت
7 Waɗansu Isra’ilawa, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da masu aiki a haikali su ma suka zo Urushalima a shekara ta bakwai a zamanin mulkin sarki Artazerzes.
و همراه عده‌ای از یهودیان و نیز کاهنان، لاویان، نوازندگان، نگهبانان و خدمتگزاران خانهٔ خدا به اورشلیم رفت. ایشان روز اول ماه اول از سال هفتم سلطنت اردشیر از بابِل حرکت کردند و به یاری خدا روز اول ماه پنجم همان سال، به سلامت به اورشلیم رسیدند.
8 Ezra ya iso Urushalima a wata na biyar na shekara ta bakwai na kama mulkin sarkin.
9 Ya fara tafiyarsa daga Babilon a rana ta farko ga watan farko, ya kuma iso Urushalima a rana ta farko ga watan biyar, gama alherin Allahnsa yana tare da shi.
10 Gama Ezra ya miƙa kansa ga bincike da kuma kiyaye Dokar Ubangiji, da kuma koya wa Isra’ilawa dokoki da kuma umarnan Ubangiji.
عِزرا زندگی خود را وقف مطالعهٔ تورات و به کار بستن دستورهای آن و تعلیم احکامش به مردم اسرائیل نموده بود.
11 Ga wasiƙar da sarki Artazerzes ya ba Ezra wanda yake firist da kuma malami, mutumin da yake cike da sani game da dokoki da kuma umarnan Ubangiji wa Isra’ila.
این است متن نامه‌ای که اردشیر پادشاه به عِزرای کاهن و کاتب داد. (عِزرا در امور مربوط به فرمانهای خداوند و فرایض او به اسرائیل شخص صاحب‌نظری بود):
12 Artazerzes, sarkin sarakuna. Zuwa ga Ezra firist, malamin Dokar Allah na sama. Gaisuwa.
از اردشیر پادشاه، به عِزرای کاهن و عالم شریعت خدای آسمان.
13 Yanzu ina ba da umarni cewa duk wani mutumin Isra’ilan da yake cikin mulkina, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da suke so su tafi tare da kai zuwa Urushalima za su iya tafiya.
به این وسیله فرمان می‌دهم که از تمام مردم اسرائیل و کاهنان و لاویانی که در سراسر قلمرو سرزمین من به سر می‌برند، هر که بخواهد می‌تواند همراه تو به اورشلیم بازگردد.
14 Sarki ne da mashawartansa guda bakwai suka aike ka don ka je ka ga halin da Yahuda da Urushalima suke ciki game da dokokin Allahnka, waɗanda suke a hannunka.
تو از طرف من و هفت مشاورم به اورشلیم و یهودا فرستاده می‌شوی تا بر اساس قوانین خدایت وضع مردم آنجا را تحقیق کنی.
15 Za ka kuma tafi da zinariya da azurfa waɗanda sarki da mashawartansa suka ba da kyautar yardar rai ga Allah na Isra’ila, wanda haikalinsa ke a Urushalima,
در ضمن طلا و نقره‌ای را که ما به خدای اسرائیل تقدیم می‌کنیم و طلا و نقره‌ای را که اهالی بابِل می‌دهند، همراه با هدایایی که یهودیان و کاهنان برای خانهٔ خدا تقدیم می‌کنند، با خود به اورشلیم ببر.
16 haɗe da duk zinariya da azurfan da za ka iya samu a Babilon, da kuma duk bayarwar yardar rai daga mutane da firistoci, domin haikalin Allahnsu da yake a Urushalima.
17 Ka tabbata ka yi amfani da kuɗin nan don ka sayi bijimai, da raguna, da’yan raguna, da hadayu na gari, da na sha, ka kuma miƙa su a kan bagade na haikalin Allahnka a Urushalima.
وقتی به آنجا رسیدی قبل از هر چیز با این هدایا، گاوها، قوچها، بره‌ها، و موادی را که برای هدایای آردی و نوشیدنی لازم است خریداری کن و تمام آنها را روی مذبح خانهٔ خدای خود تقدیم نما.
18 Sa’an nan kai da’yan’uwanka Yahudawa ku yi abin da kuka ga ya fi kyau da sauran zinariya da azurfa ɗin bisa ga nufin Allah.
بقیهٔ هدایا را به هر طریقی که تو و برادرانت صلاح می‌دانید و مطابق خواست خدای شماست به کار ببرید.
19 Ka kai wa Allah na Urushalima duk kayan da aka ba ka amanarsu don yin sujada a haikalin Allahnka.
لوازمی را که ما برای خانهٔ خدای شما در اورشلیم می‌دهیم به خدای خود تقدیم کنید.
20 Duk kuma wani abin da ake bukata domin haikalin Allahnka, daga ɗakunan ajiya sarki za ka fitar da kuɗin.
اگر چیز دیگری برای خانهٔ خدا احتیاج داشتید می‌توانید از خزانهٔ سلطنتی دریافت نمایید.
21 Yanzu fa ni, Sarki Artazerzes, ina ba da umarni ga kowane ma’aji na Kewayen Kogin Yuferites su tanada duk abin da Ezra firist, wanda kuma yake malamin Dokar Allah na sama zai bukaci,
من، اردشیر پادشاه، به تمام خزانه‌دارها در مناطق غرب رود فرات دستور می‌دهم که هر چه عِزرا، کاهن و عالم شریعت خدای آسمان، از شما درخواست نماید تا سه هزار و چهارصد کیلوگرم نقره، ده هزار کیلوگرم گندم، دو هزار لیتر شراب، دو هزار لیتر روغن زیتون و هر مقدار نمک که لازم باشد فوری به او بدهید.
22 har zuwa talenti ɗari na azurfa, da mudu ɗari na alkama, da garwa ɗari na ruwan inabi, da garwa ɗari na man zaitun, da kuma gishiri ba iyaka.
23 A yi duk abin da Allah na sama ya ce don haikalin Allah na sama, sai a yi shi da himma. Me zai sa a jawo wa sarki da’ya’yansa fushin Allah?
هر چه خدای آسمان فرموده باشد، بدون تأخیر برای خانهٔ او بجا آورید، مبادا خشم خدا بر من و خاندانم نازل شود.
24 Ku kuma san cewa, ba ku da ikon sa firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofin haikali, da masu aiki a gidan Allah, ko waɗansu masu aiki a haikali su biya haraji, ko kuɗin shiga.
همچنین اعلان می‌کنم که تمام کاهنان، لاویان، نوازندگان، نگهبانان، خدمتگزاران و سایر کارکنان خانهٔ خدا از پرداخت هرگونه مالیات معاف هستند.
25 Kai kuma Ezra, bisa ga hikimar da Allah ya ba ka, sai ka zaɓi mahukunta da alƙalai waɗanda za su zama masu yanke hukunci ga dukan mutanen Kewayen Kogin Yuferites, duk waɗanda suka san dokokin Allahnka, ka kuma koya wa duk waɗanda ba su san dokokin ba.
و تو ای عِزرا، با حکمتی که خدا به تو داده است، حکام و قضاتی را که شریعت خدایت را می‌دانند برای رسیدگی به مسائل مردم غرب رود فرات انتخاب کن. اگر آنها با شریعت خدای تو آشنا نباشند، باید ایشان را تعلیم دهی.
26 Ba shakka duk wanda bai yi biyayya da dokokin Allahnka ba, da kuma dokokin sarki ba dole a yanke masa hukuncin kisa, ko hukuncin kora, ko hukuncin raba shi da mallakarsa, ko kuma hukuncin kulle shi a kurkuku.
اگر کسی نخواهد از شریعت خدای تو و دستور پادشاه اطاعت کند، باید بی‌درنگ مجازات شود؛ مجازات او یا مرگ است یا تبعید، یا ضبط اموال یا زندان.
27 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na kakanninmu, ya taɓa zuciyar sarki don yă kawo ɗaukaka ga haikalin Allah a Urushalima ta wannan hanya.
سپس عِزرا اینطور دعا کرد: «سپاس بر خداوند، خدای اجداد ما که این اشتیاق را در دل پادشاه گذاشت تا خانهٔ خداوند را که در اورشلیم است زینت دهد.
28 Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a gaban sarki da mashawartansa, da kuma duk manyan masu muƙami nasa. Gama Ubangiji Allahna yana tare da ni, sai na sami ƙarfin hali na tattara shugabannin mutane daga Isra’ila, don mu tafi tare.
خداوند، خدایم را شکر می‌کنم که مرا مقبول پادشاه و مشاوران و تمام مقامات مقتدرش گردانید و به من قوت بخشید تا بتوانم سران طایفه‌های اسرائیل را جمع کنم تا با من به اورشلیم بازگردند.»

< Ezra 7 >