< Ezra 7 >

1 Bayan waɗannan abubuwa, a zamanin Artazerzes sarkin Farisa, sai Ezra ɗan Serahiya, ɗan Azariya, ɗan Hilkiya,
Nogen tid efter, under perserkongen Artaxerxes' regjering, drog Esras, sønn av Seraja, sønn av Asarja, sønn av Hilkias,
2 ɗan Shallum, ɗan Zadok, ɗan Ahitub,
sønn av Sallum, sønn av Sadok, sønn av Akitub,
3 ɗan Amariya, ɗan Azariya, ɗan Merahiyot,
sønn av Amarja, sønn av Asarja, sønn av Merajot,
4 ɗan Zerahiya, ɗan Uzzi, ɗan Bukki,
sønn av Serahja, sønn av Ussi, sønn av Bukki,
5 ɗan Abishuwa, ɗan Finehas, ɗan Eleyazar, ɗan Haruna babban firist.
sønn av Abisua, sønn av Pinehas, sønn av Eleasar, sønn av ypperstepresten Aron -
6 Shi Ezra ɗin ya zo daga Babilon. Shi malami ne ya kuma san Dokar Musa sosai wadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya bayar. Sarki ya ba shi duk abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
denne Esras drog op fra Babel. Han var en skriftlærd mann, vel kjent med Mose lov, den som Herren, Israels Gud, hadde gitt. Kongen gav ham alt det han bad om; for Herren hans Gud holdt sin hånd over ham.
7 Waɗansu Isra’ilawa, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da masu aiki a haikali su ma suka zo Urushalima a shekara ta bakwai a zamanin mulkin sarki Artazerzes.
Nogen av Israels barn og av prestene, levittene, sangerne, dørvokterne og tempeltjenerne drog med ham op til Jerusalem i kong Artaxerxes' syvende år.
8 Ezra ya iso Urushalima a wata na biyar na shekara ta bakwai na kama mulkin sarkin.
Han kom til Jerusalem i den femte måned; det var i kongens syvende år.
9 Ya fara tafiyarsa daga Babilon a rana ta farko ga watan farko, ya kuma iso Urushalima a rana ta farko ga watan biyar, gama alherin Allahnsa yana tare da shi.
For på den første dag i den første måned begynte han å ordne alt til ferden fra Babel, og på den første dag i den femte måned kom han til Jerusalem; for hans Gud holdt sin gode hånd over ham.
10 Gama Ezra ya miƙa kansa ga bincike da kuma kiyaye Dokar Ubangiji, da kuma koya wa Isra’ilawa dokoki da kuma umarnan Ubangiji.
For Esras hadde satt sin hu til å granske Herrens lov og gjøre efter den og til å lære folk lov og rett i Israel.
11 Ga wasiƙar da sarki Artazerzes ya ba Ezra wanda yake firist da kuma malami, mutumin da yake cike da sani game da dokoki da kuma umarnan Ubangiji wa Isra’ila.
Dette er en avskrift av det brev som kong Artaxerxes gav presten Esras, den skriftlærde, som var kyndig i de bud og lover som Herren hadde gitt Israel:
12 Artazerzes, sarkin sarakuna. Zuwa ga Ezra firist, malamin Dokar Allah na sama. Gaisuwa.
Artaxerxes, kongenes konge, til presten Esras, han som er full-lært i himmelens Guds lov, og så videre.
13 Yanzu ina ba da umarni cewa duk wani mutumin Isra’ilan da yake cikin mulkina, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da suke so su tafi tare da kai zuwa Urushalima za su iya tafiya.
Jeg har gitt befaling om at alle de av Israels folk og av dets prester og levitter i mitt rike som har lyst til å dra til Jerusalem, kan dra med dig,
14 Sarki ne da mashawartansa guda bakwai suka aike ka don ka je ka ga halin da Yahuda da Urushalima suke ciki game da dokokin Allahnka, waɗanda suke a hannunka.
siden du er sendt av kongen og hans syv rådgivere til å se efter hvorledes det er med Juda og Jerusalem, efter din Guds lov, som du har i hende,
15 Za ka kuma tafi da zinariya da azurfa waɗanda sarki da mashawartansa suka ba da kyautar yardar rai ga Allah na Isra’ila, wanda haikalinsa ke a Urushalima,
og til å føre dit det sølv og gull som kongen og hans rådgivere frivillig har gitt Israels Gud, han som har sin bolig i Jerusalem,
16 haɗe da duk zinariya da azurfan da za ka iya samu a Babilon, da kuma duk bayarwar yardar rai daga mutane da firistoci, domin haikalin Allahnsu da yake a Urushalima.
og likeledes alt det sølv og gull som du kan få i hele Babels landskap, og de frivillige gaver som folket og prestene vil gi til sin Guds hus i Jerusalem.
17 Ka tabbata ka yi amfani da kuɗin nan don ka sayi bijimai, da raguna, da’yan raguna, da hadayu na gari, da na sha, ka kuma miƙa su a kan bagade na haikalin Allahnka a Urushalima.
Derfor skal du for disse penger samvittighetsfullt kjøpe okser, værer og lam med tilhørende matoffere og drikkoffere; og du skal ofre dem på alteret i eders Guds hus i Jerusalem.
18 Sa’an nan kai da’yan’uwanka Yahudawa ku yi abin da kuka ga ya fi kyau da sauran zinariya da azurfa ɗin bisa ga nufin Allah.
Og hvad du og dine brødre finner det riktig å gjøre med resten av sølvet og gullet, det kan I gjøre efter eders Guds vilje.
19 Ka kai wa Allah na Urushalima duk kayan da aka ba ka amanarsu don yin sujada a haikalin Allahnka.
Men de kar som du har fått til tjenesten i din Guds hus, dem skal du gi fra dig for Jerusalems Guds åsyn.
20 Duk kuma wani abin da ake bukata domin haikalin Allahnka, daga ɗakunan ajiya sarki za ka fitar da kuɗin.
Hvad du ellers må utrede til din Guds hus av nødvendige utgifter, det skal du utrede av kongens skattkammer.
21 Yanzu fa ni, Sarki Artazerzes, ina ba da umarni ga kowane ma’aji na Kewayen Kogin Yuferites su tanada duk abin da Ezra firist, wanda kuma yake malamin Dokar Allah na sama zai bukaci,
Og jeg, kong Artaxerxes, har gitt befaling til alle skattmestere hinsides elven at alt hvad presten Esras, han som er kyndig i himmelens Guds lov, krever av eder, det skal nøiaktig ydes,
22 har zuwa talenti ɗari na azurfa, da mudu ɗari na alkama, da garwa ɗari na ruwan inabi, da garwa ɗari na man zaitun, da kuma gishiri ba iyaka.
inntil hundre talenter sølv, hundre kor hvete, hundre bat vin og hundre bat olje, og salt uten foreskrevet mål.
23 A yi duk abin da Allah na sama ya ce don haikalin Allah na sama, sai a yi shi da himma. Me zai sa a jawo wa sarki da’ya’yansa fushin Allah?
Alt hvad himmelens Gud befaler, det skal nøiaktig utføres for himmelens Guds hus, så det ikke skal komme vrede over kongens og hans sønners rike.
24 Ku kuma san cewa, ba ku da ikon sa firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofin haikali, da masu aiki a gidan Allah, ko waɗansu masu aiki a haikali su biya haraji, ko kuɗin shiga.
Og eder lar vi vite at ingen skal ha makt til å pålegge nogen av prestene, levittene, sangerne, dørvokterne, tempeltjenerne eller nogen annen som har en tjeneste ved dette Guds hus, skatt, toll eller veipenger.
25 Kai kuma Ezra, bisa ga hikimar da Allah ya ba ka, sai ka zaɓi mahukunta da alƙalai waɗanda za su zama masu yanke hukunci ga dukan mutanen Kewayen Kogin Yuferites, duk waɗanda suka san dokokin Allahnka, ka kuma koya wa duk waɗanda ba su san dokokin ba.
Og du, Esras, skal efter den visdom du har fått av din Gud, innsette dommere og lovkyndige til å dømme alt folket hinsides elven, alle dem som kjenner din Guds lover; og om nogen ikke kjenner dem, så skal I lære ham å kjenne dem.
26 Ba shakka duk wanda bai yi biyayya da dokokin Allahnka ba, da kuma dokokin sarki ba dole a yanke masa hukuncin kisa, ko hukuncin kora, ko hukuncin raba shi da mallakarsa, ko kuma hukuncin kulle shi a kurkuku.
Og om nogen ikke gjør efter din Guds lov og efter kongens lov, så skal der samvittighetsfullt holdes dom over ham, enten det nu fører til døden eller til landflyktighet eller til bøter eller til bånd og fengsel.
27 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na kakanninmu, ya taɓa zuciyar sarki don yă kawo ɗaukaka ga haikalin Allah a Urushalima ta wannan hanya.
Lovet være Herren, våre fedres Gud, som gav kongen slikt i sinne, så Herrens hus i Jerusalem kunde bli prydet,
28 Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a gaban sarki da mashawartansa, da kuma duk manyan masu muƙami nasa. Gama Ubangiji Allahna yana tare da ni, sai na sami ƙarfin hali na tattara shugabannin mutane daga Isra’ila, don mu tafi tare.
og som lot mig finne nåde hos kongen og hans rådgivere og hos alle kongens mektige høvdinger! Jeg kjente mig sterk, fordi Herren min Gud holdt sin hånd over mig, og jeg fikk samlet nogen av Israels overhoder til å dra op sammen med mig.

< Ezra 7 >