< Ezra 7 >

1 Bayan waɗannan abubuwa, a zamanin Artazerzes sarkin Farisa, sai Ezra ɗan Serahiya, ɗan Azariya, ɗan Hilkiya,
Or après ces choses, [et] durant le règne d'Artaxerxes, Roi de Perse, Esdras fils de Séraja, fils de Hazaria, fils de Hilkija,
2 ɗan Shallum, ɗan Zadok, ɗan Ahitub,
Fils de Sallum, fils de Tsadok, fils d'Ahitub,
3 ɗan Amariya, ɗan Azariya, ɗan Merahiyot,
Fils d'Amaria, fils de Hazaria, fils de Mérajoth,
4 ɗan Zerahiya, ɗan Uzzi, ɗan Bukki,
Fils de Zérahia, fils de Huzi, fils de Bukki,
5 ɗan Abishuwa, ɗan Finehas, ɗan Eleyazar, ɗan Haruna babban firist.
Fils d'Abisuah, fils de Phinées, fils d'Eléazar, fils d'Aaron premier Sacrificateur;
6 Shi Ezra ɗin ya zo daga Babilon. Shi malami ne ya kuma san Dokar Musa sosai wadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya bayar. Sarki ya ba shi duk abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
Esdras, dis-je, qui était un Scribe bien exercé en la Loi de Moïse, que l'Eternel le Dieu d'Israël avait donnée, monta de Babylone, et le Roi lui accorda toute sa requête, selon que la main de l'Eternel son Dieu était sur lui.
7 Waɗansu Isra’ilawa, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da masu aiki a haikali su ma suka zo Urushalima a shekara ta bakwai a zamanin mulkin sarki Artazerzes.
Quelques-uns aussi des enfants d'Israël, des Sacrificateurs, des Lévites, des chantres, des portiers, et des Néthiniens, montèrent à Jérusalem la septième année du Roi Artaxerxes.
8 Ezra ya iso Urushalima a wata na biyar na shekara ta bakwai na kama mulkin sarkin.
Et [Esdras] arriva à Jérusalem le cinquième mois de la septième année du Roi.
9 Ya fara tafiyarsa daga Babilon a rana ta farko ga watan farko, ya kuma iso Urushalima a rana ta farko ga watan biyar, gama alherin Allahnsa yana tare da shi.
Car au premier jour du premier mois, on commença de partir de Babylone; et au premier jour du cinquième mois il arriva à Jérusalem, selon que la main de son Dieu était bonne sur lui.
10 Gama Ezra ya miƙa kansa ga bincike da kuma kiyaye Dokar Ubangiji, da kuma koya wa Isra’ilawa dokoki da kuma umarnan Ubangiji.
Car Esdras avait disposé son cœur à étudier la Loi de l'Eternel, et à [la] faire, et à enseigner parmi le peuple d'Israël les statuts, et les ordonnances.
11 Ga wasiƙar da sarki Artazerzes ya ba Ezra wanda yake firist da kuma malami, mutumin da yake cike da sani game da dokoki da kuma umarnan Ubangiji wa Isra’ila.
Or c'est ici la teneur des patentes que le Roi Artaxerxes donna à Esdras, Sacrificateur et Scribe, Scribe des paroles des commandements de l'Eternel et de ses ordonnances, entre les Israélites.
12 Artazerzes, sarkin sarakuna. Zuwa ga Ezra firist, malamin Dokar Allah na sama. Gaisuwa.
Artaxerxes Roi des Rois, à Esdras Sacrificateur et Scribe de la Loi du Dieu des cieux, soit une parfaite santé; et de telle date.
13 Yanzu ina ba da umarni cewa duk wani mutumin Isra’ilan da yake cikin mulkina, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da suke so su tafi tare da kai zuwa Urushalima za su iya tafiya.
J'ordonne, que tous ceux de mon Royaume qui sont du peuple d'Israël, et de ses Sacrificateurs et Lévites, qui se présenteront volontairement pour aller à Jérusalem, aillent avec toi;
14 Sarki ne da mashawartansa guda bakwai suka aike ka don ka je ka ga halin da Yahuda da Urushalima suke ciki game da dokokin Allahnka, waɗanda suke a hannunka.
Parce que tu es envoyé de la part du Roi, et de ses sept conseillers, pour t'informer en Judée, et à Jérusalem touchant la Loi de ton Dieu, laquelle tu as en ta main.
15 Za ka kuma tafi da zinariya da azurfa waɗanda sarki da mashawartansa suka ba da kyautar yardar rai ga Allah na Isra’ila, wanda haikalinsa ke a Urushalima,
Et pour porter l'argent et l'or que le Roi et ses conseillers ont volontairement offerts au Dieu d'Israël, dont la demeure est à Jérusalem;
16 haɗe da duk zinariya da azurfan da za ka iya samu a Babilon, da kuma duk bayarwar yardar rai daga mutane da firistoci, domin haikalin Allahnsu da yake a Urushalima.
Et tout l'argent et l'or que tu trouveras en toute la province de Babylone, avec les offrandes volontaires du peuple et des Sacrificateurs, offrant volontairement à la maison de leur Dieu qui habite à Jérusalem.
17 Ka tabbata ka yi amfani da kuɗin nan don ka sayi bijimai, da raguna, da’yan raguna, da hadayu na gari, da na sha, ka kuma miƙa su a kan bagade na haikalin Allahnka a Urushalima.
Afin qu'incessamment tu achètes de cet argent-là des veaux, des béliers, des agneaux, avec leurs gâteaux et leurs aspersions, et que tu les offres sur l'autel de la maison de votre Dieu, qui habite à Jérusalem.
18 Sa’an nan kai da’yan’uwanka Yahudawa ku yi abin da kuka ga ya fi kyau da sauran zinariya da azurfa ɗin bisa ga nufin Allah.
Et que vous fassiez selon la volonté de votre Dieu, ce qu'il te semblera bon à toi et à tes frères de faire du reste de l'argent et de l'or.
19 Ka kai wa Allah na Urushalima duk kayan da aka ba ka amanarsu don yin sujada a haikalin Allahnka.
Et quant aux ustensiles qui te sont donnés pour le service de la maison de ton Dieu, remets-les en la présence du Dieu de Jérusalem.
20 Duk kuma wani abin da ake bukata domin haikalin Allahnka, daga ɗakunan ajiya sarki za ka fitar da kuɗin.
Et quant au reste qui sera nécessaire pour la maison de ton Dieu, autant qu'il t'en faudra employer, tu [le] prendras de la maison des trésors du Roi.
21 Yanzu fa ni, Sarki Artazerzes, ina ba da umarni ga kowane ma’aji na Kewayen Kogin Yuferites su tanada duk abin da Ezra firist, wanda kuma yake malamin Dokar Allah na sama zai bukaci,
Et de ma part Artaxerxes Roi il est ordonné à tous les trésoriers qui sont au delà du fleuve, que tout ce qu'Esdras Sacrificateur [et] Scribe de la Loi du Dieu des cieux vous demandera soit fait incontinent.
22 har zuwa talenti ɗari na azurfa, da mudu ɗari na alkama, da garwa ɗari na ruwan inabi, da garwa ɗari na man zaitun, da kuma gishiri ba iyaka.
Jusqu'à cent talents d'argent, et jusqu'à cent Cores de froment, et jusqu'à cent Bats de vin, et jusqu'à cent Bats d'huile; et du sel sans nombre.
23 A yi duk abin da Allah na sama ya ce don haikalin Allah na sama, sai a yi shi da himma. Me zai sa a jawo wa sarki da’ya’yansa fushin Allah?
Que tout ce qui est commandé par le Dieu des cieux, soit promptement fait à la maison du Dieu des cieux; de peur qu'il n'y ait de l'indignation contre le Royaume, et contre le Roi et ses enfants.
24 Ku kuma san cewa, ba ku da ikon sa firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofin haikali, da masu aiki a gidan Allah, ko waɗansu masu aiki a haikali su biya haraji, ko kuɗin shiga.
De plus, nous vous faisons savoir qu'on ne pourra imposer ni taille, ni gabelle, ni péage sur aucun Sacrificateur, ou Lévite, ou chantre, ou portier, ou Néthinien, ou ministre de cette maison de Dieu.
25 Kai kuma Ezra, bisa ga hikimar da Allah ya ba ka, sai ka zaɓi mahukunta da alƙalai waɗanda za su zama masu yanke hukunci ga dukan mutanen Kewayen Kogin Yuferites, duk waɗanda suka san dokokin Allahnka, ka kuma koya wa duk waɗanda ba su san dokokin ba.
Et quant à toi, Esdras, établis des magistrats et des juges selon la sagesse de ton Dieu, de laquelle tu es doué, afin qu'ils fassent justice à tout ce peuple qui est au delà du fleuve; [c'est-à-dire], à tous ceux qui connaissent les lois de ton Dieu, et afin que vous enseigniez celui qui ne les saura point.
26 Ba shakka duk wanda bai yi biyayya da dokokin Allahnka ba, da kuma dokokin sarki ba dole a yanke masa hukuncin kisa, ko hukuncin kora, ko hukuncin raba shi da mallakarsa, ko kuma hukuncin kulle shi a kurkuku.
Et quant à tous ceux qui n'observeront point la Loi de ton Dieu, et la Loi du Roi, qu'il soit aussitôt jugé, soit à la mort, soit au bannissement, soit à une amende pécuniaire, ou à l'emprisonnement.
27 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na kakanninmu, ya taɓa zuciyar sarki don yă kawo ɗaukaka ga haikalin Allah a Urushalima ta wannan hanya.
Béni soit l'Eternel, le Dieu de nos pères, qui a mis une telle chose au cœur du Roi, pour honorer la maison de l'Eternel, qui habite à Jérusalem;
28 Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a gaban sarki da mashawartansa, da kuma duk manyan masu muƙami nasa. Gama Ubangiji Allahna yana tare da ni, sai na sami ƙarfin hali na tattara shugabannin mutane daga Isra’ila, don mu tafi tare.
Et qui a fait que j'ai trouvé grâce devant le Roi, devant ses conseillers, et devant tous les puissants gentils-hommes du Roi. Ainsi donc m'étant fortifié, selon que la main de l'Eternel mon Dieu [était] sur moi, j'assemblai les Chefs d'Israël, afin qu'ils montassent avec moi.

< Ezra 7 >