< Ezra 6 >

1 Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincika a duba cikin littattafan tarihin da suke a ajiye a wurin ajiyarsu a Babilon.
Então o rei Dario fez um decreto, e a casa dos arquivos, onde os tesouros foram depositados na Babilônia, foi revistada.
2 Sai aka sami takarda a Ekbatana a yankin Mediya, ga kuma abin da yake rubuce a ciki. Abin tunawa.
Um pergaminho foi encontrado em Achmetha, no palácio que fica na província de Mídia, e nele foi escrito para registro:
3 A shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus, sarki ya ba da umarni game da haikalin Allah a Urushalima, ya ce, Bari a sāke gina haikalin yă zama wurin miƙa hadayu, a kuma aza harsashin ginin haikalin. Tsayinsa zai zama ƙafa tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tasa’in.
No primeiro ano de Ciro, o rei, Ciro, o rei, fez um decreto: Quanto à casa de Deus em Jerusalém, que a casa seja construída, o lugar onde oferecem sacrifícios, e que suas fundações sejam fortemente assentadas, com sua altura sessenta côvados e sua largura sessenta côvados;
4 Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako. Daga asusun sarki kuma za a biya kuɗin aikin.
with três cursos de grandes pedras e um curso de madeira nova. Deixe que as despesas sejam feitas fora da casa do rei.
5 Kwanonin zinariya da na azurfan gidan Allah waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga haikali a Urushalima ya kawo Babilon, a mayar da su wurinsu a haikali a Urushalima; a sa su cikin gidan Allah.
Que também os vasos de ouro e prata da casa de Deus, que Nabucodonosor tirou do templo que está em Jerusalém e trouxe para a Babilônia, sejam restaurados e levados novamente para o templo que está em Jerusalém, tudo para seu lugar. Colocá-los-eis na casa de Deus. '
6 Saboda haka Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai, da ku masu muƙami na yankin, ku bar wurin.
Agora, portanto, Tattenai, governador além do rio, Shetharbozenai, e seus companheiros os afarsacitas, que estão além do rio, você deve ficar longe dali.
7 Kada ku hana wannan aiki na haikalin Allah. Bari gwamnan Yahudawa, da dattawan Yahudawa su sāke gina wannan gidan Allah a wurin da yake a dā.
Deixe a obra desta casa de Deus em paz; deixe o governador dos judeus e os anciãos dos judeus construírem esta casa de Deus em seu lugar.
8 Na kuma ba da umarni game da abin da za ku yi wa dattawan Yahudawa cikin aikin ginin wannan gidan Allah. Daga asusun sarki a kuɗin da yake shigo wa Kewayen Kogin Yuferites za a biya mutanen nan duka, domin kada aikin yă tsaya.
Moreover Eu faço um decreto a respeito do que vocês farão por estes anciãos dos judeus para a construção desta casa de Deus: o dos bens do rei, mesmo do tributo além do rio, as despesas devem ser dadas com toda diligência a estes homens, para que eles não sejam impedidos.
9 A tanada musu duk abin da suke bukata. A ba su’yan bijimai, da raguna, da’yan tumaki domin miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na sama, haka kuma dole a tanada wa firistoci alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da mai, kullum ba fasawa yadda firistoci suke yi a Urushalima
Aquilo de que eles precisam, incluindo os jovens touros, carneiros e cordeiros, para holocaustos ao Deus do céu; também trigo, sal, vinho e azeite, segundo a palavra dos sacerdotes que estão em Jerusalém, que lhes seja dado dia após dia sem falta,
10 domin su miƙa hadayu masu daɗi ga Allah na Sama, su kuma yi addu’a domin lafiyar sarki da’ya’yansa.
para que possam oferecer sacrifícios de agradável aroma ao Deus do céu, e rezar pela vida do rei e de seus filhos.
11 Na kuma yi umarni cewa duk wanda ya karya wannan doka sai a fitar da itace daga cikin gidansa, a fiƙe kan itacen, a tsire mutumin, sa’an nan a mai da gidansa juji.
Fiz também um decreto para que quem alterar esta mensagem, que uma viga seja tirada de sua casa, e que seja levantada e fixada nela; e que sua casa seja feita um monturo para isto.
12 Bari Allah yă sa sunansa yă kasance, yă hamɓarar da duka wani sarki ko mutanen da za su sa hannu don a sāke wannan doka, ko kuma don su rushe haikalin nan a Urushalima. Ni Dariyus na ba da wannan umarni, bari a yi biyayya babu wasa.
May o Deus que fez habitar ali seu nome derrubou todos os reis e povos que estendem sua mão para alterar isto, para destruir esta casa de Deus que está em Jerusalém. Eu, Dario, fiz um decreto. Que isso seja feito com toda a diligência. '
13 Saboda umarnin da sarki Dariyus ya aika, sai Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites da Shetar-Bozenai da abokansu suka yi biyayya da umarnin babu wasa.
Então Tattenai, o governador além do rio, Shetharbozenai, e seus companheiros fizeram o mesmo com toda a diligência, porque Dario, o rei, havia enviado um decreto.
14 Dattawan Yahuda kuwa suka ci gaba da ginin suna yin nasara ta wurin wa’azin Haggai annabi da Zakariya ɗan Iddo. Suka kuma gama ginin haikalin bisa ga umarnin Allah na Isra’ila da kuma umarnin Sairus da Artazerzes, sarakunan Farisa.
Os anciãos dos judeus construíram e prosperaram, através da profecia de Ageu, o profeta, e Zacarias, o filho de Iddo. Eles o construíram e terminaram, de acordo com o mandamento do Deus de Israel, e de acordo com o decreto de Ciro, Dario e Artaxerxes, rei da Pérsia.
15 An gama ginin haikalin a rana ta uku na watan Adar a shekara ta shida ta mulkin Sarki Dariyus.
Esta casa foi concluída no terceiro dia do mês de Adar, que foi no sexto ano do reinado de Dario, o rei.
16 Sai mutanen Isra’ila, firistoci, Lawiyawa da kuma sauran waɗanda suka dawo daga bauta suka yi bikin keɓe gidan Allah, cike da farin ciki.
Os filhos de Israel, os sacerdotes, os levitas e os demais filhos do cativeiro, mantiveram com alegria a dedicação desta casa de Deus.
17 Suka miƙa bijimai guda ɗari, da raguna ɗari biyu, da’yan raguna ɗari huɗu. Suka kuma miƙa hadayu don zunubi saboda dukan Isra’ila, suka kuma miƙa bunsurai guda goma sha biyu don hadaya ta zunubi, kowane bunsuru ɗaya don kowace kabila ta Isra’ila.
They ofereceu na dedicação desta casa de Deus cem touros, duzentos carneiros, quatrocentos cordeiros; e por uma oferta pelo pecado por todo Israel, doze bodes, de acordo com o número das tribos de Israel.
18 Suka kuma naɗa firistoci a gundumominsu da kuma Lawiyawa a ƙungiyoyinsu don hidimar Allah a Urushalima, bisa ga abin da aka rubuta a Littafin Musa.
Eles colocaram os sacerdotes em suas divisões e os levitas em seus cursos, para o serviço de Deus que está em Jerusalém, como está escrito no livro de Moisés.
19 A rana ta goma sha huɗu ga watan farko, sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi Bikin Ƙetarewa.
As crianças do cativeiro celebraram a Páscoa no décimo quarto dia do primeiro mês.
20 Firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka zama da tsabta. Lawiyawa suka yanka ragon Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda suka dawo daga bauta, da kuma domin’yan’uwansu firistoci, da kuma domin kansu.
Como os sacerdotes e os levitas haviam se purificado juntos, todos eles eram puros. Eles mataram a Páscoa para todos os filhos do cativeiro, para seus irmãos, os sacerdotes, e para si mesmos.
21 Sai Isra’ilawa waɗanda suka dawo daga bauta suka ci tare da duk waɗanda suka keɓe kansu daga halin ƙazanta na Al’ummai maƙwabtansu, don su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Os filhos de Israel que haviam voltado do cativeiro, e todos os que se haviam separado a eles da imundícia das nações da terra para buscar a Javé, o Deus de Israel, comeram,
22 Suka yi kwana bakwai suna Bikin Burodi Marar Yisti, suna cike da farin ciki, gama Ubangiji ya cika su da farin ciki don ya sa sarkin Assuriya ya canja tunaninsa, ya taimake su cikin aikin gidan Allah, Allah na Isra’ila.
e guardaram a festa dos pães ázimos sete dias com alegria; porque Javé os havia alegrado, e lhes havia voltado o coração do rei da Assíria, para fortalecer suas mãos na obra de Deus, o Deus da casa de Israel.

< Ezra 6 >