< Ezra 6 >
1 Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincika a duba cikin littattafan tarihin da suke a ajiye a wurin ajiyarsu a Babilon.
Alors le roi Darius rendit un décret et l’on fit des recherches dans la maison des archives, où étaient déposés les trésors, à Babylone.
2 Sai aka sami takarda a Ekbatana a yankin Mediya, ga kuma abin da yake rubuce a ciki. Abin tunawa.
Et l’on trouva à Ecbatane, la forteresse qui est en la province de Médie, un rouleau sur lequel était écrit le document suivant:
3 A shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus, sarki ya ba da umarni game da haikalin Allah a Urushalima, ya ce, Bari a sāke gina haikalin yă zama wurin miƙa hadayu, a kuma aza harsashin ginin haikalin. Tsayinsa zai zama ƙafa tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tasa’in.
« La première année du roi Cyrus, le roi Cyrus a donné cet ordre: que la maison de Dieu qui est à Jérusalem, que cette maison soit rebâtie pour être un lieu où l’on offre des sacrifices, et que les fondations soient solidement posées. Sa hauteur sera de soixante coudées et sa largeur de soixante coudées.
4 Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako. Daga asusun sarki kuma za a biya kuɗin aikin.
Il y aura trois rangées de pierre de taille et une rangée de bois; la dépense sera payée par la maison du roi.
5 Kwanonin zinariya da na azurfan gidan Allah waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga haikali a Urushalima ya kawo Babilon, a mayar da su wurinsu a haikali a Urushalima; a sa su cikin gidan Allah.
En outre, on rendra les ustensiles d’or et d’argent de la maison de Dieu, que Nabuchodonosor avait enlevés du temple qui est à Jérusalem, et ils seront transportés au temple qui est à Jérusalem, à la place où ils étaient, et tu les déposeras dans la maison de Dieu. »
6 Saboda haka Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai, da ku masu muƙami na yankin, ku bar wurin.
« ... Maintenant, Thathanaï, gouverneur d’au delà du fleuve, Stharbuzanaï et vos compagnons d’Apharsach, qui êtes au delà du fleuve, tenez-vous éloignés de là,
7 Kada ku hana wannan aiki na haikalin Allah. Bari gwamnan Yahudawa, da dattawan Yahudawa su sāke gina wannan gidan Allah a wurin da yake a dā.
et laissez continuer les travaux de cette maison de Dieu; que le gouverneur des Juifs et les anciens des Juifs rebâtissent cette maison de Dieu sur son ancien emplacement.
8 Na kuma ba da umarni game da abin da za ku yi wa dattawan Yahudawa cikin aikin ginin wannan gidan Allah. Daga asusun sarki a kuɗin da yake shigo wa Kewayen Kogin Yuferites za a biya mutanen nan duka, domin kada aikin yă tsaya.
Voici l’ordre que je donne touchant ce que vous devez faire avec ces anciens des Juifs pour rebâtir cette maison de Dieu: sur les biens du roi, provenant des impôts d’au delà du fleuve, la dépense sera exactement payée à ces hommes, afin qu’il n’y ait pas d’interruption.
9 A tanada musu duk abin da suke bukata. A ba su’yan bijimai, da raguna, da’yan tumaki domin miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na sama, haka kuma dole a tanada wa firistoci alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da mai, kullum ba fasawa yadda firistoci suke yi a Urushalima
Ce qui sera nécessaire pour les holocaustes du Dieu du ciel, jeunes taureaux, béliers et agneaux, froment, sel, vin et huile, selon l’ordonnance des prêtres qui sont à Jérusalem, leur sera donné jour par jour, sans faute,
10 domin su miƙa hadayu masu daɗi ga Allah na Sama, su kuma yi addu’a domin lafiyar sarki da’ya’yansa.
afin qu’ils offrent des sacrifices d’agréable odeur au Dieu du ciel, et qu’ils prient pour la vie du roi et de ses fils.
11 Na kuma yi umarni cewa duk wanda ya karya wannan doka sai a fitar da itace daga cikin gidansa, a fiƙe kan itacen, a tsire mutumin, sa’an nan a mai da gidansa juji.
Je donne aussi cet ordre: Si quelqu’un change cette parole, qu’on arrache de sa maison une poutre, qu’il y soit suspendu et attaché, et qu’à cause de cela l’on fasse de sa maison un tas d’immondices.
12 Bari Allah yă sa sunansa yă kasance, yă hamɓarar da duka wani sarki ko mutanen da za su sa hannu don a sāke wannan doka, ko kuma don su rushe haikalin nan a Urushalima. Ni Dariyus na ba da wannan umarni, bari a yi biyayya babu wasa.
Que le Dieu qui fait résider là son nom renverse tout roi et tout peuple qui étendraient la main pour changer ce décret et détruire cette maison de Dieu qui est à Jérusalem! Moi, Darius, j’ai donné cet ordre: qu’il soit ponctuellement exécuté. »
13 Saboda umarnin da sarki Dariyus ya aika, sai Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites da Shetar-Bozenai da abokansu suka yi biyayya da umarnin babu wasa.
Alors Thathanaï, gouverneur d’au delà du fleuve, Stharbuzanaï et leurs compagnons se conformèrent ponctuellement à l’ordre que le roi Darius leur avait envoyé.
14 Dattawan Yahuda kuwa suka ci gaba da ginin suna yin nasara ta wurin wa’azin Haggai annabi da Zakariya ɗan Iddo. Suka kuma gama ginin haikalin bisa ga umarnin Allah na Isra’ila da kuma umarnin Sairus da Artazerzes, sarakunan Farisa.
Et les anciens d’Israël se mirent à bâtir et firent des progrès, soutenus par les prophéties d’Aggée, le prophète, et de Zacharie, fils d’Addo. Ils bâtirent et achevèrent, d’après l’ordre du Dieu d’Israël et d’après l’ordre de Cyrus, de Darius et d’Artaxerxès, roi de Perse.
15 An gama ginin haikalin a rana ta uku na watan Adar a shekara ta shida ta mulkin Sarki Dariyus.
On acheva cette maison le troisième jour du mois d’Adar, dans la sixième année du règne du roi Darius.
16 Sai mutanen Isra’ila, firistoci, Lawiyawa da kuma sauran waɗanda suka dawo daga bauta suka yi bikin keɓe gidan Allah, cike da farin ciki.
Les enfants d’Israël, les prêtres et les lévites, et le reste des fils de la captivité, firent avec joie la dédicace de cette maison de Dieu.
17 Suka miƙa bijimai guda ɗari, da raguna ɗari biyu, da’yan raguna ɗari huɗu. Suka kuma miƙa hadayu don zunubi saboda dukan Isra’ila, suka kuma miƙa bunsurai guda goma sha biyu don hadaya ta zunubi, kowane bunsuru ɗaya don kowace kabila ta Isra’ila.
Ils offrirent, pour la dédicace de cette maison de Dieu, cent taureaux, deux cents béliers, quatre cents agneaux, et, comme victimes pour le péché, en faveur de tout Israël, douze boucs, d’après le nombre des tribus d’Israël.
18 Suka kuma naɗa firistoci a gundumominsu da kuma Lawiyawa a ƙungiyoyinsu don hidimar Allah a Urushalima, bisa ga abin da aka rubuta a Littafin Musa.
Ils établirent les prêtres selon leurs divisions et les lévites selon leurs classes pour le service du Dieu qui est à Jérusalem, comme il est écrit dans le livre de Moïse.
19 A rana ta goma sha huɗu ga watan farko, sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi Bikin Ƙetarewa.
Les fils de la captivité célébrèrent la Pâque le quatorzième jour du premier mois.
20 Firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka zama da tsabta. Lawiyawa suka yanka ragon Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda suka dawo daga bauta, da kuma domin’yan’uwansu firistoci, da kuma domin kansu.
Car les prêtres et les lévites sans exception s’étaient purifiés; tous étaient purs; et ils immolèrent la Pâque pour tous les fils de la captivité, pour leurs frères les prêtres et pour eux-mêmes.
21 Sai Isra’ilawa waɗanda suka dawo daga bauta suka ci tare da duk waɗanda suka keɓe kansu daga halin ƙazanta na Al’ummai maƙwabtansu, don su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Les enfants d’Israël revenus de la captivité mangèrent la Pâque, ainsi que tous ceux qui s’étaient séparés de l’impureté des nations du pays pour se joindre à eux afin de chercher Yahweh, le Dieu d’Israël.
22 Suka yi kwana bakwai suna Bikin Burodi Marar Yisti, suna cike da farin ciki, gama Ubangiji ya cika su da farin ciki don ya sa sarkin Assuriya ya canja tunaninsa, ya taimake su cikin aikin gidan Allah, Allah na Isra’ila.
Ils célébrèrent avec joie pendant sept jours la fête des Azymes; car Yahweh les avait réjouis en tournant vers eux le cœur du roi d’Assyrie, pour soutenir leurs mains dans l’œuvre de la maison de Dieu, du Dieu d’Israël.