< Ezra 6 >
1 Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincika a duba cikin littattafan tarihin da suke a ajiye a wurin ajiyarsu a Babilon.
Then Darius king the he made a decree and they searched - in [the] house books the where treasures the [were] deposited there in Babylon.
2 Sai aka sami takarda a Ekbatana a yankin Mediya, ga kuma abin da yake rubuce a ciki. Abin tunawa.
And it was found in Ecbatana in citadel the which [is] in Media province the a scroll one and as follows it was written in midst its memorandum.
3 A shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus, sarki ya ba da umarni game da haikalin Allah a Urushalima, ya ce, Bari a sāke gina haikalin yă zama wurin miƙa hadayu, a kuma aza harsashin ginin haikalin. Tsayinsa zai zama ƙafa tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tasa’in.
In year one of Cyrus king the Cyrus king the he made a decree [the] house of God in Jerusalem house the let it be built a place which [they were] sacrificing sacrifices and foundations its [be] retained height its cubits sixty width its cubits sixty.
4 Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako. Daga asusun sarki kuma za a biya kuɗin aikin.
Rows of stone of rolling three and a row of timber new and expense the from [the] house of king the let it be given.
5 Kwanonin zinariya da na azurfan gidan Allah waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga haikali a Urushalima ya kawo Babilon, a mayar da su wurinsu a haikali a Urushalima; a sa su cikin gidan Allah.
And also [the] vessels of [the] house of God of gold and silver which Nebuchadnezzar he brought out from temple the which [was] in Jerusalem and he carried to Babylon let them send back and let it go to temple the which [is] in Jerusalem to place its so you may deposit [them] in [the] house of God.
6 Saboda haka Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai, da ku masu muƙami na yankin, ku bar wurin.
Now O Tattenai [the] governor of [the] region beyond river the Shethar-Bozenai and associates their officials the who [are] in [the] region beyond river the far be! from there.
7 Kada ku hana wannan aiki na haikalin Allah. Bari gwamnan Yahudawa, da dattawan Yahudawa su sāke gina wannan gidan Allah a wurin da yake a dā.
Leave! [the] work of [the] house of God this [the] governor of Jews the and [the] elders of Jews the [the] house of God this let them build on place its.
8 Na kuma ba da umarni game da abin da za ku yi wa dattawan Yahudawa cikin aikin ginin wannan gidan Allah. Daga asusun sarki a kuɗin da yake shigo wa Kewayen Kogin Yuferites za a biya mutanen nan duka, domin kada aikin yă tsaya.
And from me it is made a decree to whatever that you will do with [the] elders of Jews the these to build [the] house of God this and from [the] properti of king the which [is] [the] tribute of [the] region beyond river the diligently expense the let it be given to men the these that not to make to cease.
9 A tanada musu duk abin da suke bukata. A ba su’yan bijimai, da raguna, da’yan tumaki domin miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na sama, haka kuma dole a tanada wa firistoci alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da mai, kullum ba fasawa yadda firistoci suke yi a Urushalima
And whatever things needed and young of bulls and rams and lambs - for burnt offerings - to [the] God of heavens the wheat salt - wine and oil according to [the] word of priests the who [are] in Jerusalem it will be given to them day - by day that not negligence.
10 domin su miƙa hadayu masu daɗi ga Allah na Sama, su kuma yi addu’a domin lafiyar sarki da’ya’yansa.
That they will be offering soothing offerings to [the] God of heavens the and praying for [the] life of king the and sons his.
11 Na kuma yi umarni cewa duk wanda ya karya wannan doka sai a fitar da itace daga cikin gidansa, a fiƙe kan itacen, a tsire mutumin, sa’an nan a mai da gidansa juji.
And from me it is made a decree that every person who he will violate command the this let it be pulled away a beam from house his and [he will] be lifted up let him be impaled on it and house his a refuse-heap let it be made on this.
12 Bari Allah yă sa sunansa yă kasance, yă hamɓarar da duka wani sarki ko mutanen da za su sa hannu don a sāke wannan doka, ko kuma don su rushe haikalin nan a Urushalima. Ni Dariyus na ba da wannan umarni, bari a yi biyayya babu wasa.
And God who he has caused to dwell name his there may he overthrow every king and people who - he will stretch out hand his to violate to destroy [the] house of God this which [is] in Jerusalem I Darius I make a decree diligently let it be done.
13 Saboda umarnin da sarki Dariyus ya aika, sai Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites da Shetar-Bozenai da abokansu suka yi biyayya da umarnin babu wasa.
Then Tattenai [the] governor of [the] region beyond river the Shethar-Bozenai and associates their before that he had sent Darius king the accordingly diligently they did.
14 Dattawan Yahuda kuwa suka ci gaba da ginin suna yin nasara ta wurin wa’azin Haggai annabi da Zakariya ɗan Iddo. Suka kuma gama ginin haikalin bisa ga umarnin Allah na Isra’ila da kuma umarnin Sairus da Artazerzes, sarakunan Farisa.
And [the] elders of Jews the [were] building and prospering by [the] prophesying of Haggai (prophet the *Q(K)*) and Zechariah [the] son of Iddo and they built and they finished according to [the] decree of [the] God of Israel and according to [the] decree of Cyrus and Darius and Artaxerxes [the] king of Persia.
15 An gama ginin haikalin a rana ta uku na watan Adar a shekara ta shida ta mulkin Sarki Dariyus.
And it was brought forth house the this until day three of [the] month of Adar which it [was] year six of [the] reign of Darius king the.
16 Sai mutanen Isra’ila, firistoci, Lawiyawa da kuma sauran waɗanda suka dawo daga bauta suka yi bikin keɓe gidan Allah, cike da farin ciki.
And they made [the] people of Israel priests the and Levites the and [the] rest of [the] people of exile the [the] dedication of [the] house of God this with joy.
17 Suka miƙa bijimai guda ɗari, da raguna ɗari biyu, da’yan raguna ɗari huɗu. Suka kuma miƙa hadayu don zunubi saboda dukan Isra’ila, suka kuma miƙa bunsurai guda goma sha biyu don hadaya ta zunubi, kowane bunsuru ɗaya don kowace kabila ta Isra’ila.
And they offered for [the] dedication of [the] house of God this bulls one hundred rams two hundred lambs four hundred and he-goats of goats (for a sin offering *Q(K)*) on all Israel two [plus] ten to [the] number of [the] tribes of Israel.
18 Suka kuma naɗa firistoci a gundumominsu da kuma Lawiyawa a ƙungiyoyinsu don hidimar Allah a Urushalima, bisa ga abin da aka rubuta a Littafin Musa.
And they appointed priests the in divisions their and Levites the in classes their over [the] service of God which [is] in Jerusalem according to [the] writing of [the] book of Moses.
19 A rana ta goma sha huɗu ga watan farko, sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi Bikin Ƙetarewa.
And they celebrated [the] children of the exile the passover on [day] four-teen of the month the first.
20 Firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka zama da tsabta. Lawiyawa suka yanka ragon Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda suka dawo daga bauta, da kuma domin’yan’uwansu firistoci, da kuma domin kansu.
For they had purified themselves the priests and the Levites as one all of them [were] pure and they slaughtered the passover for all [the] children of the exile and for brothers their the priests and for themselves.
21 Sai Isra’ilawa waɗanda suka dawo daga bauta suka ci tare da duk waɗanda suka keɓe kansu daga halin ƙazanta na Al’ummai maƙwabtansu, don su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And they ate [the] people of Israel who had returned from the exile and every [one who] had separated himself from [the] uncleanness of [the] nations of the land to them to seek Yahweh [the] God of Israel.
22 Suka yi kwana bakwai suna Bikin Burodi Marar Yisti, suna cike da farin ciki, gama Ubangiji ya cika su da farin ciki don ya sa sarkin Assuriya ya canja tunaninsa, ya taimake su cikin aikin gidan Allah, Allah na Isra’ila.
And they celebrated [the] feast of unleavened bread seven days with joy for - he had made rejoice them Yahweh and he had turned [the] heart of [the] king of Assyria towards them to make strong hands their in [the] work of [the] house of God [the] God of Israel.