< Ezra 6 >

1 Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincika a duba cikin littattafan tarihin da suke a ajiye a wurin ajiyarsu a Babilon.
Then Darius the king made a decree, and they sought in the house of the scrolls of the treasuries placed there in Babylon,
2 Sai aka sami takarda a Ekbatana a yankin Mediya, ga kuma abin da yake rubuce a ciki. Abin tunawa.
and there has been found at Achmetha, in a palace that [is] in the province of Media, a scroll, and a record thus written within it [is]:
3 A shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus, sarki ya ba da umarni game da haikalin Allah a Urushalima, ya ce, Bari a sāke gina haikalin yă zama wurin miƙa hadayu, a kuma aza harsashin ginin haikalin. Tsayinsa zai zama ƙafa tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tasa’in.
“In the first year of Cyrus the king, Cyrus the king has made a decree concerning the house of God in Jerusalem: let the house be built in the place where they are sacrificing sacrifices, and its foundations strongly laid; its height sixty cubits, its breadth sixty cubits;
4 Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako. Daga asusun sarki kuma za a biya kuɗin aikin.
three rows of rolled stones, and a row of new wood, and let the outlay be given out of the king’s house.
5 Kwanonin zinariya da na azurfan gidan Allah waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga haikali a Urushalima ya kawo Babilon, a mayar da su wurinsu a haikali a Urushalima; a sa su cikin gidan Allah.
And also, the vessels of the house of God, of gold and silver, that Nebuchadnezzar took forth out of the temple that [is] in Jerusalem, and brought to Babylon, let be given back, and go to the temple that [is] in Jerusalem, [each] to its place, and put [them] down in the house of God.
6 Saboda haka Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai, da ku masu muƙami na yankin, ku bar wurin.
Now Tatnai, governor beyond the river, Shethar-Boznai, and their companions, the Apharsachites, who [are] beyond the river, be far from here;
7 Kada ku hana wannan aiki na haikalin Allah. Bari gwamnan Yahudawa, da dattawan Yahudawa su sāke gina wannan gidan Allah a wurin da yake a dā.
let alone the work of this house of God, let the governor of the Jews, and [the] elders of the Jews, build this house of God on its place.
8 Na kuma ba da umarni game da abin da za ku yi wa dattawan Yahudawa cikin aikin ginin wannan gidan Allah. Daga asusun sarki a kuɗin da yake shigo wa Kewayen Kogin Yuferites za a biya mutanen nan duka, domin kada aikin yă tsaya.
And a decree is made by me concerning that which you do with [the] elders of these Jews to build this house of God, that of [the] riches of [the] king, that [are] of [the] tribute beyond [the] river, let the outlay be given speedily to these men, that they do not cease;
9 A tanada musu duk abin da suke bukata. A ba su’yan bijimai, da raguna, da’yan tumaki domin miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na sama, haka kuma dole a tanada wa firistoci alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da mai, kullum ba fasawa yadda firistoci suke yi a Urushalima
and what they are needing—both young bullocks, and rams, and lambs for burnt-offerings to the God of the heavens, wheat, salt, wine, and oil according to the saying of the priests who [are] in Jerusalem—let be given to them day by day without fail,
10 domin su miƙa hadayu masu daɗi ga Allah na Sama, su kuma yi addu’a domin lafiyar sarki da’ya’yansa.
that they are bringing sweet savors near to the God of the heavens, and praying for the life of the king, and of his sons.
11 Na kuma yi umarni cewa duk wanda ya karya wannan doka sai a fitar da itace daga cikin gidansa, a fiƙe kan itacen, a tsire mutumin, sa’an nan a mai da gidansa juji.
And a decree is made by me, that anyone who changes this thing, let wood be pulled down from his house, and being raised up, let him be struck on it, and let his house be made a dunghill for this.
12 Bari Allah yă sa sunansa yă kasance, yă hamɓarar da duka wani sarki ko mutanen da za su sa hannu don a sāke wannan doka, ko kuma don su rushe haikalin nan a Urushalima. Ni Dariyus na ba da wannan umarni, bari a yi biyayya babu wasa.
And God, who caused His Name to dwell there, casts down any king and people that puts forth his hand to change, to destroy this house of God that [is] in Jerusalem; I Darius have made a decree; let it be done speedily.”
13 Saboda umarnin da sarki Dariyus ya aika, sai Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites da Shetar-Bozenai da abokansu suka yi biyayya da umarnin babu wasa.
Then Tatnai, governor beyond the river, Shethar-Boznai, and their companions, according to that which Darius the king has sent, so they have done speedily;
14 Dattawan Yahuda kuwa suka ci gaba da ginin suna yin nasara ta wurin wa’azin Haggai annabi da Zakariya ɗan Iddo. Suka kuma gama ginin haikalin bisa ga umarnin Allah na Isra’ila da kuma umarnin Sairus da Artazerzes, sarakunan Farisa.
and [the] elders of [the] Jews are building and prospering through [the] prophecy of Haggai [the] prophet, and Zechariah son of Iddo, and they have built and finished by [the] decree of [the] God of Israel, and by [the] decree of Cyrus, and Darius, and Artaxerxes king of Persia.
15 An gama ginin haikalin a rana ta uku na watan Adar a shekara ta shida ta mulkin Sarki Dariyus.
And this house has gone out until the third day of the month Adar, that is [in] the sixth year of the reign of Darius the king.
16 Sai mutanen Isra’ila, firistoci, Lawiyawa da kuma sauran waɗanda suka dawo daga bauta suka yi bikin keɓe gidan Allah, cike da farin ciki.
And the sons of Israel have made, [and] the priests, and the Levites, and the rest of the sons of the captivity, a dedication of this house of God with joy,
17 Suka miƙa bijimai guda ɗari, da raguna ɗari biyu, da’yan raguna ɗari huɗu. Suka kuma miƙa hadayu don zunubi saboda dukan Isra’ila, suka kuma miƙa bunsurai guda goma sha biyu don hadaya ta zunubi, kowane bunsuru ɗaya don kowace kabila ta Isra’ila.
and have brought near for the dedication of this house of God: one hundred bullocks, two hundred rams, four hundred lambs; and twelve young male goats for a sin-offering for all Israel according to the number of the tribes of Israel;
18 Suka kuma naɗa firistoci a gundumominsu da kuma Lawiyawa a ƙungiyoyinsu don hidimar Allah a Urushalima, bisa ga abin da aka rubuta a Littafin Musa.
and they have established the priests in their divisions, and the Levites in their courses, over the service of God that [is] in Jerusalem, as it is written in the scroll of Moses.
19 A rana ta goma sha huɗu ga watan farko, sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi Bikin Ƙetarewa.
And the sons of the captivity make the Passover on the fourteenth of the first month,
20 Firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka zama da tsabta. Lawiyawa suka yanka ragon Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda suka dawo daga bauta, da kuma domin’yan’uwansu firistoci, da kuma domin kansu.
for the priests and the Levites have been purified together—all of them [are] pure—and they slaughter the Passover for all the sons of the captivity, and for their brothers the priests, and for themselves.
21 Sai Isra’ilawa waɗanda suka dawo daga bauta suka ci tare da duk waɗanda suka keɓe kansu daga halin ƙazanta na Al’ummai maƙwabtansu, don su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And the sons of Israel, those returning from the captivity, and everyone who is separated from the uncleanness of the nations of the land to them, to seek to YHWH, God of Israel, eat,
22 Suka yi kwana bakwai suna Bikin Burodi Marar Yisti, suna cike da farin ciki, gama Ubangiji ya cika su da farin ciki don ya sa sarkin Assuriya ya canja tunaninsa, ya taimake su cikin aikin gidan Allah, Allah na Isra’ila.
and they make the Celebration of Unleavened Things seven days with joy, for YHWH made them to rejoice, and turned around the heart of the king of Asshur to them, to strengthen their hands in the work of the house of God, the God of Israel.

< Ezra 6 >