< Ezra 6 >
1 Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincika a duba cikin littattafan tarihin da suke a ajiye a wurin ajiyarsu a Babilon.
Then king Darius instructed, and they searched in the library of books that were deposited in Babylon.
2 Sai aka sami takarda a Ekbatana a yankin Mediya, ga kuma abin da yake rubuce a ciki. Abin tunawa.
And there was found at Ecbatana, which is a fortified place in the province of Media, one volume, and this record was written in it:
3 A shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus, sarki ya ba da umarni game da haikalin Allah a Urushalima, ya ce, Bari a sāke gina haikalin yă zama wurin miƙa hadayu, a kuma aza harsashin ginin haikalin. Tsayinsa zai zama ƙafa tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tasa’in.
“In the first year of king Cyrus, Cyrus the king decreed that the house of God, which is in Jerusalem, shall be built in the place where they immolate victims, and that they should set the foundations so as to support a height of sixty cubits and a width of sixty cubits,
4 Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako. Daga asusun sarki kuma za a biya kuɗin aikin.
with three rows of rough stones, and so as to have rows of new timber, and that the expenses shall be given from the house of the king.
5 Kwanonin zinariya da na azurfan gidan Allah waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga haikali a Urushalima ya kawo Babilon, a mayar da su wurinsu a haikali a Urushalima; a sa su cikin gidan Allah.
But also, let the gold and silver vessels of the temple of God, which Nebuchadnezzar took from the temple of Jerusalem, and which he carried away to Babylon, be restored and be carried back to the temple of Jerusalem, to their place, just as they had been placed in the temple of God.
6 Saboda haka Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai, da ku masu muƙami na yankin, ku bar wurin.
Now therefore, let Tattenai, the governor of the region which is beyond the river, Shetharbozenai, and your counselors, the rulers who are beyond the river, withdraw far away from them,
7 Kada ku hana wannan aiki na haikalin Allah. Bari gwamnan Yahudawa, da dattawan Yahudawa su sāke gina wannan gidan Allah a wurin da yake a dā.
and let this temple of God be released to the governor of the Jews and to their elders, so that they may build that house of God in its place.
8 Na kuma ba da umarni game da abin da za ku yi wa dattawan Yahudawa cikin aikin ginin wannan gidan Allah. Daga asusun sarki a kuɗin da yake shigo wa Kewayen Kogin Yuferites za a biya mutanen nan duka, domin kada aikin yă tsaya.
Moreover, it has been instructed by me as to what ought to be done by those priests of the Jews, so that the house of God may be built, specifically, that from the king’s treasury, that is, from the tribute which is taken from the region beyond the river, the expenses shall be scrupulously given to those men, so that the work may not be impeded.
9 A tanada musu duk abin da suke bukata. A ba su’yan bijimai, da raguna, da’yan tumaki domin miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na sama, haka kuma dole a tanada wa firistoci alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da mai, kullum ba fasawa yadda firistoci suke yi a Urushalima
But if it may be necessary, let also calves, and lambs, and young goats for holocausts to the God of heaven, with grain, salt, wine, and oil, according to the rite of the priests who are in Jerusalem, be given to them for each day, so that there may be no complaint in anything.
10 domin su miƙa hadayu masu daɗi ga Allah na Sama, su kuma yi addu’a domin lafiyar sarki da’ya’yansa.
And let them offer oblations to the God of heaven, and let them pray for the life of the king and for the lives of his sons.
11 Na kuma yi umarni cewa duk wanda ya karya wannan doka sai a fitar da itace daga cikin gidansa, a fiƙe kan itacen, a tsire mutumin, sa’an nan a mai da gidansa juji.
Therefore, the decree has been set forth by me, so that, if there be any man who will change this order, a beam shall be taken from his own house, and it shall be set up, and he shall be nailed to it. Then his house shall be confiscated.
12 Bari Allah yă sa sunansa yă kasance, yă hamɓarar da duka wani sarki ko mutanen da za su sa hannu don a sāke wannan doka, ko kuma don su rushe haikalin nan a Urushalima. Ni Dariyus na ba da wannan umarni, bari a yi biyayya babu wasa.
So then, may the God who has caused his name to live there destroy any kingdoms or people who would extend their hand to fight against or to destroy that house of God, which is in Jerusalem. I, Darius, have established the decree, which I wish to be fulfilled scrupulously.”
13 Saboda umarnin da sarki Dariyus ya aika, sai Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites da Shetar-Bozenai da abokansu suka yi biyayya da umarnin babu wasa.
Therefore, Tattenai, the governor of the region beyond the river, and Shetharbozenai, and his counselors, in accord with what king Darius had instructed, diligently executed the same.
14 Dattawan Yahuda kuwa suka ci gaba da ginin suna yin nasara ta wurin wa’azin Haggai annabi da Zakariya ɗan Iddo. Suka kuma gama ginin haikalin bisa ga umarnin Allah na Isra’ila da kuma umarnin Sairus da Artazerzes, sarakunan Farisa.
Then the elders of the Jews were building and prospering, in accord with the prophecy of Haggai, the prophet, and Zechariah, the son of Iddo. And they built and constructed by the order of the God of Israel, and by the order of Cyrus and Darius, as well as Artaxerxes, the kings of the Persians.
15 An gama ginin haikalin a rana ta uku na watan Adar a shekara ta shida ta mulkin Sarki Dariyus.
And they completed this house of God on the third day of the month of Adar, which was in the sixth year of the reign of king Darius.
16 Sai mutanen Isra’ila, firistoci, Lawiyawa da kuma sauran waɗanda suka dawo daga bauta suka yi bikin keɓe gidan Allah, cike da farin ciki.
Then the sons of Israel, the priests, and the Levites, and the remainder of the sons of the transmigration celebrated the dedication of the house of God with gladness.
17 Suka miƙa bijimai guda ɗari, da raguna ɗari biyu, da’yan raguna ɗari huɗu. Suka kuma miƙa hadayu don zunubi saboda dukan Isra’ila, suka kuma miƙa bunsurai guda goma sha biyu don hadaya ta zunubi, kowane bunsuru ɗaya don kowace kabila ta Isra’ila.
And they offered, for the dedication of the house of God, one hundred calves, two hundred rams, four hundred lambs, and, as a sin offering for all of Israel, twelve he-goats from among the goats, according to the number of the tribes of Israel.
18 Suka kuma naɗa firistoci a gundumominsu da kuma Lawiyawa a ƙungiyoyinsu don hidimar Allah a Urushalima, bisa ga abin da aka rubuta a Littafin Musa.
And they appointed the priests into their divisions, and the Levites into their turns, over the works of God in Jerusalem, just as it was written in the book of Moses.
19 A rana ta goma sha huɗu ga watan farko, sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi Bikin Ƙetarewa.
Then the sons of Israel of the transmigration kept the Passover, on the fourteenth day of the first month.
20 Firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka zama da tsabta. Lawiyawa suka yanka ragon Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda suka dawo daga bauta, da kuma domin’yan’uwansu firistoci, da kuma domin kansu.
For the priests and Levites had been purified as one. All were cleansed in order to immolate the Passover for all the sons of the transmigration, and for their brothers, the priests, and for themselves.
21 Sai Isra’ilawa waɗanda suka dawo daga bauta suka ci tare da duk waɗanda suka keɓe kansu daga halin ƙazanta na Al’ummai maƙwabtansu, don su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And the sons of Israel, who had been returned from the transmigration, and all those who had separated themselves from the defilement of the Gentiles of the earth to them, so that they might seek the Lord, the God of Israel, ate
22 Suka yi kwana bakwai suna Bikin Burodi Marar Yisti, suna cike da farin ciki, gama Ubangiji ya cika su da farin ciki don ya sa sarkin Assuriya ya canja tunaninsa, ya taimake su cikin aikin gidan Allah, Allah na Isra’ila.
and kept the solemnity of unleavened bread for seven days with joy. For the Lord had made them joyful, and he had converted the heart of the king of Assur to them, so that he would assist their hands in the work of the house of the Lord, the God of Israel.