< Ezra 5 >

1 Sai annabi Haggai, da annabi Zakariya zuriyar Iddo, suka yi wa Yahudawa a Yahuda da Urushalima annabci a cikin sunan Allah na Isra’ila wanda yake da mulki a kansu.
Or, le prophète Haggaï et le prophète Zacharie, fils d’Iddo, adressèrent des prophéties aux Judéens, établis en Judée et à Jérusalem, au nom du Dieu d’Israël, qui leur en avait donné mission.
2 Sa’an nan Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da Yeshuwa ɗan Yozadak suka yi shiri suka kama aikin sāke gina gidan Allah a Urushalima. Annabawan Allah kuwa suna tare da su, suna taimakonsu.
Alors Zorobabel, fils de Chealtiël, et Yêchoua, fils de Joçadak, se mirent à reprendre la construction du temple de Dieu à Jérusalem, ayant à leurs côtés les prophètes de Dieu pour les seconder.
3 A wannan lokaci, Tattenai gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu suka je wurinsu suka tambaye su cewa, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali har ku gyara katangar?”
Mais tout de suite, Tattenaï, gouverneur des pays en deçà du fleuve, Chetar Bozenaï et consorts vinrent les trouver, et leur parlèrent en ces termes: "Qui est-ce qui vous a délivré l’autorisation de rebâtir cette maison et de rétablir ces murailles?"
4 Suka kuma tambaye su “Ina sunayen waɗanda suke wannan gini?”
En même temps ils ajoutèrent ces paroles: "Quels sont les noms des hommes qui s’occupent de cette construction?"
5 Amma Allah yana tsaron dattawan Yahudawa, saboda haka ba a hana su aikin ba har sai rahoto ya kai wurin Dariyus aka kuma sami amsarsa a rubuce tukuna.
Mais la protection de Dieu s’étendait sur les anciens des Judéens, et on ne les empêcha pas de continuer avant qu’un rapport parvînt à Darius et qu’on leur retournât une réponse écrite sur cette affaire.
6 Ga wasiƙar da Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu masu riƙe da muƙamai a Kewayen Kogin Yuferites suka aika wa Sarki Dariyus.
Teneur de la missive que Tattenaï, gouverneur des pays en deçà du fleuve, Chetar Bozenaï et ses suivants, les Afarsakéens établis en deçà du fleuve, expédièrent au roi Darius.
7 Ga rahoton da suka aika masa. Zuwa ga Sarki Dariyus. Gaisuwa da fatan alheri.
Ils lui transmirent un compte rendu, et voici ce qui s’y trouvait consigné: "A Darius, paix parfaite!
8 Ya kamata sarki yă sani cewa mun je yankin Yahuda, zuwa gidan Allah mai girma. Muka ga mutanen suna ginin haikalin da manyan duwatsu, suna sa katakai a bangon. Ana aikin da ƙwazo, aikin kuma yana cin gaba sosai, suna kuma lura da shi.
Il faut que le roi sache que nous nous sommes rendus dans la province de Judée, au temple du Dieu puissant; ce temple est en train d’être construit en pierres de taille, et des poutres en bois sont posées dans les murs. Le travail se poursuit avec diligence et progresse entre leurs mains.
9 Mun tambayi dattawan muka ce musu, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali, ku kuma sāke gyara katangarsa?”
Nous avons aussitôt interrogé les Anciens parmi eux et leur avons posé cette question: "Qui est-ce qui vous a délivré l’autorisation de rebâtir cette maison et de rétablir ces murailles?"
10 Muka kuma tambaye su sunayensu don mu rubuta mu sanar da kai waɗanda suke shugabanninsu.
Nous leur avons aussi demandé leurs noms pour les porter à ta connaissance, en mettant par écrit les noms de ceux qui sont à leur tête.
11 Wannan ita ce amsar da suka ba mu. “Mu bayin Allah na sama da ƙasa ne, muna sāke gina haikalin da aka gina tun shekaru da yawa da suka wuce, da wani babban sarkin Isra’ila ya gina ya kuma gama.
Voici la déclaration qu’ils nous ont faite en réponse: "Nous sommes les serviteurs du Dieu du ciel et de la terre, et nous reconstruisons la maison qui avait été bâtie, il y a de longues années de cela; c’est un grand roi d’Israël qui l’avait bâtie et achevée.
12 Amma domin kakanninmu sun ɓata wa Allah na sama rai, sai ya bari suka fāɗa cikin hannun Nebukadnezzar mutumin Kaldiya, sarkin Babilon, wanda ya rushe wannan haikali, ya kuma kwashe mutane zuwa Babilon.
Seulement, nos ancêtres ayant irrité le Dieu du ciel, celui-ci les livra au pouvoir de Nabuchodonosor, roi de Babylone, le Chaldéen, qui renversa ce temple et déporta la population en Babylonie.
13 “Duk da haka, a shekara ta farko ta mulkin Sairus sarkin Babilon, Sarki Sairus ya ba da umarni cewa a sāke gina wannan gidan Allah.
Toutefois, dans la première année de Cyrus, roi de Babylone, le roi Cyrus rendit un édit prescrivant de rebâtir ce temple de Dieu.
14 Ya kuma kwashe kwanonin zinariya da azurfa na gidan Allah daga haikalin Babilon waɗanda Nebukadnezzar ya kwasa daga haikali a Urushalima. Sa’an nan sarki Sairus ya ba wa wani mutum mai suna Sheshbazzar umarni wanda ya sa ya zama gwamna,
En outre, les ustensiles de la maison de Dieu, en or et en argent, que Nabuchodonosor avait enlevés du sanctuaire de Jérusalem et transportés dans le sanctuaire de Babylone, le roi Cyrus les fit retirer du sanctuaire de Babylone et remettre au nommé Chêchbaçar, qu’il avait désigné comme gouverneur,
15 ya ce masa, ‘Ka kwashe kayan nan ka je ka zuba su a cikin haikalin Allah a Urushalima. Ka kuma sāke gina gidan Allah a wurin da yake a dā.’
en lui disant: "Les ustensiles que voici, prends-les et va les déposer dans le sanctuaire de Jérusalem; que la maison de Dieu soit rebâtie sur son emplacement."
16 “Saboda haka Sheshbazzar ya so ya aza harsashin gina gidan Allah a Urushalima. Tun daga wancan lokaci har zuwa yau ana kan gina shi amma ba a gama ba.”
C’Est alors que ce Chêchbaçar vint ici; il posa les fondations de la maison de Dieu à Jérusalem; depuis lors on travaille à la construction et elle n’est pas achevée!
17 Yanzu in sarki yana so, bari a duba cikin littattafan tarihi na sarakuna na Babilon a gani ko lalle sarki Sairus ya ba da umarni a sāke gina gidan Allah a Urushalima. Bari sarki yă aiko mana da abin da ya gani game da wannan abu.
Maintenant si tel est le bon plaisir du roi, qu’on recherche dans le dépôt des archives royales, là-bas, à Babylone, s’il est exact qu’un édit ait été rendu par le roi Cyrus, prescrivant de rebâtir ce temple de Dieu à Jérusalem; et que le roi nous communique sa volonté dans cette affaire!

< Ezra 5 >