< Ezra 5 >

1 Sai annabi Haggai, da annabi Zakariya zuriyar Iddo, suka yi wa Yahudawa a Yahuda da Urushalima annabci a cikin sunan Allah na Isra’ila wanda yake da mulki a kansu.
Forsothe Aggei, the prophete, and Zacharie, the prophete, the sone of Ado, prophesieden, prophesiynge in the name of God of Israel, to the Jewis that weren in Juda and Jerusalem.
2 Sa’an nan Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da Yeshuwa ɗan Yozadak suka yi shiri suka kama aikin sāke gina gidan Allah a Urushalima. Annabawan Allah kuwa suna tare da su, suna taimakonsu.
Thanne Zorobabel, the sone of Salatiel, and Josue, the sone of Josedech, risiden, and bigunnen to bilde the temple of God in Jerusalem; and with hem rysyden the prophetis of God, helpynge hem.
3 A wannan lokaci, Tattenai gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu suka je wurinsu suka tambaye su cewa, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali har ku gyara katangar?”
Forsothe in that tyme Tatannai, that was duyk biyende the flood, and Starbusannay, and the counselouris of hem, camen to hem, and seiden thus to hem, Who yaf counsel to you to bilde this hows, and to restore these wallis?
4 Suka kuma tambaye su “Ina sunayen waɗanda suke wannan gini?”
To which thing we answeriden to hem, whiche weren the names of men, autours of that bildyng.
5 Amma Allah yana tsaron dattawan Yahudawa, saboda haka ba a hana su aikin ba har sai rahoto ya kai wurin Dariyus aka kuma sami amsarsa a rubuce tukuna.
Forsothe the iye of God of hem was maad on the elde men of Jewis, and thei myyten not forbede the Jewis; and it pleside that the thing schulde be teld to Darius, and thanne thei schulden make satisfaccioun ayens that accusyng.
6 Ga wasiƙar da Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu masu riƙe da muƙamai a Kewayen Kogin Yuferites suka aika wa Sarki Dariyus.
This is the saumpler of the pistle, which Tathannai, duyk of the cuntrey biyende the flood, and Starbursannai, and hise counselouris, Arphasacei, that weren biyende the flood, senten to kyng Darius.
7 Ga rahoton da suka aika masa. Zuwa ga Sarki Dariyus. Gaisuwa da fatan alheri.
The word which thei senten to hym was writun thus; Al pees be to the kyng Darius.
8 Ya kamata sarki yă sani cewa mun je yankin Yahuda, zuwa gidan Allah mai girma. Muka ga mutanen suna ginin haikalin da manyan duwatsu, suna sa katakai a bangon. Ana aikin da ƙwazo, aikin kuma yana cin gaba sosai, suna kuma lura da shi.
Be it knowun to the kyng, that we yeden to the prouince of Judee, to the hows of greet God, which is bildid with stoon vnpolischid, and trees ben set in the wallis, and thilke werk is bildid diligently, and encreessith in the hondis of hem.
9 Mun tambayi dattawan muka ce musu, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali, ku kuma sāke gyara katangarsa?”
Therfor we axiden tho elde men, and thus we seiden to hem, Who yaf to you power to bilde this hows, and to restore these wallis?
10 Muka kuma tambaye su sunayensu don mu rubuta mu sanar da kai waɗanda suke shugabanninsu.
But also we axiden of hem the names `of hem, that we schulden telle to thee; and we han write the names of men, whiche thei ben, that ben princes among hem.
11 Wannan ita ce amsar da suka ba mu. “Mu bayin Allah na sama da ƙasa ne, muna sāke gina haikalin da aka gina tun shekaru da yawa da suka wuce, da wani babban sarkin Isra’ila ya gina ya kuma gama.
Sotheli thei answeriden bi sich word, and seiden, We ben the seruauntis of God of heuene and of erthe; and we bilden the temple that was bildid bifor these many yeeris, and `which temple the greet kyng of Israel `hadde bildid, and maad.
12 Amma domin kakanninmu sun ɓata wa Allah na sama rai, sai ya bari suka fāɗa cikin hannun Nebukadnezzar mutumin Kaldiya, sarkin Babilon, wanda ya rushe wannan haikali, ya kuma kwashe mutane zuwa Babilon.
But aftir that oure fadris stiryden God of heuene and of erthe to wrathfulnesse, bothe he bitook hem in the hond of Nabugodonosor, Caldey, kyng of Babiloyne; and he distriede this hows, and translatide the puple therof in to Babiloyne.
13 “Duk da haka, a shekara ta farko ta mulkin Sairus sarkin Babilon, Sarki Sairus ya ba da umarni cewa a sāke gina wannan gidan Allah.
Forsothe in the firste yeer of Cirus, king of Babiloyne, Cirus, the king of Babiloyne, settide forth `a comaundement, that the hows of God schulde be bildid.
14 Ya kuma kwashe kwanonin zinariya da azurfa na gidan Allah daga haikalin Babilon waɗanda Nebukadnezzar ya kwasa daga haikali a Urushalima. Sa’an nan sarki Sairus ya ba wa wani mutum mai suna Sheshbazzar umarni wanda ya sa ya zama gwamna,
For whi kyng Cirus brouyte forth `fro the temple of Babiloyne also the goldun and siluerne vessels of Goddis temple, whiche Nabugodonosor hadde take fro the temple, that was in Jerusalem, and hadde bore tho awei in to the temple of Babiloyne; and tho vessels weren youun to Sasabazar bi name, whom `he made also prince. And Cirus seide to hym, Take these vessels,
15 ya ce masa, ‘Ka kwashe kayan nan ka je ka zuba su a cikin haikalin Allah a Urushalima. Ka kuma sāke gina gidan Allah a wurin da yake a dā.’
and go, and sette tho in the temple, which is in Jerusalem; and the hows of God be bildid in `his place.
16 “Saboda haka Sheshbazzar ya so ya aza harsashin gina gidan Allah a Urushalima. Tun daga wancan lokaci har zuwa yau ana kan gina shi amma ba a gama ba.”
Therfor thanne thilke Sasabazar cam, and settide the foundementis of Goddis temple in Jerusalem; and fro that tyme `til to now it is bildid, and is not yit fillid.
17 Yanzu in sarki yana so, bari a duba cikin littattafan tarihi na sarakuna na Babilon a gani ko lalle sarki Sairus ya ba da umarni a sāke gina gidan Allah a Urushalima. Bari sarki yă aiko mana da abin da ya gani game da wannan abu.
Now therfor if it `semeth good to the king, rikene he in the biblet of the kyng, which is in Babiloyne, whether it be comaundid of kyng Cyrus, that Goddis hows schulde be bildid in Jerusalem; and sende he to vs the wille of the kyng `on this thing.

< Ezra 5 >