< Ezra 5 >

1 Sai annabi Haggai, da annabi Zakariya zuriyar Iddo, suka yi wa Yahudawa a Yahuda da Urushalima annabci a cikin sunan Allah na Isra’ila wanda yake da mulki a kansu.
Og Profeterne, Profeten Haggaj og Sakarias, Iddo's Søn, profeterede for Jøderne, som vare i Juda og Jerusalem, i Israels Guds Navn, som var over dem.
2 Sa’an nan Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da Yeshuwa ɗan Yozadak suka yi shiri suka kama aikin sāke gina gidan Allah a Urushalima. Annabawan Allah kuwa suna tare da su, suna taimakonsu.
Da gjorde Serubabel, Sealthiels Søn, og Jesua, Jozadaks Søn, sig rede og begyndte at bygge Guds Hus, som var i Jerusalem, og med dem de Guds Profeter, som styrkede dem.
3 A wannan lokaci, Tattenai gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu suka je wurinsu suka tambaye su cewa, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali har ku gyara katangar?”
Paa den Tid kom Thatnaj, Landshøvdingen paa denne Side Floden, og Sthar-Bosnaj og deres Selskab til dem og sagde til dem: Hvo har givet eder Befaling om at bygge dette Hus og at fuldføre denne Mur?
4 Suka kuma tambaye su “Ina sunayen waɗanda suke wannan gini?”
Da sagde vi altsaa til dem, hvad de Mænd hed, som byggede denne Bygning.
5 Amma Allah yana tsaron dattawan Yahudawa, saboda haka ba a hana su aikin ba har sai rahoto ya kai wurin Dariyus aka kuma sami amsarsa a rubuce tukuna.
Og over Jødernes Ældste var deres Guds Øje, og man forhindrede dem ikke, indtil der kom Befaling fra Darius, og man da sendte dem Brev tilbage derom.
6 Ga wasiƙar da Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu masu riƙe da muƙamai a Kewayen Kogin Yuferites suka aika wa Sarki Dariyus.
Afskriften af Brevet, som Thatnaj, Landshøvdingen paa denne Side Floden, og Sthar-Bosnaj og hans Selskab, de fra Afarsakta, som vare paa den Side Floden, sendte til Kong Darius; —
7 Ga rahoton da suka aika masa. Zuwa ga Sarki Dariyus. Gaisuwa da fatan alheri.
de sendte Beretningen til ham, og saaledes var der skrevet i den: Kong Darius ønske vi al Fred!
8 Ya kamata sarki yă sani cewa mun je yankin Yahuda, zuwa gidan Allah mai girma. Muka ga mutanen suna ginin haikalin da manyan duwatsu, suna sa katakai a bangon. Ana aikin da ƙwazo, aikin kuma yana cin gaba sosai, suna kuma lura da shi.
Det være Kongen vitterligt, at vi kom til det Landskab Juda, til den store Guds Hus, og at man bygger det med storø Stene og lægger Træ i Væggene, og at Arbejdet gaar rask frem og lykkes ved deres Hænder.
9 Mun tambayi dattawan muka ce musu, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali, ku kuma sāke gyara katangarsa?”
Da spurgte vi disse. Ældste ad og sagde saaledes til dem: Hvo har givet eder Befaling om at bygge dette Hus og at fuldføre denne Mur?
10 Muka kuma tambaye su sunayensu don mu rubuta mu sanar da kai waɗanda suke shugabanninsu.
Vi spurgte og om deres Navne for at give dig dem til Kende, at vi kunde skrive de Mænds Navne, som vare deres Øverster.
11 Wannan ita ce amsar da suka ba mu. “Mu bayin Allah na sama da ƙasa ne, muna sāke gina haikalin da aka gina tun shekaru da yawa da suka wuce, da wani babban sarkin Isra’ila ya gina ya kuma gama.
Og de gave os saadant Svar tilbage og sagde: Vi ere Himmelens og Jordens Guds Tjenere og bygge et Hus, som var fordum bygget, for mange Aar siden; thi en stor Konge i Israel havde bygget det og fuldført det.
12 Amma domin kakanninmu sun ɓata wa Allah na sama rai, sai ya bari suka fāɗa cikin hannun Nebukadnezzar mutumin Kaldiya, sarkin Babilon, wanda ya rushe wannan haikali, ya kuma kwashe mutane zuwa Babilon.
Men efterdi vore Fædre havde fortørnet Himmelens Gud, gav han dem i Kongen af Babel, Kaldæeren Nebukadnezars Haand, og denne nedbrød dette Hus og førte Folket bort til Babel.
13 “Duk da haka, a shekara ta farko ta mulkin Sairus sarkin Babilon, Sarki Sairus ya ba da umarni cewa a sāke gina wannan gidan Allah.
Men i Kongen af Babel, Kyrus's første Aar, gav Kong Kyrus Befaling at bygge dette Guds Hus.
14 Ya kuma kwashe kwanonin zinariya da azurfa na gidan Allah daga haikalin Babilon waɗanda Nebukadnezzar ya kwasa daga haikali a Urushalima. Sa’an nan sarki Sairus ya ba wa wani mutum mai suna Sheshbazzar umarni wanda ya sa ya zama gwamna,
Ja, ogsaa de Guds Hus's Kar, som vare af Guld og Sølv, hvilke Nebukadnezar havde udtaget af Templet, som var i Jerusalem, og ført til Templet i Babel, dem udtog Kong Kyrus af Templet i Babel, og de bleve givne en, hvis Navn var Sesbazar, hvilken han satte til Landshøvding.
15 ya ce masa, ‘Ka kwashe kayan nan ka je ka zuba su a cikin haikalin Allah a Urushalima. Ka kuma sāke gina gidan Allah a wurin da yake a dā.’
Og han sagde til ham: Tag disse Kar, gak bort og bring dem ind i Templet, som er i Jerusalem, og lad Guds Hus bygges paa sit Sted!
16 “Saboda haka Sheshbazzar ya so ya aza harsashin gina gidan Allah a Urushalima. Tun daga wancan lokaci har zuwa yau ana kan gina shi amma ba a gama ba.”
Da kom den samme Sesbazar, han lagde Grundvolden til Guds Hus, som er i Jerusalem; og fra da af og indtil nu bygges det og er ikke fuldført.
17 Yanzu in sarki yana so, bari a duba cikin littattafan tarihi na sarakuna na Babilon a gani ko lalle sarki Sairus ya ba da umarni a sāke gina gidan Allah a Urushalima. Bari sarki yă aiko mana da abin da ya gani game da wannan abu.
Og dersom det nu synes godt for Kongen, saa lad der blive eftersøgt i Kongens Skatkammer, som er i Babel, om det er saa, at der er given Befaling af Kong Kyrus om at bygge dette Guds Hus i Jerusalem, og man sende os Kongens Vilje derom!

< Ezra 5 >