< Ezra 4 >

1 Sa’ad da abokan gāban Yahuda da na Benyamin suka ji cewa waɗanda suka dawo daga bauta suna gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila
Or les ennemis de Juda et de Benjamin apprirent que les enfants de la captivité bâtissaient un temple au Seigneur Dieu d’Israël:
2 sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
Et s’approchant de Zorobabel et des princes des pères, ils leur dirent: Nous bâtirons avec vous, parce que, comme vous, nous cherchons votre Dieu: voilà que nous, nous avons immolé des victimes depuis les jours d’Asor-Haddan, roi d’Assur, qui nous amena ici.
3 Amma Zerubbabel, Yeshuwa, da sauran shugabannin iyalai na Isra’ila suka amsa suka ce, “Ba za ku sa hannu cikin gina wa Allahnmu haikali ba, mu kaɗai za mu gina wa Ubangiji, Allah na Isra’ila gini kamar yadda Sarki Sairus, sarkin Farisa, ya umarce mu.”
Zorobabel leur répondit, ainsi que Josué et tous les autres princes des pères d’Israël: Ce n’est pas à vous et à nous de bâtir ensemble une maison à notre Dieu; mais nous seuls nous bâtirons au Seigneur notre Dieu, comme nous l’a ordonné Cyrus, roi des Perses.
4 Sai mutanen da suke zama a wurin suka fara yin ƙoƙari su sa mutanen Yahuda su karaya, suka sa su ji tsoron ci gaba da ginin.
Il arriva donc que le peuple du pays empêchait les mains du peuple de Juda, et le troublait pendant qu’il bâtissait.
5 Suka yi hayar mashawarta don su ga cewa sun ɓata ƙoƙarinsu dukan kwanakin mulkin Sairus sarkin Farisa har zuwa kwanakin mulkin Dariyus sarkin Farisa.
Ensuite on gagna contre eux des conseillers, pour détruire leur dessein durant les jours de Cyrus, roi des Perses, et jusqu’au règne de Darius, roi des Perses.
6 A farkon mulkin Zerzes, sai abokan gāba suka kawo ƙarar mutanen Yahuda da na Urushalima.
Or, sous le règne d’Assuérus, et au commencement de son règne, ils écrivirent une accusation contre les habitants de Juda et de Jérusalem;
7 A zamanin Artazerzes sarkin Farisa kuma, sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da sauran abokansu suka rubuta wasiƙa zuwa ga Artazerzes. Aka rubuta wasiƙar da harufan Arameyik, aka kuma fassara ta a yaren Arameyik.
Et aux jours d’Artaxerxès, Bésélam-Mithridate et Thabéel et les autres qui étaient dans leur conseil, écrivirent à Artaxerxès, roi des Perses: or la lettre d’accusation était écrite en syriaque, et on la lisait en la langue de Syrie.
8 Rehum shugaban rundunar soja, da Shimshai marubuci, suka rubuta wasiƙar a kan Urushalima zuwa ga sarki Artazerzes, suka ce.
Réum-Béeltéem et Samsaï, le scribe, écrivirent une lettre de Jérusalem au roi Artaxerxès, en ces termes:
9 Rehum shugaban sojoji, da Shimshai marubuci, da sauran abokansu, wato, alƙalai, da masu riƙe da muƙamai daga Farisa, Uruk da Babilon, mutanen Elam da na Shusha,
Réum-Béeltéem et Samsaï, le scribe, et leurs autres conseillers, Dinéens, Apharsathachéens, Therphaléens, Apharséens, Erchuéens, Babyloniens, Susanéchéens, Diévéens, et Elamites,
10 da sauran mutane waɗanda mai girma Osnaffar ya kwaso, ya zaunar da su cikin birnin Samariya da sauran wurare na Kewayen Kogin Yuferites.
Et tous les autres des nations qu’a transportées Asénaphar, le grand et le glorieux, et qu’il a fait habiter en paix dans les villes de Samarie et dans les autres contrées au-delà du fleuve.
11 (Ga abin da suka rubuta.) Zuwa ga sarki Artazerzes. Daga bayinka, mutanen Kewayen Kogin Yuferites.
(Voici la copie de la lettre qu’ils lui envoyèrent): À Artaxerxès roi, vos serviteurs, les hommes qui sont au-delà du fleuve, disent salut.
12 Ya kamata sarki ya san cewa Yahudawan da suka hauro wurinmu daga wurinka, sun je Urushalima suna sāke gina wannan mugun birni mai tawaye. Suna sāke gyara katangar, suna kuma gyara harsashin katangar.
Qu’il soit connu du roi que les Juifs qui sont montés de chez vous vers nous, sont venus à Jérusalem, ville rebelle et très méchante, qu’ils bâtissent, construisant ses murs et rétablissant les maisons.
13 Ya kamata fa, sarki ya san cewa in aka sāke gina wannan birni duk da katangar birnin, mutanen birnin ba za su dinga biyan haraji, da kuɗin shiga, da na fitar da kaya ba, wannan zai sa aljihun masarauta yă bushe.
Maintenant donc, qu’il soit connu du roi que si cette ville est bâtie et ses murs restaurés, ils ne payeront ni tribut, ni impôt, ni revenus annuels; et cette perte retombera jusque sur le roi.
14 Tun da yake muna ƙarƙashin fada, bai kyautu mu bari a rena sarki ba, Saboda haka muke sanar da sarki,
Or, nous souvenant du sel que nous avons mangé dans le palais, et parce que nous regardons comme un crime les offenses faites au roi, c’est pourquoi nous avons envoyé, et nous avons averti le roi,
15 domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka ga cewa wannan birni mai tawaye ne. Tun daga zamanin dā wannan birnin yana ba sarakuna da yankuna damuwa. Wannan ne ya sa aka ragargazar da birnin.
Afin que vous regardiez dans les livres des histoires de vos pères; car vous trouverez écrit dans les annales, et vous apprendrez que cette ville est une ville rebelle et funeste aux rois et aux provinces, et que des guerres sont fomentées en elle depuis les jours anciens: c’est pourquoi la cité elle-même a été détruite.
16 Muna sanar da sarki cewa in har aka sāke gina wannan birnin da katangarsa, zai zama ka rasa kome a gefen Kewayen Kogin Yuferites ke nan.
Nous annonçons donc au roi que, si cette ville est rebâtie et ses murs restaurés, vous n’aurez pas de possession au-delà du fleuve.
17 Sarki ya aika da wannan amsa. Zuwa ga Rehum shugaban sojoji, Shimshai marubuci da kuma sauran abokansu waɗanda suke zama a Samariya da kuma sauran wurare a Kewayen Kogin Yuferites. Gaisuwa.
Le roi envoya une réponse à Réum-Béeltéem, et à Samsaï, le scribe, aux autres habitants de Samarie qui étaient dans leur conseil, et à tous ceux d’au-delà du fleuve, disant salut et paix.
18 An karanta, an kuma fassara mini wasiƙar da kuma aika.
L’accusation que vous nous avez envoyée a été lue clairement devant moi,
19 Na ba da umarni aka kuma yi bincike, aka tarar cewa wannan birni ya daɗe yana yi wa sarakuna tawaye, an yi tashin hankali a birnin.
Et il a été ordonné par moi, et on a examiné, et on a trouvé que cette ville, depuis les jours anciens, se révolte contre les rois, et que les séditions et les guerres sont fomentées en elle;
20 Urushalima ta yi sarakuna masu iko sosai waɗanda suka yi mulkin Kewayen Kogin Yuferites gaba ɗaya, an kuma biya masu haraji, da kuɗin shiga da na fita na kaya.
Car il y a eu aussi des rois très puissants à Jérusalem, qui ont même dominé sur toute la contrée qui est au-delà du fleuve; ils recevaient un tribut, un impôt et des revenus.
21 Saboda haka sai ku ba da umarni yanzu cewa mutanen su daina wannan aiki sai lokacin da na ba da umarni.
Maintenant donc, écoutez ma décision: Empêchez ces hommes, afin que cette ville ne soit pas bâtie, jusqu’à ce que cela ait été commandé par moi.
22 Ku tabbata ka ɗauki wannan da muhimmanci. Don me za a bari wannan abu yă zama abin damuwa ga sarauta?
Prenez garde de remplir cet ordre avec négligence, et que peu à peu le mal ne s’accroisse contre les rois.
23 Da gama karanta wasiƙar sarki Artazerzes wa Rehum da Shimshai marubuci, da abokansu, sai suka yi sauri suka je wurin Yahudawa a Urushalima, suka hana su aikin ƙarfi da yaji.
C’est pourquoi la copie de l’édit du roi Artaxerxès fut lue devant Réum-Béeltéem et Samsaï, le scribe, et leurs conseillers; et ils allèrent en grande hâte à Jérusalem vers les Juifs, et les repoussèrent avec un bras fort.
24 Saboda haka aikin a gidan Allah a Urushalima ya tsaya cik sai a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus sarkin Farisa.
Alors fut interrompu l’ouvrage de la maison du Seigneur à Jérusalem, et l’on n’y travailla pas jusqu’à la seconde année du règne de Darius, roi des Perses.

< Ezra 4 >