< Ezra 4 >

1 Sa’ad da abokan gāban Yahuda da na Benyamin suka ji cewa waɗanda suka dawo daga bauta suna gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila
Les adversaires de Juda et de Benjamin, ayant appris que les Israélites revenus de l’exil bâtissaient un sanctuaire à l’Eternel, Dieu d’Israël,
2 sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
se présentèrent à Zorobabel et aux chefs des familles et leur dirent: "Nous voulons bâtir de concert avec vous, car, comme vous, nous recherchons votre Dieu, et c’est à lui que nous offrons des sacrifices depuis les jours d’Essar-Haddôn, roi d’Assyrie, qui nous a transportés ici."
3 Amma Zerubbabel, Yeshuwa, da sauran shugabannin iyalai na Isra’ila suka amsa suka ce, “Ba za ku sa hannu cikin gina wa Allahnmu haikali ba, mu kaɗai za mu gina wa Ubangiji, Allah na Isra’ila gini kamar yadda Sarki Sairus, sarkin Farisa, ya umarce mu.”
Zorobabel, Yêchoua et les autres chefs des familles d’Israël leur répondirent: "Il ne vous appartient pas de construire avec nous une maison à notre Dieu: nous seuls, tant que nous sommes, nous voulons faire la construction en l’honneur de l’Eternel, Dieu d’Israël, ainsi que nous l’a ordonné Cyrus, roi de Perse."
4 Sai mutanen da suke zama a wurin suka fara yin ƙoƙari su sa mutanen Yahuda su karaya, suka sa su ji tsoron ci gaba da ginin.
Alors la population du pays s’appliqua à décourager les habitants de la Judée et à les détourner de bâtir en les intimidant.
5 Suka yi hayar mashawarta don su ga cewa sun ɓata ƙoƙarinsu dukan kwanakin mulkin Sairus sarkin Farisa har zuwa kwanakin mulkin Dariyus sarkin Farisa.
De plus, ils soudoyaient contre eux des personnages influents pour entraver leur projet, tant que vécut Cyrus, roi de Perse, et jusqu’au règne de Darius, roi de Perse.
6 A farkon mulkin Zerzes, sai abokan gāba suka kawo ƙarar mutanen Yahuda da na Urushalima.
Sous le règne d’Assuérus, dès le début de son règne, ils envoyèrent une accusation écrite contre les habitants de Juda et de Jérusalem.
7 A zamanin Artazerzes sarkin Farisa kuma, sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da sauran abokansu suka rubuta wasiƙa zuwa ga Artazerzes. Aka rubuta wasiƙar da harufan Arameyik, aka kuma fassara ta a yaren Arameyik.
Puis, au temps d’Artahchasta, Bichlâm, Mithridate, Tabeêl et consorts écrivirent à Artahchasta, roi de Perse, et la teneur de la missive était écrite en caractères araméens et traduite en araméen.
8 Rehum shugaban rundunar soja, da Shimshai marubuci, suka rubuta wasiƙar a kan Urushalima zuwa ga sarki Artazerzes, suka ce.
Rehoum, le conseiller, et Chimchaï, le scribe, écrivirent au roi Artahchasta une lettre au sujet de Jérusalem, conçue en ces termes:
9 Rehum shugaban sojoji, da Shimshai marubuci, da sauran abokansu, wato, alƙalai, da masu riƙe da muƙamai daga Farisa, Uruk da Babilon, mutanen Elam da na Shusha,
"A cette heure, Rehoum, le conseiller, Chimchaï, le scribe, et consorts; les Dinéens, Afarsatkéens, Tarpeléens, Afarséens, Arkavéens, Babyloniens, Chouchankéens, Déhavéens et Elamites,
10 da sauran mutane waɗanda mai girma Osnaffar ya kwaso, ya zaunar da su cikin birnin Samariya da sauran wurare na Kewayen Kogin Yuferites.
et les autres peuplades que Asnappar le grand et le glorieux a déportés et établis dans la ville de Samarie et d’autres territoires en deçà du fleuve, et ainsi de suite.
11 (Ga abin da suka rubuta.) Zuwa ga sarki Artazerzes. Daga bayinka, mutanen Kewayen Kogin Yuferites.
Voici le contenu de la lettre qu’ils ont envoyée au roi Artahchasta: Tes serviteurs, les gens des territoires situés en deçà du fleuve et ainsi de suite.
12 Ya kamata sarki ya san cewa Yahudawan da suka hauro wurinmu daga wurinka, sun je Urushalima suna sāke gina wannan mugun birni mai tawaye. Suna sāke gyara katangar, suna kuma gyara harsashin katangar.
Que le roi sache que les Judéens qui sont partis de chez toi sont arrivés près de chez nous à Jérusalem. Ils rebâtissent cette ville rebelle et mauvaise, réparent les murailles et creusent les fondations.
13 Ya kamata fa, sarki ya san cewa in aka sāke gina wannan birni duk da katangar birnin, mutanen birnin ba za su dinga biyan haraji, da kuɗin shiga, da na fitar da kaya ba, wannan zai sa aljihun masarauta yă bushe.
Que le roi sache donc que, si cette ville est rebâtie et les murailles réparées, ils ne paieront plus ni tribut, ni impôts, ni péage, ce qui portera préjudice au trésor royal.
14 Tun da yake muna ƙarƙashin fada, bai kyautu mu bari a rena sarki ba, Saboda haka muke sanar da sarki,
Puisque donc nous mangeons le sel du palais, et qu’il ne nous sied pas d’être témoins du tort fait au roi, nous mandons ceci au roi et l’en instruisons,
15 domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka ga cewa wannan birni mai tawaye ne. Tun daga zamanin dā wannan birnin yana ba sarakuna da yankuna damuwa. Wannan ne ya sa aka ragargazar da birnin.
aux seules fins qu’on fasse des recherches dans les archives de tes ancêtres. Tu trouveras dans ces archives et t’assureras que cette cité est une cité rebelle et funeste aux rois et aux provinces, qu’on y a fomenté des révoltes dès les temps antiques, ce qui a causé la destruction de cette cité.
16 Muna sanar da sarki cewa in har aka sāke gina wannan birnin da katangarsa, zai zama ka rasa kome a gefen Kewayen Kogin Yuferites ke nan.
Nous faisons savoir au roi que, si cette cité est rebâtie et ses murailles rétablies, la conséquence sera que tu n’auras plus de part au pays en deçà du fleuve."
17 Sarki ya aika da wannan amsa. Zuwa ga Rehum shugaban sojoji, Shimshai marubuci da kuma sauran abokansu waɗanda suke zama a Samariya da kuma sauran wurare a Kewayen Kogin Yuferites. Gaisuwa.
Le roi fit parvenir la notification suivante à Rehoum, le conseiller, Chimchaï, le scribe, et consorts, établis à Samarie et dans les autres territoires en deçà du fleuve: "Salut, etc!
18 An karanta, an kuma fassara mini wasiƙar da kuma aika.
La missive que vous nous avez envoyée a été lue distinctement devant moi.
19 Na ba da umarni aka kuma yi bincike, aka tarar cewa wannan birni ya daɗe yana yi wa sarakuna tawaye, an yi tashin hankali a birnin.
Sur l’ordre que j’en ai donné, on a fait des recherches, et on a constaté que cette cité, dès les temps antiques, s’est insurgée contre les rois, et qu’on y a fomenté des révoltes et des séditions.
20 Urushalima ta yi sarakuna masu iko sosai waɗanda suka yi mulkin Kewayen Kogin Yuferites gaba ɗaya, an kuma biya masu haraji, da kuɗin shiga da na fita na kaya.
Des rois puissants ont régné à Jérusalem, qui étendaient leur domination sur toute la contrée de l’autre côté du fleuve, et à qui l’on payait des tributs, des impôts et des péages.
21 Saboda haka sai ku ba da umarni yanzu cewa mutanen su daina wannan aiki sai lokacin da na ba da umarni.
Prenez donc des dispositions pour paralyser ces gens, afin que cette ville ne soit pas rebâtie jusqu’à nouvel ordre de ma part.
22 Ku tabbata ka ɗauki wannan da muhimmanci. Don me za a bari wannan abu yă zama abin damuwa ga sarauta?
Et soyez sur vos gardes pour éviter toute négligence en cette affaire: pourquoi laisser s’aggraver le mal au détriment des rois?"
23 Da gama karanta wasiƙar sarki Artazerzes wa Rehum da Shimshai marubuci, da abokansu, sai suka yi sauri suka je wurin Yahudawa a Urushalima, suka hana su aikin ƙarfi da yaji.
Aussitôt que le contenu de la lettre d’Artahchasta eut été lu devant Rehoum, Chimchaï, le scribe, et consorts, ils se rendirent en toute hâte à Jérusalem auprès des Judéens et les réduisirent à l’inaction, en employant la force et la violence.
24 Saboda haka aikin a gidan Allah a Urushalima ya tsaya cik sai a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus sarkin Farisa.
Dès lors, les travaux du temple de Dieu, à Jérusalem, furent arrêtés jusqu’à la deuxième année du règne de Darius, roi de Perse.

< Ezra 4 >