< Ezra 4 >

1 Sa’ad da abokan gāban Yahuda da na Benyamin suka ji cewa waɗanda suka dawo daga bauta suna gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila
The enemies of the people of [the tribes of] Judah and Benjamin heard that the [Israeli] people who had returned from Babylonia were rebuilding a temple for Yahweh, the God whom the Israeli people [worshiped].
2 sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
So they went to Zerubbabel [the governor] and the other leaders, and said [deceptively], “We want to help [you build the temple], because we worship that same God whom you worship, and we have been offering sacrifices to him since Esarhaddon, the King of Assyria, brought us here.”
3 Amma Zerubbabel, Yeshuwa, da sauran shugabannin iyalai na Isra’ila suka amsa suka ce, “Ba za ku sa hannu cikin gina wa Allahnmu haikali ba, mu kaɗai za mu gina wa Ubangiji, Allah na Isra’ila gini kamar yadda Sarki Sairus, sarkin Farisa, ya umarce mu.”
But Zerubbabel, Jeshua, and the other [Israeli] leaders replied, “We will not allow you to help us build a temple for our(exc) God. We will build it (ourselves/without your help) for Yahweh, the God whom we Israelis worship, like Cyrus, the King of Persia, told us to do.”
4 Sai mutanen da suke zama a wurin suka fara yin ƙoƙari su sa mutanen Yahuda su karaya, suka sa su ji tsoron ci gaba da ginin.
Then the people who had been living in that land [before the Israelis returned] tried to cause the Jews to become discouraged and become afraid, and to cause them to stop building the temple.
5 Suka yi hayar mashawarta don su ga cewa sun ɓata ƙoƙarinsu dukan kwanakin mulkin Sairus sarkin Farisa har zuwa kwanakin mulkin Dariyus sarkin Farisa.
They bribed government officials to oppose what the Israelis were doing [and prevent them from continuing to work on the temple]. They did that all during the time that Cyrus was King of Persia. They continued to do it when Darius became the King of Persia.
6 A farkon mulkin Zerzes, sai abokan gāba suka kawo ƙarar mutanen Yahuda da na Urushalima.
During the first year that [Darius’ son] Xerxes was king, the [enemies of the Jews] wrote a note [to the king] saying that the Jews [were planning to rebel against the government].
7 A zamanin Artazerzes sarkin Farisa kuma, sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da sauran abokansu suka rubuta wasiƙa zuwa ga Artazerzes. Aka rubuta wasiƙar da harufan Arameyik, aka kuma fassara ta a yaren Arameyik.
Later, when [Xerxes’ son] Artaxerxes [became the King of Persia], Bishlam, Mithredath, Tabeel and their colleagues/companions wrote a letter to him. They wrote the letter in the Aramaic language, and it was translated [into another language that the king knew].
8 Rehum shugaban rundunar soja, da Shimshai marubuci, suka rubuta wasiƙar a kan Urushalima zuwa ga sarki Artazerzes, suka ce.
Rehum, the high commissioner, and Shimshai, the provincial secretary, wrote the letter to King Artaxerxes concerning what was happening in Jerusalem.
9 Rehum shugaban sojoji, da Shimshai marubuci, da sauran abokansu, wato, alƙalai, da masu riƙe da muƙamai daga Farisa, Uruk da Babilon, mutanen Elam da na Shusha,
They stated that the letter was from Rehum the high commissioner/governor and Shimshai the provincial secretary and from their associates, the judges, and other government officials, who were from Erech [city], Babylon [city], and Susa [city] in Elam [district].
10 da sauran mutane waɗanda mai girma Osnaffar ya kwaso, ya zaunar da su cikin birnin Samariya da sauran wurare na Kewayen Kogin Yuferites.
[They also wrote that they represented] the other people-groups whom [the army of] the great and glorious/famous [King] Ashurbanipal had (deported/forced to move from their homes) and taken to live in Samaria and in other cities in the province west of the Euphrates [River].
11 (Ga abin da suka rubuta.) Zuwa ga sarki Artazerzes. Daga bayinka, mutanen Kewayen Kogin Yuferites.
This is what they wrote in the letter: “To King Artaxerxes, From the officials who serve you who live in the province west of the Euphrates [River.]
12 Ya kamata sarki ya san cewa Yahudawan da suka hauro wurinmu daga wurinka, sun je Urushalima suna sāke gina wannan mugun birni mai tawaye. Suna sāke gyara katangar, suna kuma gyara harsashin katangar.
“Your majesty, we want you to know that the Jews who came here from your territories are rebuilding this city, [Jerusalem]. These people are wicked and want to rebel against you. Now they are repairing the foundations [of the walls/buildings] and building the walls [of the city].
13 Ya kamata fa, sarki ya san cewa in aka sāke gina wannan birni duk da katangar birnin, mutanen birnin ba za su dinga biyan haraji, da kuɗin shiga, da na fitar da kaya ba, wannan zai sa aljihun masarauta yă bushe.
“It is important for you to know that if they rebuild the city and finish building the walls, they will stop paying any kind of taxes. As a result, there will be less money in your treasury.
14 Tun da yake muna ƙarƙashin fada, bai kyautu mu bari a rena sarki ba, Saboda haka muke sanar da sarki,
Now, because we are loyal to [IDM] you, and because we do not want you to be humiliated [IDM], we are sending this information to you.
15 domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka ga cewa wannan birni mai tawaye ne. Tun daga zamanin dā wannan birnin yana ba sarakuna da yankuna damuwa. Wannan ne ya sa aka ragargazar da birnin.
And, we suggest that you order/tell [your officials] to search the records that your ancestors made/wrote. [If you do that], you will find out that the people in this city have always rebelled [against the government]. You will also find out that from long ago these people have caused trouble for kings and for rulers of provinces. They have always revolted [against those who ruled them]. That is the reason that this city was destroyed [by the Babylonian army].
16 Muna sanar da sarki cewa in har aka sāke gina wannan birnin da katangarsa, zai zama ka rasa kome a gefen Kewayen Kogin Yuferites ke nan.
We want you to know that if they rebuild this city and finish building its walls, you will no longer be able to control/rule [the people in] this province west of the Euphrates [River].”
17 Sarki ya aika da wannan amsa. Zuwa ga Rehum shugaban sojoji, Shimshai marubuci da kuma sauran abokansu waɗanda suke zama a Samariya da kuma sauran wurare a Kewayen Kogin Yuferites. Gaisuwa.
[After] the king [read this letter, he] sent this reply to them: “To Rehum, the high commissioner, and Shimshai, the provincial secretary, and their colleagues in Samaria and in other parts of the province that is west of the [Euphrates] River: I (send you my greetings/wish that things will go well for you).
18 An karanta, an kuma fassara mini wasiƙar da kuma aika.
The letter that you sent to me was translated and read to me.
19 Na ba da umarni aka kuma yi bincike, aka tarar cewa wannan birni ya daɗe yana yi wa sarakuna tawaye, an yi tashin hankali a birnin.
So then I ordered [my officials] to search the records. I have found out that [it is true that] the people of that city have always revolted against their rulers, and that the city is full of people who have rebelled and caused trouble.
20 Urushalima ta yi sarakuna masu iko sosai waɗanda suka yi mulkin Kewayen Kogin Yuferites gaba ɗaya, an kuma biya masu haraji, da kuɗin shiga da na fita na kaya.
Powerful kings have ruled in Jerusalem, and they have also ruled over the whole province west of the [Euphrates] River. [The people in that province were] paying all kinds of taxes to those kings.
21 Saboda haka sai ku ba da umarni yanzu cewa mutanen su daina wannan aiki sai lokacin da na ba da umarni.
So you must command that the people must stop rebuilding the city. Only if I tell them [that they may rebuild it] will they be allowed to continue.
22 Ku tabbata ka ɗauki wannan da muhimmanci. Don me za a bari wannan abu yă zama abin damuwa ga sarauta?
Do this immediately [LIT], because I do not want those people to do anything to harm the things/area about which I am concerned.”
23 Da gama karanta wasiƙar sarki Artazerzes wa Rehum da Shimshai marubuci, da abokansu, sai suka yi sauri suka je wurin Yahudawa a Urushalima, suka hana su aikin ƙarfi da yaji.
[Messengers took] that letter to Rehum and Shimshai and their colleagues and read it to them. Then Rehum and the others went quickly to Jerusalem, and they forced the Jews to stop [rebuilding the city wall].
24 Saboda haka aikin a gidan Allah a Urushalima ya tsaya cik sai a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus sarkin Farisa.
The result was that the Jews stopped rebuilding the temple. They did not do any more work to rebuild the temple until Darius became the King of Persia.

< Ezra 4 >