< Ezra 4 >
1 Sa’ad da abokan gāban Yahuda da na Benyamin suka ji cewa waɗanda suka dawo daga bauta suna gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila
And they heard [the] opponents of Judah and Benjamin that [the] children of the exile [were] building a temple for Yahweh [the] God of Israel.
2 sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
And they approached Zerubbabel and [the] heads of the fathers and they said to them let us build with you for like you we seek God your (and to him *Q(K)*) we [have been] sacrificing since [the] days of Esar-haddon [the] king of Assyria who brought up us here.
3 Amma Zerubbabel, Yeshuwa, da sauran shugabannin iyalai na Isra’ila suka amsa suka ce, “Ba za ku sa hannu cikin gina wa Allahnmu haikali ba, mu kaɗai za mu gina wa Ubangiji, Allah na Isra’ila gini kamar yadda Sarki Sairus, sarkin Farisa, ya umarce mu.”
And he said to them Zerubbabel and Jeshua and [the] rest of [the] heads of the fathers of Israel not for you and for us to build a house for God our for we together we will build [it] for Yahweh [the] God of Israel just as he commanded us the king Cyrus [the] king of Persia.
4 Sai mutanen da suke zama a wurin suka fara yin ƙoƙari su sa mutanen Yahuda su karaya, suka sa su ji tsoron ci gaba da ginin.
And it was [the] people of the land [were] making slack [the] hands of [the] people of Judah (and [were] terrifying *Q(K)*) them to build.
5 Suka yi hayar mashawarta don su ga cewa sun ɓata ƙoƙarinsu dukan kwanakin mulkin Sairus sarkin Farisa har zuwa kwanakin mulkin Dariyus sarkin Farisa.
And [were] hiring on them counselors to frustrate purpose their all [the] days of Cyrus [the] king of Persia and until [the] reign of Darius [the] king of Persia.
6 A farkon mulkin Zerzes, sai abokan gāba suka kawo ƙarar mutanen Yahuda da na Urushalima.
And in [the] reign of Ahasuerus at [the] beginning of reign his they wrote an accusation on [the] inhabitants of Judah and Jerusalem.
7 A zamanin Artazerzes sarkin Farisa kuma, sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da sauran abokansu suka rubuta wasiƙa zuwa ga Artazerzes. Aka rubuta wasiƙar da harufan Arameyik, aka kuma fassara ta a yaren Arameyik.
And in [the] days of Artaxerxes he wrote Bishlam Mithredath Tabeel and [the] rest of (colleagues his *Q(K)*) to (Artaxerxes *Q(k)*) [the] king of Persia and [the] writing of the letter [was] written Aramaic and [was] translated Aramaic.
8 Rehum shugaban rundunar soja, da Shimshai marubuci, suka rubuta wasiƙar a kan Urushalima zuwa ga sarki Artazerzes, suka ce.
Rehum lord of command and Shimshai scribe the they wrote a letter one concerning Jerusalem to Artaxerxes king the as follows.
9 Rehum shugaban sojoji, da Shimshai marubuci, da sauran abokansu, wato, alƙalai, da masu riƙe da muƙamai daga Farisa, Uruk da Babilon, mutanen Elam da na Shusha,
Then Rehum lord of command and Shimshai scribe the and [the] rest of associates their Dinay the and officials the Tarpelites the Sipparites the (Erechites the *Q(K)*) Babylonians the Susanchites the (Dehavites the *Q(K)*) Elamites the.
10 da sauran mutane waɗanda mai girma Osnaffar ya kwaso, ya zaunar da su cikin birnin Samariya da sauran wurare na Kewayen Kogin Yuferites.
And [the] rest of nations the which he took into exile Osnappar great and honorable and he caused to dwell them in [the] city of Samaria and [the] rest of [the] region beyond river the and now.
11 (Ga abin da suka rubuta.) Zuwa ga sarki Artazerzes. Daga bayinka, mutanen Kewayen Kogin Yuferites.
This [is] [the] copy of letter the which they sent to him to Artaxerxes king the (servant your *Q(K)*) [the] man of [the] region beyond river the and now.
12 Ya kamata sarki ya san cewa Yahudawan da suka hauro wurinmu daga wurinka, sun je Urushalima suna sāke gina wannan mugun birni mai tawaye. Suna sāke gyara katangar, suna kuma gyara harsashin katangar.
Known let it be to king the that Jews the who they came up from beside you to us they have come to Jerusalem city the rebellious (and evil *Q(k)*) [they are] building (and walls the they have finished *Q(K)*) and foundations the they are repairing.
13 Ya kamata fa, sarki ya san cewa in aka sāke gina wannan birni duk da katangar birnin, mutanen birnin ba za su dinga biyan haraji, da kuɗin shiga, da na fitar da kaya ba, wannan zai sa aljihun masarauta yă bushe.
Now known let it be to king the that if city the this it will be built and walls the they will be finished tribute tax and toll not they will give and certainly kings it will injure.
14 Tun da yake muna ƙarƙashin fada, bai kyautu mu bari a rena sarki ba, Saboda haka muke sanar da sarki,
Now as to because that [the] salt of palace the we eat salt and [the] dishonor of king the not ([is] proper *LB(ah)*) for us to see concerning this we have sent and we have made known to king the.
15 domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka ga cewa wannan birni mai tawaye ne. Tun daga zamanin dā wannan birnin yana ba sarakuna da yankuna damuwa. Wannan ne ya sa aka ragargazar da birnin.
That he will search in [the] book of records the of fathers your so you may find in [the] book of records the so you may know that city the this [is] a city rebellious and injuring kings and provinces and a revolt [it was] making in midst its from [the] days of antiquity on this city the this it was laid waste.
16 Muna sanar da sarki cewa in har aka sāke gina wannan birnin da katangarsa, zai zama ka rasa kome a gefen Kewayen Kogin Yuferites ke nan.
[are] making known We to king the that if city the this it will be built and walls the they will be finished before this possession in [the] region beyond river the not there [will be] to you.
17 Sarki ya aika da wannan amsa. Zuwa ga Rehum shugaban sojoji, Shimshai marubuci da kuma sauran abokansu waɗanda suke zama a Samariya da kuma sauran wurare a Kewayen Kogin Yuferites. Gaisuwa.
Word the he sent king the to Rehum lord of command and Shimshai scribe the and [the] rest of associates their who [were] dwelling in Samaria and [the] rest of [the] region beyond river the peace and now.
18 An karanta, an kuma fassara mini wasiƙar da kuma aika.
Letter the which you sent to us made distinct it was read aloud before me.
19 Na ba da umarni aka kuma yi bincike, aka tarar cewa wannan birni ya daɗe yana yi wa sarakuna tawaye, an yi tashin hankali a birnin.
And from me it was made a decree and they searched and they found that city the this from [the] days of antiquity against kings [was] rising up and rebellion and revolt [have] been done by it.
20 Urushalima ta yi sarakuna masu iko sosai waɗanda suka yi mulkin Kewayen Kogin Yuferites gaba ɗaya, an kuma biya masu haraji, da kuɗin shiga da na fita na kaya.
And kings strong they were over Jerusalem and having mastery over all [the] region beyond river the and tribute tax and toll [was] being paid to them.
21 Saboda haka sai ku ba da umarni yanzu cewa mutanen su daina wannan aiki sai lokacin da na ba da umarni.
Now make a decree to make to cease men the these and city the this not it will be built until from me decree the it will be made.
22 Ku tabbata ka ɗauki wannan da muhimmanci. Don me za a bari wannan abu yă zama abin damuwa ga sarauta?
And cautious be negligence to do concerning this why? will it grow great damage the to injury kings.
23 Da gama karanta wasiƙar sarki Artazerzes wa Rehum da Shimshai marubuci, da abokansu, sai suka yi sauri suka je wurin Yahudawa a Urushalima, suka hana su aikin ƙarfi da yaji.
Then from that [the] copy of letter the of (Artaxerxes *Q(k)*) king the it was read aloud before Rehum and Shimshai scribe the and associates their they went in haste to Jerusalem to Jews the and they made to cease them with force and power.
24 Saboda haka aikin a gidan Allah a Urushalima ya tsaya cik sai a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus sarkin Farisa.
Then it ceased [the] work of [the] house of God which [is] in Jerusalem and it was ceasing until year two of [the] reign of Darius [the] king of Persia.