< Ezra 4 >
1 Sa’ad da abokan gāban Yahuda da na Benyamin suka ji cewa waɗanda suka dawo daga bauta suna gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila
Now, when the adversaries of Judah and Benjamin heard—that, the Sons of the Exile, were building the temple, unto Yahweh, God of Israel,
2 sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
then drew they near unto Zerubbabel, and unto the ancestral chiefs, and said unto them, Let us build with you, for, like you, we seek your God, and, unto him, have, we, been sacrificing since the days of Esar-haddon, king of Assyria, who brought us up hither.
3 Amma Zerubbabel, Yeshuwa, da sauran shugabannin iyalai na Isra’ila suka amsa suka ce, “Ba za ku sa hannu cikin gina wa Allahnmu haikali ba, mu kaɗai za mu gina wa Ubangiji, Allah na Isra’ila gini kamar yadda Sarki Sairus, sarkin Farisa, ya umarce mu.”
But Zerubbabel and Jeshua and the rest of the ancestral chiefs of Israel, said unto them, It pertaineth not to you and to us [in common], to build a house unto our God, —but, we ourselves together, will build unto Yahweh, God of Israel, even as King Cyrus, king of Persia, hath commanded us.
4 Sai mutanen da suke zama a wurin suka fara yin ƙoƙari su sa mutanen Yahuda su karaya, suka sa su ji tsoron ci gaba da ginin.
Then came it to pass, that, the people of the land, were weakening the hands of the people of Judah, —and troubling them in building;
5 Suka yi hayar mashawarta don su ga cewa sun ɓata ƙoƙarinsu dukan kwanakin mulkin Sairus sarkin Farisa har zuwa kwanakin mulkin Dariyus sarkin Farisa.
and hiring against them counselors, to overturn their purpose, —all the days of Cyrus, king of Persia, even until the reign of Darius, king of Persia.
6 A farkon mulkin Zerzes, sai abokan gāba suka kawo ƙarar mutanen Yahuda da na Urushalima.
And, in the reign of Ahasuerus, in the beginning of his reign, wrote they an accusation, against the inhabitants of Judah and Jerusalem.
7 A zamanin Artazerzes sarkin Farisa kuma, sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da sauran abokansu suka rubuta wasiƙa zuwa ga Artazerzes. Aka rubuta wasiƙar da harufan Arameyik, aka kuma fassara ta a yaren Arameyik.
And, in the days of Artaxerxes, wrote Bishlam, Mithredath, Tabeel, and the rest of his associates, unto Artaxerxes, king of Persia, —and, the writing of the letter, was written in Aramean, and was to be interpreted as Aramean.
8 Rehum shugaban rundunar soja, da Shimshai marubuci, suka rubuta wasiƙar a kan Urushalima zuwa ga sarki Artazerzes, suka ce.
Rehum holder of judicial authority, and Shimshai the scribe, wrote a certain letter against Jerusalem, —to Artaxerxes the king, thus:
9 Rehum shugaban sojoji, da Shimshai marubuci, da sauran abokansu, wato, alƙalai, da masu riƙe da muƙamai daga Farisa, Uruk da Babilon, mutanen Elam da na Shusha,
Then Rehum holder of judicial authority, and Shimshai the scribe, and the rest of their associates, —the Dinaites and the Apharsathchites, the Tarpelites, the Apharsites, the Archevites, the Babylonians, the Shushanchites, the Dehaites, the Elamites;
10 da sauran mutane waɗanda mai girma Osnaffar ya kwaso, ya zaunar da su cikin birnin Samariya da sauran wurare na Kewayen Kogin Yuferites.
and the rest of the peoples, whom the great and noble Osnappar hath exiled, and set in the city of Samaria, —and the rest Beyond the River, and so forth:
11 (Ga abin da suka rubuta.) Zuwa ga sarki Artazerzes. Daga bayinka, mutanen Kewayen Kogin Yuferites.
This, is a copy of the letter which they sent unto him—unto Artaxerxes the king, —Thy servants, the men Beyond the River and so forth:
12 Ya kamata sarki ya san cewa Yahudawan da suka hauro wurinmu daga wurinka, sun je Urushalima suna sāke gina wannan mugun birni mai tawaye. Suna sāke gyara katangar, suna kuma gyara harsashin katangar.
Be it known unto the king, —that, the Jews who came up from thee unto us, are come to Jerusalem, —the rebellious and wicked city, are they building, and, the walls, have they finished, and, the foundations, will they repair.
13 Ya kamata fa, sarki ya san cewa in aka sāke gina wannan birni duk da katangar birnin, mutanen birnin ba za su dinga biyan haraji, da kuɗin shiga, da na fitar da kaya ba, wannan zai sa aljihun masarauta yă bushe.
Now be it known to the king, that, if this city, be built, and, the walls thereof, be finished, neither, tribute, excise, nor toll, will they render, and so, the revenue of the kings, shalt thou damage.
14 Tun da yake muna ƙarƙashin fada, bai kyautu mu bari a rena sarki ba, Saboda haka muke sanar da sarki,
Now, because the salt of the palace we have eaten, the impoverishment of the king, it is not meet for us to see, —therefore have we sent, and certified the king;
15 domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka ga cewa wannan birni mai tawaye ne. Tun daga zamanin dā wannan birnin yana ba sarakuna da yankuna damuwa. Wannan ne ya sa aka ragargazar da birnin.
so that search may be made in the book of the records of thy fathers, so shalt thou find out in the book of records—and shalt ascertain, that, this city, is a rebellious city, and one that causeth damage unto kings and provinces, and that, rebellion, have they been wont to cause in the midst thereof since the days of age-past time, —for this cause, was this city laid waste.
16 Muna sanar da sarki cewa in har aka sāke gina wannan birnin da katangarsa, zai zama ka rasa kome a gefen Kewayen Kogin Yuferites ke nan.
We do certify the king that, if, this city, be built, and, the walls thereof, finished, for that very reason, portion Beyond the River, shalt thou have none.
17 Sarki ya aika da wannan amsa. Zuwa ga Rehum shugaban sojoji, Shimshai marubuci da kuma sauran abokansu waɗanda suke zama a Samariya da kuma sauran wurare a Kewayen Kogin Yuferites. Gaisuwa.
The king sent, a message, unto Rehum holder of judicial authority, and Shimshai the scribe, and the rest of their associates, who were dwelling in Samaria, and the rest Beyond the River, Peace and so forth.
18 An karanta, an kuma fassara mini wasiƙar da kuma aika.
The letter which ye sent unto us, was distinctly read before me;
19 Na ba da umarni aka kuma yi bincike, aka tarar cewa wannan birni ya daɗe yana yi wa sarakuna tawaye, an yi tashin hankali a birnin.
And, from me, went forth an edict, and they have made search and found, that, this city, since the days of age-past time, against kings, hath lifted herself up, —and, sedition and rebellion, have been made therein;
20 Urushalima ta yi sarakuna masu iko sosai waɗanda suka yi mulkin Kewayen Kogin Yuferites gaba ɗaya, an kuma biya masu haraji, da kuɗin shiga da na fita na kaya.
and, mighty kings, have there been over Jerusalem, and bearing rule everywhere Beyond the River, —and, tribute, excise, and toll, have been given to them.
21 Saboda haka sai ku ba da umarni yanzu cewa mutanen su daina wannan aiki sai lokacin da na ba da umarni.
Now, issue ye an edict, to forbid these men, —that, this city, be not built, until, from me, the edict be issued.
22 Ku tabbata ka ɗauki wannan da muhimmanci. Don me za a bari wannan abu yă zama abin damuwa ga sarauta?
Beware, then, of failure to do thus, —wherefore should the damage increase, to inflict loss on the kings?
23 Da gama karanta wasiƙar sarki Artazerzes wa Rehum da Shimshai marubuci, da abokansu, sai suka yi sauri suka je wurin Yahudawa a Urushalima, suka hana su aikin ƙarfi da yaji.
Then, when, the copy of the letter of Artaxerxes the king, had been read before Rehum, and Shimshai the scribe, and their associates, they journeyed in haste to Jerusalem, unto the Jews, and forbade them, with arm and force.
24 Saboda haka aikin a gidan Allah a Urushalima ya tsaya cik sai a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus sarkin Farisa.
Then ceased the work of the house of God, which was in Jerusalem, —yea it did cease, until the second year of the reign of Darius king of Persia.