< Ezra 3 >

1 Da tsayawar watan bakwai, sai Isra’ilawa waɗanda suka koma garuruwansu suka taru da nufi ɗaya a Urushalima.
Ko je prišel sedmi mesec in so bili Izraelovi otroci v mestih, se je ljudstvo kakor en človek zbralo skupaj v Jeruzalemu.
2 Sai Yeshuwa ɗan Yozadak da sauran firistoci, da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da abokan aikinsa, suka fara gina bagaden Allah na Isra’ila don miƙa hadaya ta ƙonawa bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa mutumin Allah.
Potem je vstal Jocadákov sin Ješúa in njegovi bratje duhovniki in Šealtiélov sin Zerubabél in njegovi bratje in zgradili so oltar Izraelovemu Bogu, da na njem darujejo žgalne daritve, kakor je to zapisano v postavi Mojzesa, Božjega moža.
3 Duk da tsoron da suke ji na mutanen da suke kewaye da su, sun gina bagaden a wurinsa, suka kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagaden ga Ubangiji safe da yamma.
Nad njegovimi podnožji so postavili oltar, kajti strah je bil nad njimi zaradi ljudstva tistih dežel. Na njem so darovali žgalne daritve Gospodu, torej žgalne daritve zjutraj in zvečer.
4 Bisa ga abin da yake a rubuce kuma, suka yi biki Bikin Tabanakul, suka miƙa hadayu kowace rana gwargwadon yawan hadayun da ake bukata.
Imeli so tudi šotorski praznik, kakor je ta zapisan in darovali so dnevne žgalne daritve po številu, glede na navado, kakor je zahtevala vsakodnevna dolžnost.
5 Bayan wannan, suka miƙa hadayu na ƙonawa yadda aka saba. Suka miƙa hadayu na Sabon Wata, da hadayu na bukukkuwan Ubangiji, da kuma hadayun da aka bayar da yardar rai ga Ubangiji.
Potem so darovali nenehno žgalno daritev, tako na mlaje in ob vseh določenih Gospodovih praznikih, [tisti], ki so bili posvečeni in od vsakega, ki je voljno daroval prostovoljno daritev Gospodu.
6 A ranar farko ta watan bakwai, sai suka fara miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko da yake ba a riga an aza harsashin ginin haikalin Ubangiji ba.
Od prvega dne sedmega meseca so začeli darovati žgalne daritve Gospodu. Toda temelj Gospodovega templja še ni bil položen.
7 Sai suka ba wa magina da kafintoci kuɗi, suka ba wa mutanen Sidon da na Taya abinci, da abin sha, da mai, don su kawo itatuwan al’ul a Yaffa daga Lebanon ta teku, yadda Sairus sarkin Farisa ya ba da umarni.
Denar so dajali tudi zidarjem in tesarjem; in hrano, pijačo in olje tistim iz Sidóna in tistim iz Tira, da iz Libanona pripeljejo cedrova drevesa k morju pri Jopi, glede na dovoljenje, ki so ga imeli od perzijskega kralja Kira.
8 A wata na biyu na shekara ta biyu, bayan sun komo gidan Allah a Urushalima, sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, Yoshuwa ɗan Yozadak da sauran’yan’uwansa (Firistoci da Lawiyawa da duk waɗanda suka komo Urushalima daga bauta) suka fara aiki, aka zaɓi Lawiyawa daga masu shekaru ashirin da haihuwa zuwa waɗanda suka wuce haka don su dubi aikin ginin gidan Ubangiji.
Torej v drugem letu svojega prihoda k Božji hiši v Jeruzalemu, v drugem mesecu, so začeli Šealtiélov sin Zerubabél, Jocadákov sin Ješúa in preostanek izmed njihovih bratov duhovnikov in Lévijevcev in vsi tisti, ki so prišli iz ujetništva v Jeruzalem in določili so Lévijevce, od dvajset let stare in navzgor, da poženejo delo Gospodove hiše.
9 Yeshuwa da’ya’yansa maza, da’yan’uwansa, da Kadmiyel da’ya’yan Yahuda (’yan zuriyar Hodawiya), da’ya’yan Henadad, da’ya’yansu da’yan’uwansu, dukansu Lawiyawa ne, suka haɗa kai cikin duban masu aikin gidan Allah.
Potem so skupaj vstali Ješúa, s svojimi sinovi in svojimi brati, Kadmiél in njegovi sinovi, Judovi sinovi, da postavijo delavce v Božji hiši, Henadádove sinove z njihovimi sinovi in njihovimi brati Lévijevci.
10 Da masu ginin suka aza harsashin ginin haikalin Ubangiji, sai firistoci suka sa kayansu na firistoci suka riƙe ƙahonin busa, Lawiyawa (’ya’yan Asaf) kuwa suka riƙe kuge, suka yi shiri domin su rera yabo ga Ubangiji kamar yadda Dawuda Sarkin Isra’ila ya ba da umarni.
Ko so graditelji položili temelj Gospodovemu templju, so postavili duhovnike v njihovi obleki s trobentami in Lévijevce, Asáfove sinove, s cimbalami, da hvalijo Gospoda, po odredbi Izraelovega kralja Davida.
11 Suka rera waƙar yabo da godiya ga Ubangiji, suna cewa, “Shi nagari ne; ƙaunarsa kuwa ga Isra’ila har abada ce.” Dukan jama’a kuwa suka yabi Ubangiji da murya mai ƙarfi, domin an aza harsashin ginin gidan Ubangiji.
Peli so skupaj po skupini v slavljenju in zahvaljevanju Gospodu, ker je dober, kajti njegovo usmiljenje do Izraela traja večno. In vse ljudstvo je vriskalo z močnim vzklikanjem, ko so hvalili Gospoda, ker je bil položen temelj Gospodove hiše.
12 Amma tsofaffin firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai da yawa, waɗanda dā suka ga yadda haikali na farko yake, suka fashe da kuka mai ƙarfi sa’ad da suka ga an aza harsashin ginin wannan haikali, yayinda waɗansu kuma suka yi ihu da farin ciki.
Vendar pa so mnogi izmed duhovnikov in Lévijevcev in vodij očetov, ki so bili starodavni ljudje, ki so videli prvo hišo, ko so bili temelji te hiše položeni pred njihovimi očmi, jokali z močnim glasom in mnogi so zaradi radosti na glas vzklikali,
13 Ba wanda zai iya rabe tsakanin ihun farin ciki da na kuka, domin mutanen sun tā da murya sosai har aka ji su daga nesa.
tako da ljudstvo ni moglo razločiti glasu radostnega vzklikanja od glasu jokanja ljudstva, kajti ljudstvo je vzklikalo z glasnim vriskom in zvok je bilo slišati daleč proč.

< Ezra 3 >