< Ezra 3 >

1 Da tsayawar watan bakwai, sai Isra’ilawa waɗanda suka koma garuruwansu suka taru da nufi ɗaya a Urushalima.
Le septième mois approchant, et les enfants d'Israël étant dans leurs villes, le peuple s'assembla à Jérusalem, comme un seul homme.
2 Sai Yeshuwa ɗan Yozadak da sauran firistoci, da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da abokan aikinsa, suka fara gina bagaden Allah na Isra’ila don miƙa hadaya ta ƙonawa bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa mutumin Allah.
Alors Jéshua, fils de Jotsadak, se leva avec ses frères les sacrificateurs, et Zorobabel, fils de Salathiel, avec ses frères; et ils bâtirent l'autel du Dieu d'Israël, pour y offrir les holocaustes ainsi qu'il est écrit dans la loi de Moïse, homme de Dieu.
3 Duk da tsoron da suke ji na mutanen da suke kewaye da su, sun gina bagaden a wurinsa, suka kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagaden ga Ubangiji safe da yamma.
Et ils redressèrent l'autel sur ses fondements, car ils étaient sous la crainte des populations du pays; et ils y offrirent des holocaustes à l'Éternel, les holocaustes du matin et du soir.
4 Bisa ga abin da yake a rubuce kuma, suka yi biki Bikin Tabanakul, suka miƙa hadayu kowace rana gwargwadon yawan hadayun da ake bukata.
Ils célébrèrent ensuite la fête des tabernacles, ainsi qu'il est écrit, et ils offrirent des holocaustes chaque jour, autant qu'il en fallait selon que l'ordinaire de chaque jour le demandait.
5 Bayan wannan, suka miƙa hadayu na ƙonawa yadda aka saba. Suka miƙa hadayu na Sabon Wata, da hadayu na bukukkuwan Ubangiji, da kuma hadayun da aka bayar da yardar rai ga Ubangiji.
Après cela, ils offrirent l'holocauste continuel, ceux des nouvelles lunes et de toutes les solennités consacrées à l'Éternel, et ceux que chacun présentait volontairement à l'Éternel.
6 A ranar farko ta watan bakwai, sai suka fara miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko da yake ba a riga an aza harsashin ginin haikalin Ubangiji ba.
Dès le premier jour du septième mois, ils commencèrent à offrir des holocaustes à l'Éternel, bien que le temple de l'Éternel ne fût pas encore fondé.
7 Sai suka ba wa magina da kafintoci kuɗi, suka ba wa mutanen Sidon da na Taya abinci, da abin sha, da mai, don su kawo itatuwan al’ul a Yaffa daga Lebanon ta teku, yadda Sairus sarkin Farisa ya ba da umarni.
Mais ils donnèrent de l'argent aux tailleurs de pierres et aux charpentiers; ils donnèrent aussi à manger et à boire, ainsi que de l'huile, aux Sidoniens et aux Tyriens, afin qu'ils amenassent du bois de cèdre, du Liban à la mer de Japho, selon la permission que Cyrus, roi de Perse, leur en avait donnée.
8 A wata na biyu na shekara ta biyu, bayan sun komo gidan Allah a Urushalima, sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, Yoshuwa ɗan Yozadak da sauran’yan’uwansa (Firistoci da Lawiyawa da duk waɗanda suka komo Urushalima daga bauta) suka fara aiki, aka zaɓi Lawiyawa daga masu shekaru ashirin da haihuwa zuwa waɗanda suka wuce haka don su dubi aikin ginin gidan Ubangiji.
Et la seconde année depuis leur arrivée à la maison de Dieu, à Jérusalem, au second mois, Zorobabel, fils de Salathiel, Jéshua, fils de Jotsadak, et le reste de leurs frères, les sacrificateurs, et les Lévites, et tous ceux qui étaient venus de la captivité à Jérusalem, commencèrent; et ils établirent des Lévites, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, pour présider à l'ouvrage de la maison de l'Éternel.
9 Yeshuwa da’ya’yansa maza, da’yan’uwansa, da Kadmiyel da’ya’yan Yahuda (’yan zuriyar Hodawiya), da’ya’yan Henadad, da’ya’yansu da’yan’uwansu, dukansu Lawiyawa ne, suka haɗa kai cikin duban masu aikin gidan Allah.
Et Jéshua assistait avec ses fils et ses frères, et Kadmiel avec ses fils, enfants de Juda, comme un seul homme, pour diriger ceux qui faisaient l'ouvrage de la maison de Dieu, ainsi que les fils de Hénadad, avec leurs fils et leurs frères, Lévites.
10 Da masu ginin suka aza harsashin ginin haikalin Ubangiji, sai firistoci suka sa kayansu na firistoci suka riƙe ƙahonin busa, Lawiyawa (’ya’yan Asaf) kuwa suka riƙe kuge, suka yi shiri domin su rera yabo ga Ubangiji kamar yadda Dawuda Sarkin Isra’ila ya ba da umarni.
Or, lorsque ceux qui bâtissaient jetèrent les fondements du temple de l'Éternel, on y fit assister les sacrificateurs en costume, avec les trompettes, et les Lévites, fils d'Asaph, avec les cymbales, pour louer l'Éternel, selon l'institution de David, roi d'Israël.
11 Suka rera waƙar yabo da godiya ga Ubangiji, suna cewa, “Shi nagari ne; ƙaunarsa kuwa ga Isra’ila har abada ce.” Dukan jama’a kuwa suka yabi Ubangiji da murya mai ƙarfi, domin an aza harsashin ginin gidan Ubangiji.
Et en louant et en célébrant l'Éternel, ils s'entre-répondaient ainsi: Car il est bon, car sa miséricorde demeure à toujours sur Israël! Et tout le peuple jetait de grands cris de joie, en louant l'Éternel, parce qu'on posait les fondements de la maison de l'Éternel.
12 Amma tsofaffin firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai da yawa, waɗanda dā suka ga yadda haikali na farko yake, suka fashe da kuka mai ƙarfi sa’ad da suka ga an aza harsashin ginin wannan haikali, yayinda waɗansu kuma suka yi ihu da farin ciki.
Mais plusieurs des sacrificateurs, et des Lévites, et des chefs des pères, qui étaient âgés, et qui avaient vu la première maison sur son fondement, en se représentant cette maison-ci, pleuraient à haute voix; tandis que beaucoup d'autres élevaient leurs voix avec des cris de réjouissance et avec joie.
13 Ba wanda zai iya rabe tsakanin ihun farin ciki da na kuka, domin mutanen sun tā da murya sosai har aka ji su daga nesa.
Et l'on ne pouvait discerner la voix des cris de joie d'avec la voix des pleurs du peuple; car le peuple jetait de grands cris, de sorte que leur voix fut entendue bien loin.

< Ezra 3 >